Thursday, December 20, 2012

Budadden Sako Zuwa Ga Sabon Gwamnan Jihar Kaduna

Zuwa ga Mai Girma, Alhaji Mukhtar Ramalan Yero, Gwamnan Jihar Kaduna. Assalamu – Alaikum! Da farko ina yin mana jaje na rashin Gwamnanmu da mukayi Mr. Patrick Ibrahim Yakawo, a sanadiyar hadarin jirgin sama, muna fatan Allah Yasa ya taradda da yan’uwansa acan, mu kuma Allah Ya kyautata namu bayan nasu Yasa mu cika dakyau da Imani, ba yanda za ayi domin dukkan mai rai mai mutuwa ne. Bayan haka, inaso in yi anfani da wannan dama domin inyi maka nasiha da kuma bada shawara, kasancewar bani da wata hanya da zanzo in sameka ni dakai sai ta wannan hanyar wanda na tabbata, in baka gani ba, wadanda suke kusa dakai zasu gani kuma zasu sanar dakai. 1. Da farko ina tunatar dakai da kara sanya jin tsoron Allah a cikin al’amuranka duka na yau da kullun, domin shi ne zai zame maka jagora akan dukkan abin da ka fuskanta. 2. Ka godewa Allah a bisa wannan ni’ima da ya yi maka. Ta yaya zaka gode maSa? Shi ne ta hanyar aikata abin da duk Ya umurce ka dasu gwargwadon ikonka, ka kuma nisanci duka abubuwan da Ya hanaka, idan ka siffantu da haka, to, shi zaisa Ya yi maka kari a bisa wannan ni’iman da Yayi maka yanzu. 3. Ka zamo mai adalci a bisa wadanda Allah Ya daura maka alhakinsu a kanka. Duk mai hakki ka bashi hakkinsa gwargwadon yanda doka ta tsara. 4. Ka zamo mai gaskiya da rikon amana da kuma daukan alkawarin abubuwan da kasan bisa ikon Allah bai fi karfinka ba. 5. Ka guji yin duka wani abu da zai zamo nau’in yin zalunci ne ga wadanda kake shugabanta, domin babu shamaki tsakanin addua’an wanda aka zalunta da Mahaliccinsa, kamar yanda Manzon Allah Sallallahu Alayhi Wasallam ya sanar damu haka, ya kuma ja kunnen mu akai. 6. Ni a tawa shawaran, ina ganin akwai wasu abubuwan guda biyu da suke neman sufi karfin talaka gabaki daya, wato sune harkan ilmi da abin da ya shafi harkan lafiya, ka sanya ido kai tare da bada dukkan gudummuwan da zaka iya badawa. 7. Ka sakamma kananan hukumomi mara domin suma su sami daman yin ma nasu al’ummomin ayyukan morewa. Ka kuma sanya ido akan yanda suke gudanar da harkokinsu gudun kada su wuce gona da iri. 8. Kula da harkan tsaro shima yana da matukar muhimmanci, domin sai da zaman lafiya ake samun daman gabatar da duk wasu ayyuka. Daga karke, ina rokon Allah da Yayi maka jagora, Ya sanya maka hannu a bisa wannan nauyi da ya daura maka, Ya kasance tare dakai a duk inda kake, Ya baka ikon sauke dukkan nauyin da Ya daura maka, Ya kuma sanya maka katangar karfe tsakaninka da dukkan makiya mutun ko aljan. Muma Allah Ya biya mana dukkan bukatummu. Wassalamu Alaykum, ABDULKARIM MUH’D TANKO

Tuesday, November 13, 2012

Kotu Ta Yanke Wa Jarimi Sani Musa Danja Hukunci Daurin Shekara Guda A Gidan Yari

Kotun tafi da gidanka ta Hukumar tace finafinai ta jihar Kano ta yankewa shahararren dan wasan kwaikwayon nan na Hausa Sani Musa Danja daurin shekara guda a gidan yari.

Kotun ta daure Sani Danja ne sakamakon fitar da wani fim din sa mai suna Gudaliya ba tare da bin dokar hukumar tace finafinan ta jihar Kano ba, wanda hakan ya sabawa dokar hukumar ta sashi na 100 (2) ta shekarar 2001, sannan hukuncin da aka yanke masa na karkashin sashi na 112 na kundin tsarin mulkin hukumar.

Bayan samun sa da laifin, alkalin kotun mai shari'a Mukhtar Ahmad ya yanke wa Sani Musa Danja hukuncin zaman yari na tsawon shekara guda ko kuma biyan tarar N30,000, karkashin sashi na 157 na kundin hukunta masu laifuka, na shekara ta 2001.

Yan Fashi Sun Kai Farmaki Kasuwar Chanji ta Wapa a Jihar Kano

Da tsakar ranar Talatar nan ne wasu yan fashi da makami suka kai farmaki kasuwar yan chanji dake Wapa a birnin Kano. Yan fashin su kimanin 9 da suke akan babura da kuma mota kirar Golf sun ringa harbi babu kakkautawa a kasuwar daga bisani suka kutsa cikin wani shago suka yi awon gaba da miliyoyin kudi da har yanzu ba a tantance yawansu ba.

Shugaban kasuwar Wapa Alhaji Auwal Umar Nagari ya bayyana takaici bisa rashin isowar jami'an tsaro akan lokaci da kuma yadda yan fashin suka bar wasu kwanson harsasai mai dauke da tambarin 'yan sanda lamarin da yasa suke zargin kodai akwai lauje cikin nadi. yawan fashi a kasuwannin jihar Kano dai wani babban al amari ne da a yanzu ke nema zama ruwan duk da yawan jami'an tsaro dake baje a hanyoyin jihar.

Freedom Radio FM, Kano

Kano tribunal jails Sani Danja

Kano State Censorship Tribunal sitting has sentenced popular Hausa film actor, Sani Musa Danja to one year imprisonment.Sani Danja was sentenced yesterday for exhibiting for sale an uncensored and unlicensed copy of a film titled “Gudaliya” in contravention of Section 100 (2) of the state Cinematography Censorship Regulation 2001 and punishable under Section 112 of the same law.

He pleaded guilty and asked the court for leniency. Senior State Counsel Hussain Hassan therefore applied for summary trial under section 157 of the criminal procedure court. Chief Magistrate Mukhtar Ahmed sentenced him to one year imprisonment or to pay a fine of N30,000.

Culled: Daily Trust

Saturday, November 10, 2012

Yau Jama'a Za Su Bayyana Ra'ayoyinsu Ga Gyaran Kudin Tsarin Mulkin Kasa

Yau ne, abisa mafi yawancin sanarwar da ake ta bayarwa, za a fara jin ra'ayoyin al'umma don gyaran kundin tsarin mulkin kasa, mai cike da son zuciya da kura-kurai da rashin girmama addinin Musulunci. Wannan yasa ya kamata ga kowa yasan dama ce tazo.

Malamanmu wajibi ne su shiga wannan batu, su fadakar da 'yan majalissunmu Musulmai game da damar da idan har ta kubuce, to ba mu san sai yaushe kuma za ta sake dawo ba! Malamai, 'yan siyasa, masana fannin shari'ar Musulunci, malaman Jami'o'i da makarantun gaba da sakandare, 'yan kasuwa Musulmai (musamman na Arewa), masu tunani a cikin mu, dalibai, da sauran mu............

Wajibi ne a gare mu, abu na farko a kodayaushe da zamu ke kula dashi: Addininmu! (Musulunci) sannan, Al'ummarmu (Hausawa) sannan yankinmu (Arewa) dole ne a ba mu damar yin rayuwa kamar kowa, a dai na kashe mu, a dai na cin zarafinmu.

A ba mu damar amfana da arzikin kasarmu kamar kowa, da duk wani abu wanda mai kyau ne ga addininmu da al'adarmu. Don Allah, kada musulmai su kara mika wuya ga secularism, wanda kowa yasan kai tsaye yayi kamanceceniya da kafirci!!!

(Sunnah Akhabariyah)

Friday, November 9, 2012

'Yan Kasa Ne Za Su Gyara Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya

Kamar yadda mu ka sani, Majilisar Dokoki ta kasa ta na shirye - shiryen sake yin gyare - gyare ga Tsarin Mulki na Shekarar 1999.

Wannan gyare - gyare sun shafi harkokin siyasa, tattalin arziki, zaman takewa da kuma tsarin yadda a ke tafiyar da Gwamnati. A cikin shirye - shiryen gyaran Tsarin Mulkin, Majilisar Wakilai ta Tarayya ta yanke qudurin cewa gyaran da za ta yi wa Tsarin Mulkin zai sami gudunmuwa daga Jama'ar kasa ne.

A bisa wannan ne Majalisar ta fitar da cewa duk abinda za'a yi gyara a kansa sai kowanne 'Dan Majalisa ya je Maza'barsa ya tattauna da Jama'ar da ya ke wakilta don jin ra'ayinsu a kan wa'dannan abubuwa. Idan ba'a sami ha'duwar ra'ayi ba sai a yi quri'a wanda ya fi rinjaye shi ne matsayin wannan Maza'ba a kan gyaran Tsarin Mulkin.

Bayan an kammala wannan tarurruka na Maza'bu, za'a tattara sakamako a kai Majalisa wanda wannan sakamakon ra'ayin Jama'a ne Majalisar Tarayya za ta yi amfani da shi a kan abubuwan da a ke son yin gyara a kan su.

Wa'dannan tarurruka na Maza'bu an ware ranar Asabar 10 ga Nuwamba, 2012 dan yin su a fa'din qasa ba ki 'daya a lokaci guda. An fitar da sanarwa ta musamman a gidajan radiyon yankuna - yankuna da sauran kafafan ya'da labarai dangane da wa'dannan tarurruka da kuma inda za'a yi su a kowacce Maza'ba ta Tarayya. Akwai bukatar mu halacci wa'dannan tarurruka a dukkanin Maza'bunmu dan ganin cewa ba mu bari wasu sun ari bakin mu sun ci ma na albasa ba.

Thursday, November 1, 2012

Sanarwa: Daurin Auren Gali Da Gimbiya Asma'u

To fa. . . . Bari dai na fara da mabudin kunne kafin na zarce inda na nufa “Aure rufin asirin Musulmai” na san daga jin wannan karin waka da yawa daga cikinmu za su fuskanci inda na nufa, hmmm! Kar dai kuce na cika ku da surutu bari na tafi kai tsaye:

Muhammad Gali Abubakar ne da amaryarsa Asma'u Lawan Hamza (Ummi) cike da farin ciki marar misaltuwa suke gayyatarku domin kuyi tururuwa da dafifi zuwa shaida daurin aurensu.

An tsara za a gudanar da bikin kamar haka: Rana: Juma'a 2/11/2012 = 17/12/1433

Wurin Haduwa: Za a hadu a Goron Dutse Bayan Wreca Kano, Gidan Gwani Malam Lawan Gaya

Wurin Daurin Aure: Sheka Baranda Unguwar Kudu Kano, Gidan Malam Lawan Dan Gaya Ango da amarya na cike da fatan dukkanku zaku dungumo ku shaida wannan daurin aure na su tare da taya su adduar fatan alheri.

Dandali ya samu wannan sanarwa ne daga Lawiza da Hauwa 'yayan Murtala Jar Kasa, Zuru, Jihar Kebbi.

Monday, October 22, 2012

Wacece Safeena Buhari? - Daga Yasir Ramadan Gwale

Safeena Buhari diya ce ga Gen Muhammadu Buhari. Abin da yake faruwa shine akwai wata baiwar ALLAH da watakila 'yan uwa suke ganin post dinta a koda yaushe a facebook da wannan suna na Safeena Buhari, mun yi kokari domin gano shin da gaske safeenan Gen Buhari ce ko kuwa ta karya ce, Alhamdulillah wakilinmu ya je har gidan Gen Buhari a kaduna inda aka tabbatar masa da cewar wannan Safeena Buhari da muke ganin a fzbk ba ita ce ba.

Wato muna da yawa wadanda muke musayar kalamai da ita ta bayan fage wato Inbox, na taba tambayarta tsakaninta da ALLAH ita diyar General ce, ta yi min rantsuwa akan cewa ita diyarsa ce, wanda sakamakon bincikenmu ya tabbatar mana da cewa karya take.

Abinda yake faruwa shine, kusan da yawanmu da muke magana da ita ta shaidamana cewar tana aiki a QATAR amma kuma yanzu tana zaune a Germany sakamakon jinyar mijinta, wasu kuma ta shaidamusu cewar tana England, akwai daga cikinmu wadanda ta yaudara da sunan zata samar masa da Scholarship dan su yi karatu a QATAR, haka kuma tayi wa wani alkawarin tuntubar Sarkin DUBAI domin nema masa taimako, duk da take yin wadannan maganganu da alkawura, mu tuni mun gane ta, kawai shiru muka yi mata, amma kuma yanzu lokaci yayi da muke ganin ya kamata mu bankada wannan Asiri, domin ta fara yaudarar wasu da samar musu da kwangilar harkar mai a kasashen larabawa, wanda idan muka ci-gaba da yin shiru zata bata sunan Gen Buhari ne, kuma zata damfari wadanda basu santa ba, haka kuma itace dai take amfani da wani account mai suna YUSUF BUHARI wanda shima dane ga Gen Buhari amma bai da masaniyar ana amfani da sunansa anan facebook.

Dan haka jama'a a kiyaye Mu'amala da ita, domin ba Safeenar gaskiya bace, watakila wani Dan iskan kato ne yake amfani domin ya bata musu suna kuma ya nemi abin duniya. Hakika mai amfani da wannan suna na Safeena Buhari yana da masaniyar gidan Buhari sosai, dan kawai ya samu ya ci-kasuwarsa, a kwanakin baya ta sanya wani hoto na Matar Gen Buhari da matar Tunde Bakare da kuma Safeena Buhari ta ainihin, idan kuka duba Profile dinta zaku gani. Muna addu'ar duk wanda yake wannan danyan aiki ALLAH ya shirye shi, idan kuma ba mai shiryuwa bane, ALLAH ya shiga tsakanin nagari da Mugu.

Sunday, October 21, 2012

Gwamnonin Kasar Nan Da Suka Fi Bajinta

Sakamakon binciken da wata kungiya mai suna Eagle Eyed Youth Association of Nigeria tare da hadin gwiwar kungiyoyin sa kai fiye da 100 da kuma jin ra'ayoyin jama'a a sassan kasar nan daban - daban, ya bayyana sunayen gwamnoni a kasar guda 10 da suka fi yiwa talakawansu aiki. Gwamnonin su ne: 1) Dr. (Barr) Ibrahim Shehu Shema, na jihar Katsina. 2) Barr. Babatunde Raji Fashola na jihar Lagos. 3) Chief Rochas okorocha na jihar Imo. 4) Alh. Aliyu Wamakko na jihar Sokoto. 5) Eng. Rabi'u Musa Kwankwaso na jihar Kano. 6) Alh. Tanko Al Makura na jihar Nasarawa. 7) Dr. Rotimi Amaechi na jihar Rivers. 8) Rear Admiral Murtala H. Nyako na jihar Adamawa. 9) Alh. Sule Lamido na jihar Jigawa. 10) Comrade Adams Oshiomole na jihar Edo. Shin a naku ra'ayin wannan sakamako yayi daidai ko da son zuciya a cikinsa? Idan akwai son zuciya a naka ra'ayin wane gwamna ya kamata ya zama a matakin farko?

Saturday, October 13, 2012

Sarkin Kano Ya Cika Shekaru 49 Akan Gadon Sarauta

Allah mai yadda ya so. A yau Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji (Dr.) Ado Bayero ya cika shekaru 49 akan gabon sarauta (13 Oktoba 1963 - 13 Okboba 2012) Idan Allah ya kaimu shekara mai zuwa zai cika shekaru 50 daidai wato rabin karni akan gadon na sarauta. A madadin ni kaina da sauran maziyarta wannan shafi muna taya Mai Martaba San Kano da sauran daukakin jama'ar Kano munnar wannan rana. Allah ya karawa Sarki lafiya da imani, Allah ya bamu zaman lafiya da kwanciyar hankali a jiharmu Kano da kasarmu Nijeriya baki daya. Bashir Ahmad

Thursday, September 27, 2012

Nigeria: Zan Cika Shekaru 52 Bayan Samun 'Yancin Kai Na

Kwanaki uku ya rage na cika shekaru 52 bayan samun 'yancin kai na daga hannun turawan mulkin mallakar kasar Burtaniya. Zan yi murnar zagayowar ranar ne kawai saboda ta cancanci hakan, amma ba don ina da 'yancin kan nawa ba, domin kuwa a tarihin rayuwa ta ban taba shan wahala, da rayuwa marar 'yanci ba kamar bayan samun 'yancin kan nawa da ake ikirarin wai na samu. Hmmm ta bangare na dai ba wani 'yanci da zan iya cewa na samu, sai dai samuwar rayuwar bauta da na sake samun kai na a ciki. To ku kuma 'yayana, mai za ku ce da wannan rana ta 1st October? Na san kalilan daga cikin ku suna murna da ranar har bukukuwa suke yi sakamakon zagayowarta. Amma dai bari na ji amsa daga gare ku. Shin kuna farin ciki da zagayowar ranar? Ku ziyarci Dandali Domin ba da amsoshinku.

Tuesday, September 18, 2012

Mu Kauracewa Amfani Shafin YouTube


Yan uwa ya kamata mu kauracewa amfani da shafin YouTube da rage mu'amala a shafin matambayi baya bata na Google, sakamakon kin cire video wasan kwaikwayon da aka yi isgilanci ga Fiyayyen Halitta Annabin Muhammad (SAW).

Tun bayan fitowar wannan wasan kwaikwayo a shafin na YouTube gwamnatin kasar Amurka ta umarci kamfanin Google da ya mallaki shafin na YouTube da su cire video daga shafinsu, saboda kyale shi cin zarafin mabiya addinin Musulunci ne.

Amma kamfani na Google ya kekasa kasa da cewar yin hakan ya saba dokar kare hakkin loda video na masu amfani da shafin.

Wannan dalilin ya sa wasu kasashen Musulmai suka yanke shawarar kauracewa amfani da YouTube a ranakun 20, 21 da 22 na watan Satumba da muke ciki, don nuna fushin su ga kin cire video da shafin yayi. Wanda kuma akalla Musulmai sama da miliyan 100 suna amfani da shafin a kowace rana.

To ya kamata mu ma mu shiga sahun 'yan uwanmu Musulman duniya, na kauracewa amfani da shafin a wadannan rana ku, koda kuwa akwai muhimmin aiki da za muyi a cikin sa, yin hakan ba karamin asara zai haifarwa kamfanin ba, idan kuma hakan ma suka ki yarda da bukatarmu na cire video, to sai mu dauki matakin daina amfani da shafin na dindindin, wato na har abada.

Aikawa, sauran 'yan uwa wannan sako.

Friday, September 14, 2012

Na Yi Nadamar Yin Zanga - Zangar Janye Tallafin Man Fetur


Ban taba tunanin zan yi nadamar kasancewa daya daga cikin miliyoyin jama'ar kasar nan da suka gudanar da zanga - zangar nuna rashin amincewa da kudirin gwamnatin tarayya na janye tallafin albarkatun man fetur ba, hasalima a kullum na tuna lokacin sai naji nishadi ya baibaye dukkan zuciyata koda kuwa ina cikin yanayin bakin ciki ne, kai har alfahari nake da lokacin musamman ranar da ni da wasu jajirtattun matasa muka fita shatale-talen Silver Jubilee dake tsakanin fadar masarautar Kano da fadar gwamnatin Kano da daddare da niyyar kwana a filin duk don mu nunawa duniya cewar bama goyon bayan kudirin na gwamnati, duk da bamu yi nasarar kwana a wurin ba kamar yadda muka shirya yi sakamakon jami'an tsaro da suka tarwatsa mu cikin talatainin dare da harbin harsashi da barkonon tsohowa.

Ba komai yake sani alfahari da ranar ba, sai don a tarihin Nijeriya mu kadai ne muka taba yunkurin yin hakan duk kuwa da bamu yi nasarar kwana a wurin ba. Amma duk da irin jami'an tsaron da aka jibge a Silver Jubilee a lokacin sai da washe gari jama'a suka sake fitowa nuna rashin goyon bayansu duk saboda a tunaninmu idan gwamnati ta janye tallafin man fetur din nan zamu shigo wani sabon kangi na wahalhalun rayuwa, to a karshe dai gwamnatin ba ta fasa aiwatar da kudirin na ta ba, sai dai 'yar kwaskwarima kadan da tayi masa, wadda wasu ke alakanta hakan da zanga - zangar da muka yi a sassa daban - daban na kasar nan.

Kamar yadda na fada a baya bana tunanin zan taba yin nadamar yin hakan a sauran rayuwata da ta rage, wanda nasan kuma ba za ku ga laifina ba, saboda kuwa na nuna kishin kasata da kokarin kwatowa talakawa 'yanci, wadanda wahalhalun da muke tunanin za a shiga za ta fi shafa, sai ga shi lokaci daya nadamar yin hakan ta wanzu cikin zuciyata ta hanani sukuni da jin dadin rayuwata.

Tun a ranar da tsinannun kafiran Amurka suka fito da wani yanki daga cikin wasan kwaikwayon da suka shirya mai taken Innocence of Muslims wanda suka shirya isgilanci da batancin da ba'a taba yin irin sa a tarihin duniya ba akan Annabi Muhammad (SAW) na shiga wannan nadama tawa, ba don komai ba sai a duk lokacin da na kamo gidajen television da suke nuna labaran da suka shafi duniya sai naga ba labarin da suke nunawa sai zanga - zangar da ake kan gudanarwa a kasashen larabawa sakamakon shirya wannan wasan kwaikayo, sai naga cewa shin mu menene dalilin daya sa bamu fita zanga - zangar ba domin nuna rashin amincewarmu akan fim din, saboda fita wannan zanga - zangar itace mai asali da kuma tushe ba wadda muka yi a baya ba.

Kowace kasa aka nuno za ka ga manyan malamai da attajirai sune a sahun gaba, ana kona tutar Amurka da yin tofin alatsine a gare su, a kasar Libya kuwa tun da sanyin safiya suka dauki matakin kashe jakadan Amurka dake kasar, wanda kuma shi ne karo na farko da aka taba yiwa Amurka haka, a kasar Sudan manyan jami'an gwamnatin kasar ne suka shirya zanga - zangar, haka kasar Egypt, Tunisia, Pakistan, Iran, India, Morocco, Syria da sauran kasashe masu kishin addinin Islama.

To a Nijeriya fa???

Ina malamanmu suke? Menene dalilansu nayin shiru akan wannan maganar, shin ko sun manta da cewa wannan maganar ta fi karfi a yi shiru a barta a fatar baki? Menene dalilin da zai sa su zauna a gida ba zasu fito su jagorance mu ba, mu shiga sahun miliyoyin Musulmai duniya wurin yin Allah wadai ga Amurka?

Ya Allah ka gaggauta daukar mataki mummuna akan dukkan wanda yake da hannu a cikin shirya fim din.

Tuesday, September 11, 2012

Hukuncin Wanda Yayi Kisan Kai Bisa Gangaci: Sheikh Ja'afar Mahmud Adam


Ya yan uwa musulmi, yana daga cikin manufofin shari'ar musulunci tsare rayukan bil'adama tsare jinin su, don haka ne nassoshi suka zo acikin alkurani mai girma da abin da ya inganta na hadisan manzon Allah salallahu alaihi wasallam, wadan da suke nuna haramcin jinin bil'adama mu samman dan adam musulmi.

Ubangiji ta'ala ya yi wannan bayani ta hanyar salon zance da ban da ban, ta hanyar nau'ikan magana da ban da ban, Salon zan ce na farko. Ubangiji ta'ala ya wajabta kisasi (ramuwar gayya) ga dukkan wanda ya kashe musulmi da ganganci, hukuncin sa shi ne a kashe shi, dukkan wani mutum da ya kashe musulmi da ganganci ya yi amfani da wani abu wanda ya iya zare rai, ya nufi dan uwan sa musulmi ya aiwatar da wannan makamin akan sa har ya kashe shi, to shi ma akamashi a kashe shi ko shi kadai ne, ko su da yawa ne, sai dai fa idan dangin wanda aka kashe musu dan uwan su suka ce sun yafe, zasu karbi diyya, to sai a basu diyya.

To amma idan ba hakaba hukuncin su da Ubangiji Ta'ala ya nassanta shi ne kisasi, ko da mutum daya ne, ko biyu, ko uku, ko sama da haka, sukayi taron dangi suka kashe mutum daya, kuma hakan ya tabbata, ta hanyara tabbatar da laifi a addinance, a musulunce, hukuncin su shi ne akamasu a kashe su gaba dayan su; Kamar yadda aikin Umar bin Khaddab ya nuna lokacin da wani adadi na wasu mutane suka yi taron dangi suka kashe wani mutum daya su kadai, Umar ya ce a kashesu su duka, wadansu suka yi masa inkari da cewa ya ya za a yi ace a kashe rayuka da dama bayan rai daya suka kashe, Umar ya ce wallahi inda mutanan birnin san'a za su hadu su kashe rai daya to wallahi da na kashe su gaba daya.

Hikimar hakan cikin shari'ar musulunci, shi ne in da ace ana yin kisasi ne kadai idan mutum ya kashe mutum daya za'a kashe shi, sai wanda zai yi kisan ya raba goran gayyata ga abokansa, ko yan uwansa, su je, su kashe wane, don sun san insunyi baza a kashe suba, gobe kai ma idan kana jin hashin wani sai karaba goran gayyata ga wadan da zasu taya ka fada domin kuje ku kashe wane. Wannan sai ya bayu zuwa ga hasarar rayuka, amma idan mutum biyu ko uku ko sama da haka sukayi haka aka kashe su,wannan zai sa dukkan wani da da wani ya rabawa goron gayyata cewa zaka rakani in kashe wane to bazai je ba saboda yasan idan ya aikata hakan to zai bayu zuwaga akashe shi, don haka sai rayukan mutane su zauna cikin aminci. Allah ta'ala yana cewa "lallai kuna da tabbatacciyar rayuwa a cikin kisasi matukar an tabbatar da kisasi a bankasa, wanda duk ya kashe wani da ganganci da kowanne irin dalili cikin dalilai to shi ma za'a kama shi a kashe shi" to wannan sai ya bayu zuwa ga tsare rayukan mutane, kisa ba zai yaduba a bankasa da kowanne irin dalili cikin dalilai. wannan salon magan na farko kenan.

Salon magana na biyu, Ubangiji Ta'ala ya saukar da narkon azaba da firgitarwa da rudarwa da kidimarwa ga dukkan mutumin da ya kashe mumini da ganganci yana ji yana gani sakamakon sa wutar jahannama, zai dawwama a cikin ta ubangiji ta'ala ya yi fushi da shi, ya tsine mashi, sannan yayi masa tanadin azaba maigirma. kaji irin wannan firgici, ka ji irin wannan razani, ka ji irin wannan tsawa, da ya sauka cikin suratul Nisa'i domin aja hankalinka aja hankalina kada kayi dukkan wani yunkuri na zubar da jinin dan uwanka musulmi bisa ganganci.

Salon magana na uku, Ubangiji Ta'ala ya nuna cewa duk wanda ya kashe mumini da ganganci, to baya cikin siffofin muminai nagari, wadan da ubangiji ta'ala ya jero siffofin su a cikin suratul furqan a inda Allah ta'ala yace "sune wadan da basa kiran wani tare da Allah, suna kiran Allah ne kadai dan jawo amfani ko dan ko dan dauke musu wata cuta, sannan ba sa kashe wata rai da Allah ya haramta kisan ta sai ta hanyar gaskiya da adalci”. Sannan kuma cewa mumini baya kisan kai, wannan dalili ne da yake nuna cewa idan kuna son kalmar adalci ta tabbata a kanku to kuyi iyakar kokarinku na tsare jinin yan uwan ku musulmi.

Sannan salon magana na gaba, Ubangiji ta'ala ya danka amana ko ya bayara da iko a hannu wadan da aka kashe wa dan uwa da ganganci, dangin duk wanda aka kashe bisa ganganci. Haka ya ce ya basu iko duk wanda aka kashe bisa ganganci ya bada dama ga yan uwan sa, a hannun dangin sa ko makusantan sa, wannan iko kodai su nemi a basu diyya, ko su nemi a kashe wanda da ya kashe musu dan uwansu, Allah ya basu kowacce daya daga cikin biyun nan a matsayin zabi in suka zabi na farko ya yi in suka zabi na biyu ya yi.

Bayan haka ubangiji subahanahu wata'ala, ya nuna tsare jinin mumini, tsare jinin musulmi, kare jinin dan uwanka musulmi, wannan daya ne daga cikin wasiyyoyi guda goma da Allah ya kebanci al-ummar manzon Allah dasu, wadan da suka zo a jere cikin "suratul An'am" Ya ‘yan uwa musulmi! Manzon Allah sallalahu alaihi wasallam, ya labarta mana cewa dukkan wani mutum da ya kashe dan uwansa da ganganci, to za a zo dasu, ranar alkiyama sai wanda aka kashe ya rike wanda ya kashe shi, hannun sa yana kan zankonsa ya ja shi sutafi gaban Ubangiji Ta'ala ya ce ya ubangiji tambayi wane, me nayi ya kasheni? Alokacin da zai fadi haka jijiyoyin wuyan sa suna furzar da jini domin a halartowa da makshin munin hotan abin da ya akata a gidan duniya, yace tambayi wane me nayi ya kashe ni akan wanne dalili? banbancin siyasa, ko addini, ko manufa, zai ce ya ubnagiji tambayi shi me nayi ya kashe ni. Haka hadisi ya tabbata acikin Sinanu Nisa'i wanda ya ke hadisi ne sahihi.

Ya yan uwa musulmi, addinin musulunci a lokacin da yake haramta kisan kai, ba wai yana haramta zubar da jinin muminai ba kadai! a a hatta daga cikin kafirai wanda shariar musulunci ta kare masu jinin su da dukiyoyinsu, to in ya zamto dokokin Allah da ya saukar ta haramta zubar da jinin wanda bai furta kalmar shahada ba, jinin wanda ya ce Allah uku ne, wanda ya ce Uzairu Binullah! To ya ya kima da daraja da tsada ga jinin wanda ya ce ya shaida babu abin bautawa bisa cancanta da gaskiya sai Allah, kuma Annabi Muhammad Manzan Allah ne.

Haka kuma, kafiri wanda kuka yi yarjejeniyar zaman lafiya tsahon wasu shekaru kan cewa ba za ku yaki juna ba a iya wannan sheakarun na yarjejeniya, to haramunne ka kashe daya daga cikin su ko ka kwace dukiyar sa, sai wadan da kuka yi yarjejeniyar basu rushe ko wanne irin sharadi ba na yarjejeniyar, kuma baku tallafawa wasu ko wani akan ya yake su ba. To, irin wannan, ku tsare masu alkawarin su na tsahon lokacin da kuka yi alkawarin da su, alokacin inda zaku kashe wani kafiri to wanda yayi kisan, Manzan Allah ya ce tsakanin sa da Al-jannah tshon tafiyar shekara dari biyar, haka ya bayyana acikin hadisi sahihi, ga shi kuma arne ka kashe ba musulmi ba, to ina ga dan uwanka musulmi! Ka dauki bindiga da kowanne irin dalili cikin dalilai ka rabashi da rayuwar sa, to kai kuma kayi me a bankasa? kuma mu duba muga "Al-mu'utamalun" wadan da yaki tsakanin ku da kasar su wanda akace inda daya da ga cikin su ya nemi izinin zuwa kasar ku, kuma ku ka bashi dama ya zo yayi iya ka kwanakin da zai yi, to wajibine ku tsare masa jinin sa da dukiyar sa har ya gama iyakar kwanakin da zaiyi, kuma ku yi masa rakiya har sai kunje inda zai ji ya amintu daga gare ku. Wannan ya na nuna kulawar shari’ar musulunci da dokokin Allah dangane da tsadar rayuwar biladama, ko da ya ki da aka shar’anta mana ba wai an halarta mana shi ne kawai don malalar da jinin kafirai ba, manufar shar’anta yaki ne idan kafirai suka furta kalmar shahada bisa ga zabin su sai a kyale musu jinin su, wannan tasa idan kafirai sukaki su furta kalmar shahada amma zasu shiga cikin "amman dinku" wato karkashin gwamnatinku, ku kyale su akan addinin su, baza ku kashe su ba. Ashe da manufar itace kisa to da idan amfito sai an kashe mutum koda ya yi kalmar shahada, sai ace ai anriga anfito lokaci ya kure me yasa yaki yi kafin a fito, da manufar itace kisa to da babu yadda za'a ce an samu wasu kafiran amana wadan da zasu zauna karkashin daular musulunci, kuma a tsare musu jinin su da dukiyar su ba tare da anribace su ba.

To wannan ya nuna cewa addainin musulunci addini ne da yake kare rayuwa, ba na salwantar da rayuwa bane, duk wanda dokokin addini suka ce a salwantar da rayuwarsa, to idan ka duba zaka ga babu abin da yafi dacewa sama da a salwantar da ratuwar sa, shi yasa kafirai duk kafircin su duk barnar da sukayi a bankasa, Allah ya ce idan sun tuba ta hanyar furta kalmar shahada sun bayar da zakkah, kar a kashe masu rayukansu kar a ribace su, to ina ga dan uwanka musulmi wanda ba tuba ya yi ba, dama can shi musulmi ne, bawai tuba yayi ba, yana sallah, yana zakkah, yana karatun al-qurani, da salati da istigfari gwargwadon iko, yana yi, tare da haka kace zaka rabashi da rayuwar sa da wanne dalili cikin dalilai.

Ya yan uwa dalilan da suke sanya mutane kisan kai suna da yawa, amma ga misali, yan fashi da makami wanda zasu kashe mutum don su kwace dukiyar sa sawa'un a cikin gidan sa ko akan hanya lokacin da yake tafiya a kashe shi don a kwaci dukiyar sa, to wadannan Allah ya fadi sakamakon su acikin Al-qurani hukuncin su shi ne akashe su ko a tsire su ko a yan ke musu kafar dama da hannun hagu ko kuma akore su daga kasar musulmi.

Haka kuma, ‘yan ta’adda wadan da su ba dukiyarka suke da bukata ba, rayuwarka kawai suke son dauka, saboda kawai wata manufa ta duniya da suke fatan samu, sannan da tunanin watakila kana iya zamar musu barazana wajen samun abinda suke son samu.

Wannan dai Khudba ce da Marigayi Shiekh Jafar Adam ya gabatar a masallacin Juma’a na Dorayi a lokacin da yake raye. Muna addu’ar Allah ya kai rahama gareshi, ya kyauta makwancinsa.

Shin Menene Madubi???


Madubi dai kusan duk wanda ka tambaya me ye Madubi? Zai ce maka wani abu ne da ake duba sura da shi wato zati, madubi dai kana duba shi ne yana baka zahirin zatin ka, wato yana kara tabbatar maka da cewar wannan shi ne wane. Kai tsaye zamu iya fassara ma’anar haruffan madubi kamar haka, wato MA tana nufin “Ma’auni” haruffan DUBI kuma suna nufin “Rayuwa” wannan fassara ce bisa abinda muka fahimta.

Menene Madubi? Madubi dai zamu iya cewa wani irin sinadari ne wanda ake sarrafa shi ta hanyar wasu abubuwa da ake samu misali akwai mudubin da ake kira Plane glass wanda bai da zane wato mai ruwan Garau Garau, sannan akwai madubi wanda ake kira Curves glass wato mai zane ko wanda aka yabe bayansa da wani abu, madubi an samoshi sama da shekaru miliyan daya da dari biyar da suka gabata.

Madubi dai yana baka hoton rayuwarka ne ta zahiri wadda kake acikinta. Lallai idan ka tsaya ka nutsu zaka samu cewa madubi yana baka hoton irin yadda rayuwarka ta ke, kuma madubi yana gaya maka waye kai, misali Baki, fari, gajere, dogo, kyakykyawa, mummuna da sauransu wannan shi ne kai tsaye abinda madubi yake gaya maka game da kanka.

Madubi yana tarkato Dukkan abinda yake iya kaiwa gareshi. Wato a fakaice yana gaya maka waye kai? Ina zaka? Me zaka yi? Hakika Madubi yana yin isharori da yawa izuwa gareka, amma mai hankali da lura ne kadai yake ganewa. Idan ka dauki misali madubin gefen mota, yana yi maka ishara ne da abinda yake wajen wato ina zaka je, ka kusa zuwa ko ka wuce, ko zaka fada wani wajen da bai kamata ba. Ka dauki kuma madubin mota da yake a gaba wato saman kurar mai tuka mota, yana dauko hoton abinda yake baya ne yake isar da shi zuwa ga matukin motar nan. To shakka babu haka madubi yake a cikin rayuwa, ba wai kawai yana nuna maka cewa kai wane ka yi kyau ko baka yi kyau ba a’a yana baka labarin rayuwar da ta gabata a gareka da kuma wadda zata zo nan gaba, domin idan ka tsaya tsaf ka kalli kanka sai kaga da fa ba haka nake ba, amma yanzu gashi nayi kaza da kaza.

Idan ka yi sa’a kai kadai ne a cikin daki, kuma ka dauki madubi ka duba fuskarka me ne yake fara zuwa ranka? Wani ya yi murmushi, wani ya yi sigina wa kansa, wani watakila har gwalo yake yiwa kansa, duk saboda ya samu damar ganin aininhin zatinsa a zahiri. A lokacin da ka kalli Madubi ka tambayi kanka da babu madubi duk wannan abubuwan da ke jikinka da madubi kan sada su da idanuwanka baza ka samu damar ganinsu ba. Madubi wani jakada ne a gareka da yake baka sakon izna zuwa gareka cewa lallai fa ka shiryawa mai aukuwa a gareka, domin kai matafiyi ne ba mazauni ba, kamar yadda wata mawakiya ta ke cewa “rayuwa tana faruwa wucewa take kamar ba’a yiba” shakka babu wannan haka yake, domin da za’a dauki Madubi a haska sai a hango ga wane can ya tafi, haka nan za’a yi ta wucewa kamar ba’a rayu a wannan duniyar ba.

Lallai mu tsaya tsaf mu lura da irin abinda madubi yake nusar da mu izuwa gareshi. Lallai ka duba rayuwarka ta baya ka ga me ye abinda ka aikata na kuskure ka gyara sannan kuma, ka duba abinda ya kamata ka yi a gaba. Kukan kurciya . . .

Wannan bayani ne wanda dan uwana Auwalu Adamu Tahir Sabon Gida ya taba gabatarwa, ni kuma naga dacewar na yi masa ta’alika na kawo muku.

Daga Mallam Yasir Ramadan Gwale

Tuesday, September 4, 2012

Mallam Nasiru el-Rufai: Dangajere Kusar Yaki!


Kamar yadda tsohon mataimakin Shugaban kasa Alhaji Atiku Abubakar ya taba fada a wata hira da ya yi da Jaridar This Day, cewar tsohon shugaban kasa Olushegun Obasanjo ya buka ce shi da ya zabo masa mutum mai jini a jika kuma wanda ba shi da tsoro, wanda idan ma ta kama zai iya yin akuya ga mahaifiyar obasanjon don ya bashi mukamin ministan babban birnin tarayya Abuja saboda ya dai-daitawa mutane sahu daga karkacewar da ya yi. Atiku ya shaidawa Obsanjo cewar Nasan wasu mutane guda biyu abokai da Allah bai sanya sun taba hada hanya da tsoron wani mahaluki ba a fadin tarayyar kasar nan, daya daga cikinsu kuwa shi ne Nasiru el-Rufai, wanda a lokacin shine shugaban hukumar sayar da kadarorin gwamnati ta kasa (Director General Bureau of Public Enterprises (BPE) and the Secretary of the National Council of Privatisation).

Tabbas Mallam Nasiru el-Rufai ya nuna cewar shi ba matsoraci bane, lokacin da majalisa ta zo tantance shi a matsayin mutumin da za’a nada minister. Domin idan zamu iya tunawa anyi dauki babu dadi da el-Rufai kafin a nada shi minister, inda aka nemi ya bayar da cin-hanci shi kuma ya yi kememe ya ki bayarwa, wanda wannan ta sanya wasu da yawa daga cikin shugabannin majalisa a wancan lokacin jin kunya ciki kuwa harda Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa Sanata Nasir Ibrahim Mantu, inda el-Rufai ya bayyana a majalisa dauke da al-qur’ani a hannunsa ya yi rantsuwa cewar an nemi hanci daga wajensa, kuma shi Mantu ya karyata, inda el-Rufai ya bukaci Mantu shima da ya rantse da Al-qur’ani amma hakan ta gagara inda ya ce shifa bashi da tsarki duk kuwa da cewar akwai makewayi a majalisar, kusan zamu iya cewa tun a wannan lokacin el-Rufai ya nuna jarumtaka da tabbatarwa da duniya cewar shifa ba mutumin banza bane. Wannan namijin kokari da bajinta da el-Rufai ya nuna, shi ya sa jihar Georgia da ke kasar Amerika ta bashi izinin zama dan wannan jihar, wanda yanzu haka el-Rufai yana daga cikin ‘yan Najeriya da suke zuwa kasar Amerika ba tare da anyi musu binciken kwakwaf ba.

Lokacin da Mallam Nasiru el-Rufai ya zama babban ministan babban birnin tarayya ya nuna babu sani babu sabo. Domin ya kau-da duk wasu gine gine da akayi ba bisa ka’ida ba, ciki kuwa harda gidan matar shugaban kasa marigayiya Stella Obasanjo da gidan shugaban PDP na wannan lokacin Sanata Amadu Ali da wasu manya manyan kusoshin gwamnati a wancan lokacin. Haka dai el-Rufai ya ringa sanya gireda yana ma-ke duk wani gini da aka gina shi ba bisa kai’da ba a Habuja. Mallam Nasiru el-Rufai kusan shine ministan Abuja mafi dadewa a tarihin wannan birni tun daga 1999 har zuwa 2007, kuma ya yi aiki dai-dai nasa.

Tun da Marigayi Mallam Umaru Yar’Adua ya zama shugaban kasa el-Rufai ya tsallake yabar kasar nan inda ya tafi kasar Amerika ya koma makaranta, ya halarci kwasa kwasai da dama a fannoni daban daban, ciki kuwa harda katafariyar Jami’arnan ta Harvard, kadan daga Makarantun da el-Rufai ya halarta sun hada da Jami’ar Ahmadu Bello University, Zaria, Najeryia, Jami’ar London ko University of London a Burtaniya da Harvard Business School, Arthur D. Little School of Management a birnin Massachusetts da Georgetown University da School of Foreign Services a birnin Washington dukkaninisu a kasar Amerika da kuma D.C. da John F. Kennedy School of Government da Harvard University duk dai a can Amerika. Sannan el-Rufai yana da babbar Lambar yabo ta kasa wadda ake kira OFR (Officer of the Order of the Federal Republic of Nigeria) wadda aka bashi tun yana BFE, haka kuma a shekarar 2005 jami’ar Abuja ko University of Abuja ta bashi Babban digirin girmamawa da ake kira Doctorate Degree D.Sc (honoris causa).

Bayan da el-Rufai ya dawo gida Najeriya, ya fada Jam’iyyar adawa ta CPC inda ya mara baya ga takarar tsohon shugaban kasa Gen. Muhammadu Buhari duk kuwa da ana kallon zai goya baya ne ga takarar babban abokinsa wato Mallam Nuhu Ribadu. A halin yanzu dai Mallam Nasiru el-Rufai shi ne babban bakaniken jam’iyyar ta CPC wadda Buharin ya dora masa wannan nauyi na dai-daita sahun jam’iyyar kamar yadda a yiwa birnin tarayya Abuja, saboda fama da matsaloli da jam’iyyar ta ke yi a kusan daukacin jihohin kasarnan.

Bayan haka kuma, el-Rufai shi ne kusan mutum daya tilo wanda tauraruwarsa ke haskawa wajen adawa da gwamnati mai ci ta Goodluck Jonathan da kuma Jam’iyyar PDP. Mallam Nasir el-Rufai ya dauki lokaci yana sharhi akan kasafin kudi na wannan shekarar ta 2012 inda ya yi kaca-kaca da wannan gwamnatin ya nuna ma basu san me suke yi ba. Hakan ta sanya el-Rufai ya dinga daukan hankalin jama’a a ciki da wajen kasarnan wajen yadda yake fashin baki a harkar tafiyar da wannan gwamnatin musamman a harkar da ta shafi tattalin arziki, wannan ta sanya jami’an SSS suka ringa sanya masa tarko suna kamashi a kusan duk lokacin da zai yi wata tafiya zuwa kasashen waje, haka nan yake tsallake irin wannan turaku da ake sanya masa.

Bahaushe ya ce al-kalami ya fi Takobi, lallai wannan magana haka ta ke, domin shakka babu wannan gwamnati mai ci babu wani alkalami da ta ke jin tsoro a kullum kamar na el-Rufai, domin sun san cewar mai ilimin gaske ne kuma masani ta fannoni da daman gaske. Mallam Nasiru el-Rufai dai idan ka ganshi irin mutanan nan ne da zaka gansu ‘yan tsirit wato ba shi da wani cika ido, wannan ce ma ta sanya abokansa suke masa lakabi da sunan GIANT wato wani babban mutum kamar dai yadda Bahaushe yake ce wa gajere malam dogo. Lallai kam ya zuwa yanzu babu wani daga cikin ‘yan Adawa wanda tauraruwarsa take haskawa kamar el-Rufai ba, kuma duk wannan ya faru ne ta sanadiyar al-kalaminsa da yake caccakar wannan gwamnati da shi. Tabbas maganar Bahaushe gaskiya ce da ya ce Alkamai ya fi takobi, domin idan da fada za’a iya da takobi watakila da farat daya za’a gama da el-Rufai amma da yake fadan na alkalami ne, babu yadda aka iya da shi sai dai a kayar da shi da hujja idan ana da ita.

Lallai Najeriya tana bukatar mutane masu gaskiya wadan da zasu iya yakar cin-hanci da rashawa da gaskiya kuma hazikai irinsu Mallam Nasiru el-Rufai.

Daga marubuci Mallam Yasir Ramadan Gwale.

Monday, September 3, 2012

Babbar Magana: Tsakanin Shugaba Goodluck Da Fastor Tunde Bakare


Bari mu waiwayi tarihi na baya-bayan nan. La’alla a matsayinsa na fasto, dan siyasa, mai wa’azi, mutumin Allah, lauya ko mai kwato hakkin ’yan kasa – wanda dukkansu shi ne – Fasto Tunde Bakare a koyaushe ya kasance mai akida kuma maras wargi...

A matsayinsa na lauya ya yi aiki a karkashin Gani Fawehinmi. A 1999, a lokacin da kusan kowa ke zumudin takarar Olusegun Obasanjo, Bakare ya fito gaba-gadi ya ayyana cewa ba a dauko mai ceton al’umma ba. Ya yi ikirarin cewa, a hakikani ma dai Obasanjo zai sake yamutsa matsalolin Nijeriya ne. Tuni a ka tabbatar da gaskiyar batunsa a aikace. Ba ma haka kadai ba, Obasanjo ya zama annoba ta yadda ya dasa harsashin gurbataccen shugabancin da duk ya biyo bayansa.

A lokacin da Shugaba Umaru Musa Yar’Adua ya gaza saboda jinya, kwakwalwarsa ta daskare kuma ’yan ma’abban gwamnatinsa su ke amfani da rashin lafiyar wajen hana mataimakin shugaban kasa na lokacin, Goodluck Jonathan, ya gaje shi, Fasto Bakare ya jagoranci kungiyar Save Nigeria Group (SNG) wacce ta tilastawa ’yan siyasar aikata abinda ya dace. A yanzu Shugaba Jonathan ya shaku da sabbin abokansa har ya mance da kokarin Fasto Bakare a mawuyacin lokaci. Dukkanmu, har shi Tunde Bakare, mun dage a kan sai an aiwatar da sashe na 144 na kundin tsarin mulkin kasa ne, wanda zai bai wa mataimakin shugaban kasa Jonathan darewa karagar mulki kai tsaye ba wai a matsayin mai rikon kwarya ba, saboda hakan ne daidai. Ni na ga wautar majalisar dattawa ma da su ka yi amfani da wani abu wai shi ‘matakin tilashi’ su ka ayyana mataimakin shugaban a matsayin shugaba na rikon kwarya alhali sashe na 144 a fayyace ya ke kan abinda ya dace kasar ta aikata a irin wancan hali.

Fasto Bakare ya kausasa harshe ga masu rike da madafun iko kamar yadda littafin Bible ya wa’azantar. Ba wai kawai rashin tsoro ne da faston ba, ya na ma da kwakwalwar yin kyakkyawan hasashe.

’Yan kwanaki kadan da su ka gabata, jami’an tsaro na farin kaya, SSS, su ka gayyaci faston bisa lafazansa. Akwai shakkun cewa idan SSS za su iya gayyatar Bakare ba tare da izinin shugaban kasar ba. Wannan cin zarafi ne ga ’yancin fadar albarkacin baki kuma hakan bai dace da dimukradiyya ba a ko’ina cikin duniya. Irin wadannan ne abubuwan da su ke faruwa a Nijeriya lokaci zuwa lokaci wadanda ke nuni da cewa babu dimukradiyya a Nijeriya sabanin abinda a ke ikirari. An gayyaci Fasto Bakare ne saboda ya ce makomar Jonathan ita ce talauta Nijeriya bisa la’akari da irin almundahanar da a ke tafkawa a kasar tun ma kafin 2015. Abinda Bakare ya fadi kenan. Har yanzu babu wanda ya shaida mi ni cewa an gano bindigu ko bama-bamai a gidansa ko mujami’arsa da za a iya yin kokwanton cewa ya na shirin kifar da gwamnatin Jonathan ne ko kuma a matsayin wata shaida da ke nuna cewa shi dan ta’adda ne.

To, amma mene ne laifin kalaman na Fasto Bakare, dan takarar mataimakin shugaban kasa na jam’iyyar CPC a zaben 2011? Idan don ya ce makomar Jonathan ita ce talauta Nijeriya, to me ye laifi a wannan? Shin ba abinda Jonathan ke aikatawa din ba kenan? Idan har Jonathan zai iya barnata Naira tiriliyan 2.6 ga masu kawo mai na karya, alhali sauran shugabannin kasar na baya su na kashe kasa da biliyan 300, ta yaya ma wani zai ga laifin lafazan Bakare? Ko kuwa shugaban ya na so ya mari ’yan Nijeriya ne ya kuma hana su kuka? Gaskiyar magana ita ce, idan har shugaban kasa zai kashe tiriliyan 2.6 a shekarar zabe maimakon biliyan 245 na tallafin mai, shin ba zai zama abu mai sauki ga dan kasa ya ce Jonathan ya na neman tsiyata kasarsa ba? Kai Bakare ma ya yi sassauci da yawa ga shugaban kasar. Lamarin ya fi haka la’acewa. Idan da a ce dimukradiyya na aikinta yadda ya dace, ai da tuni an tsige shi bisa aikata wannan danyen aiki na barnata tiriliyan 2.6 ba bisa ka’ida ba.

Faston ya kuma nusar da cewa, a matakin da cin hanci ya ke a kasar da Jonathan ke jagoranta, babu fa’ida a yi magana ma kan 2015. Fasto Bakare ya furta abinda kowa ke furtawa ne. Ya yiwa shugaban alfarma ne ma da ya sanar da shi abinda kowa ya fadi – ciki kuwa har da wadanda ke ikirarin su na tare da shi – amma su ke fadi a bayan idanunsa. Ni Ina mamakin yadda babu wanda ya taba bude baki ya gaya ma sa gaba da gaba. Tiriliyan din Nairori da a ka sace a karkashin kulawar Jonathan za su iya sanyawa kasar ta durkushe idan ba a hana ba.

Sace kudin tallafin mai, fashin kudin ’yan fansho, wawure gangar mai akalla 400,000 kullum ba bisa ka’ida ba, cefanar da rijiyoyin mai 245 da sauransu da sauransu ba abubuwa ne da sa mu su idanu ba. Eh, Nijeriya ta yi suna wajen tafka almundahana a idanun duniya, amma ba irin wannan rashin hankalin da mu ke gani a gwamnatin Jonathan ba. Wannan ne hakikanin abinda ya hana komai aiki a kasar. Lokacin da Jonathan ya yi alkawarin kawo sauyi, ba mu san irin sauyin da ya ke magana a kai ba. Hatta Naira biliyan 300 da Yar’Adua ya saki kafin ya kwanta jinya don gyara yankin Neja Delta, har yau ba a san inda su ka kwana ba. Rabin kudin PTF ta kashe a kasar bakidaya a ka ga bambanci.

Kuma ma don karin abin haushi shi ne Shugaba Jonathan ya umarci matsiyancin gwamnan can Henry Seriake Dickson na jihar Bayelsa ya nada matarsa mukamin babbar sakatare. Hakan ya biyo bayan bai wa bokansa, Tompolo, kwangilar tsaron tashar sauke kayan da a ka yi jigalar su a jirgi ne fa. Watarana lokaci zai zo wanda a bainar jama’a za a shaidawa ’yan Nijeriya hakikanin dangantakar Jonathan, babban kwamandan askarawan Nijeriya, da dan bindiga (tsoho ko mai yi), wanda ayyukansa su ka halaka sojoji da dama a kasar. ’Yan Nijeriya da dama har ma da ’yan kasashen waje sun shiga rudani kan ainihin dangantakarsu. Hakika lamari ne mai cike da dimuwa.

Ya kamata Shugaba Jonathan ya san cewa, ’yancin fadar albarkacin baki ya na daya daga cikin alfarmar dimukradiyya. Kamar yadda ’yancin wallafawa da yin abota su ke, haka nan fadin albarkacin baki ba za a turbude shi a dimukradiyya ba. Tauye hakkin fadin albarkacin baki ya zama al’ada a gwamnatin Jonathan. Shugaban ya na so ne ya rika aikata duk abinda ya ga dama ba tare da a na sanya ma sa shingaye ba. Ya na son kashe Naira tiriliyan 2.6 a shekarar zabe duk da majalisar dokoki ta kasafta Naira biliyan 245 ne kacal, amma ba ya so Fasto Bakare ya ce kanzil! A bara an tsare Nasir el-Rufai, daya daga cikin ’yan adawa na siyasa, a filin saukar jiragen sama, saboda rubutun da ya yi a kan shugaban kasar, kuma a 2011, gabanin zabe, jami’an SSS sun gayyaci Bola Tinubu saboda ya ce, ’yan Nijeriya su daina sauraron bugaggen mai kamun kifi, wato ya na nufin Jonathan. Martani ne fa ga Jonathan din bisa kiran ’yan jam’iyyar ACN da ya yi da ‘’yan iska’ a lokacin da ya ce “Kudu maso Yamma ta wuce a bar wa ’yan iska ita”. Tabbas al’ummar yankin Kudu maso Yamma sun mayar da martani ta hanyar kin zaben jam’iyyar Jonathan da Obasanjo a bakidayan yankinsu, kuma a nan an gane su wa su ka mayar ’yan iskan.

Abu ne mai wahala ga duk wanda ke kaunar Nijeriya ya iya tsuke baki ya na kallon yadda a ke tafiyar da kasar a halin yanzu. Fasto Bakare ya taimakawa shugaban kasar ne kawai don ya fahimci yadda ’yan Nijeriya ke ji a ransu game da shi. Fasto Bakare ya kuma ce, juyin-juya hali lallai zai afku a Nijeriya, saboda salon yadda a ke tafiyar kasar, musamman kan irin yadda a ke barnatar da arzikin kasar.
Shugaban ya nuna cewa, hakan fa ko a jikinsa. Shugaba Jonathan ya kamata ya sani cewa, ya na rubutawa kansa tarihi ne ta hanyar sigar da ta tafiyar da Nijeriya. Don haka tilas ya sauya salonsa ya kuma fara nuna halin-ko-in-kula.

Daga Jaridar Leadership Hausa

Saturday, September 1, 2012

Buhari Ya Ziyarci Kwankwaso


Tsohon Shugaban kasa kuma dan takarar Shugaban kasa a zaben bara a karkashin Jam’iyyar CPC Janar Muhammadu Buhari ya kai ziyarar jaje ga Gwamnan Jihar Kano Dokta Rabi’u Musa Kwankwaso dangane da tashe-tashen hankula da jihar ke fama da su,

inda ya nemi Gwamnatin Tarayya ta yi duk abin da za ta iya don kawo karshen rashin tsaro da ke dada tura mutane cikin ‘bakin talauci’ a Arewa.
Janar Buhari wanda ya ziyarci Gwamna Kwankwaso a shekaranjiya Laraba ya bayyana rashin tsaro a Jihar Kano da wasu jihohin Arewa a matsayin “Babban abin bakin ciki,” inda ya ce ya yi matukar kawo nakasu ga kasuwanci da sauran harkokin tattalin arziki.
Janar Buhari ya ce: “Na zo ne domin in gaida Mai martaba Sarkin Kano kuma in yi muku jaje kai da shi kana bin bakin cikin da ke faruwa na tashin bama-bamai da kuma tsauraran matakan tsaron da ake dauka da suke takura wa jama’armu.”
Janar Buhari, wanda ya je jihar don bude sakatariyar Jam’iyyar CPC ya ce, Kano wadda a baya ta yi suna a duniya wajen harkar kasuwanci a yanzu tana neman komawa kufai. “Wannan babban abin bakin ciki ne, kuma ina fata za ku kawo karshen hakan cikin gaggawa,” inji shi.

A cewar Buhari, duk da macewar kamfanoni da matakan tsaron da ake dauka a Kano, ba kowa ne daga farko ya fahimci tabarbarewar al’amuran tattalin arziki a kasar nan ba, “said a matsalar Borno da Yobe ta yi kamari,” inji shi.
“Kasancewar na yi Gwamna a yankin, na san a kullum akalla motoci 200 ke barin nan zuwa Maiduguri wasu kuma su yiwo nan. Kuma a Maiduguri za ka iske ’yan kasuwa daga kasashen Kamaru da Chadi da Nijar. Wanna yanzu ya zama tarihi. Ku tsaya ku yi nazari dimbin ’yan Najeriya musamman na wannan yanki da a yanzu aka jefa su a cikin mummunan talauci. Don haka ina fata gwamnatin tsakiya za ta yi duk abin da za ta iya wajen an magance matsalar cikin gaggawa,” inji shi.

Daga nan sai Janar Buhari ya ce Jam’iyyar CPC za ta bude sakatariyarta a Kano ne, domin ta kintsa tare da taka rawar ’yar adawa ganin an riga an kawo karshen rikicin cikin gida da ke damunta.

A nasa jawabin Gwamna Rabi’u Kwankwanso ya ce, gwamnatinsa tana aiki da hukumomin tsaro don janye shigayen duba ababen hawa, domin ba jama’ar damar walawa da shiga da faitar da kaya daga jihar.

Gwamna Kwankwaso ya yaba wa Janar Buhari kan samun lokaci ya kai masa ziyarar girmamawa duk da bambancin jam’iyya da suke da shi. “Abin da Janar ya yi shi ne abin da ya kamata dukkan ’yan siyasa su rika yi, saboda bambancin siyasa ba yana nufin zama abokan gaba ba ne.”

A yayin da yake gabatar da jawabi a harabar sakatariyar jam’iyyar, shugaban rikon Alhaji Muhammad Ahmad ya bayyana farin ciki da ziyarar ta Janar Muhammadu Buhari, a inda ya ce “ziyarar tana da muhimmanci wajen tabbatar da kawo gyara a cikin jam’iyyar, tare da tabbatar da hadin kai a tsakanin mabiyanta a jihar.”
Sai dai Janar Buhari wanda ya isa wajen taron a cikin bakar mota kirar Jeep, bai samu sukunin fitowa daga cikin motar ba, sai dai ya fito da kansa ta tagar rufin motar, inda ya rika karbar gaisuwa, tare da daga hannunsa ga cincirindon jama’ar da suka taru, sannan ya bar wurin.

Daga cikin wadanda suka yi masa rakiya akwai Shugaban Jam’iyyar CPC na kasa Yarima Tony Momoh da dan takarar Gwamnan Kano na jam’iyyar a zaben bara Janar Lawal Ja’afaru Isah da tsohon Shugaban Majalisar Tarayya Aminu Bello Masari da Alhaji Faruk Adamu Aliyu da Alhaji Sule Yahaya Hamma da Alhaji Buba Galadima da Alhaji Nasiru Baballe Ila da Abdulmajid dan Bilki Kwamanda da Kantoman Jam’iyyar CPC na Jihar Kano Dokta Mohammed Ahmed da sauran jami’an jam’iyyar na jihar da na kasa.

Daga Jaridar Aminiya

Wednesday, August 8, 2012

Musulmai Ba Za Su Yi Ittikaf Wannan Shekarar A Jihar Kano Ba

Masarautar jihar Kano ta bada umarni dakatar da yin Ittikaf a masallatan jihar a wannan shekara.

Ittikaf dai ibada ce da Musulmai suke yin ta a lokacin watan Ramadan, musamman idan ya rage saura kwanaki goma, inda ake yin kaura daga gida zuwa manyan masallatai, domin kara zage dantse wurin yin ibada da kara neman kusanci ga mahalicci Allah, wannan ibada ta samo asali tun lokacin Fiyayyen Halitta Annabi Muhammad (SAW).

Sanarwar ta fito ne a daren jiya Talata, a kafafen yada labarai dake jihar ciki har da gidan rediyon Kano mallakin gwamnatin jihar. Duk da a cikin sanarwar ba a bayyana dalilin daukar wannan mataki ba, amma wata majiya ta bayyanawa RARIYA hakan na da nasaba da harkokin tsaro da yake addabar jihar.

Wannan dai shi ne karo na farko da hukumomi a jihar suka taba yanke irin wannan hukunci tun bayan jaddada addinin Musulunci da Shehu Usman Danfodio yayi a jihar ta Kano.

Cristiano Ronaldo Ya Yi Nasara Zama Zakaran Shekara a Shafin Goal.com

Dan wasan gaba, na kungiyar Real Madrid, Cristiano Ronaldo ya zama Zakaran Shekara a shafin yanar gizo na Goal.com (Goal.com 50 Prices) na 2011/2012.

Shafin na Goal.com a duk shekara yana sanya gasar ne ta zama zakarar shekara a tsakanin gwarazan 'yan wasan kwallon kafa guda 50 wanda makaranta shafin ke zaben wanda ya fi cancanta a tsakanin 'yan wasan.

Ga jerin 'yan wasa 10 farko da suka fi samun maki:

1. Cristiano Ronaldo 38.82%
2. Lionel Messi 35.51%
3. Andrea Pirlo 12.25%
4. Didier Drogba 5.46%
5. Iker Casillas 4.07%
6. Andres Iniesta 1.57%
7. Yaya Toure 0.72%
8. Xavi Hernandez 0.63%
9. Ashley Cole 0.58%
10. Sergio Ramos 0.4%

Wannan nasara da Ronaldo ya samu za ta iya taimaka masa wurin lashe kambun gwarzon dan wasan duniya na Ballon d'Or da hukumar FIFA ke sanyawa a duk shekara ga dan wasan da ya fi gwazo a fadin duniya ta fannin kwallon kafa.

Daga Jaridar Rariya

Friday, July 27, 2012

Duniya Ina Za Ki Damu?


Wannan hoton wani matashi ne da jami'an tsaro suka cafke a Abuja dauke da kan yaron wani makwabcinsa dan shekara bakwai.

Matashin mai suna Joan Yakubu dan shekara 25, jami'an tsaron sun yi nasarar cafke shi ne a AYA, Asokoro tare da rakiyar wani abokinsa mai suna Ishaya Dukulung mai shekaru 30.

Kamar yadda matashin ya bayyana, ya ce abokinsa ne ya shawarce shi da su nemo kan mutum don su saida shi ga wani mutum a Abuja.

Rahoto Daga Jaridar Rariya

Barka Da Shan Ruwa!!!

Ranar Ba Ta Karya - Yau Za'a Fara Gasar Olympics a Birnin London


Hankulan mutanen duniya, ya karkata zuwa birnin London a yau, sakamakon kammaluwar shirin fara gasar wasannin Olympics a yau din, akalla mutane sama da biliyan hudu ne za su kalli wannan biki na bude gasar a sassan duniya daban daban

Firaministan Burtaniya, David Cameron ya bayyana cewa kasarsa ta shirya tsaf domin daukan bakuncin gasa mafi girma a duniya, gabannin bikin bude gasar wasannin Olympics da za a yi nan gaba a yau.

Mr. Cameron ya ce "Gasar wani abun alfahari ne ga Burtaniya, kuma ya kamata jama'ar kasar su karbe ta hannu biyu-biyu".

Tun farko dai an kada karaurrawa a sassa daban - daban na kasar ta Burtaniya, kuma an yi ta zagayawa da wutar gasar wasannin ta Olympics a kan kogin Thames dake tsakiyar birnin na London a cikin wani jirgin ruwan Gidan Sarauta da aka kawata shi da adon Gwal.

'Yan wasa sama da 15,000 za su fafata a wasanni sama da 300 a gasar ta Olympics.

Wednesday, July 25, 2012

Gajeren Sako Ga Makaranta Wannan Dandali

Aminci A Gare Ku!!!

Ina taya mu murnar shigowarmu watan Ramadan mai Alfarma, Allah ya gafarta mana, ya biya mana bukatun mu alfarmar wannan wata, ya sa muna daga cikin wadanda za a 'yanta a cikin wannan wata.

Nayi wannan rubutu ne a yanzu sakamokon kirana da wasu bayin Allah da suke karanta abubuwan da nake rubutawa a wannan Dandali, a waya suke tambaya ta ko lafiya kwana biyu ban cika yin rubutu ba kamar yadda na saba yi a da?

Na san wasu za su iya sanin dalilin yin hakan, ba komai bane kuwa sai don shigowar wannan wata, saboda akwai bukatar idan watan ya shigo duk wani abu da mutum yake yi ya dakatar da shi ya kusanci Allah, yayi ta rokon gafara da rahama, saboda kuwa idan wannan dama ta wuce sai kuma Allah ya kaimu wata shekarar, wanda kuma hakan ne babu tabbacin ko zamu sake ganin wani Ramadan din na gaba.

Ya Allah ya amshi ibadunmu.

Sunday, July 15, 2012

Hadin Kai Tushen Nasara: ACN/CPC Sun Yi Nasara a Jihar Edo



Gaskiyar Turawa da suka dade suna fada da nanatawa a harshensu na Turanci ko nace na Nasara cewa "United We Stand" Domin kuwa na fahimci hadin kan shi ne tushen nasara, ba komai ya sa na fahimci hakan ba sai don yadda naga cewa duk lokacin da wasu gungun mutane ko daidaiku suka hada hannun domin cimma wata manufa to tabbas ko shakka babu sai naga sun yi nasara, ba tare da shan wasu wahalhalu ko haduwa da wani kalubale ba, irin haka ta sha faruwa shekaru daruruwa da suka shude, kuma wani abin mamaki har a yanzu wannan lokaci hakan na ci gaba da faruwa, kuma faruwar hakan a wannan zamani shi ne yake tabbatar mana da lallai hakan zai faru anan gaba, faruwar hakan a gaba kuma manuni ne na ci gaba faruwar haka har abada, wato har karshen wannan zamani kenan.

Na fara da wannan batu ne na hadin kai saboda yadda naji zaben jihar Edo ya wakana a jiya Asabar, wanda ya bawa Adams Aliyu Oshiohomle nasara, karkashin jam'iyyarsa ta ACN tare da hadin gwiwar jami'yyar CPC, da gagarumin rinjaye akan jam'iyyun PDP da ANPP da suka fafata a zaben.

Wannan nasara da Adams Oshiomhole ya samu wani darasi ne da dukkan 'yan Nijeriya masu sun canji na alheri da ci gaban kasar da al'ummarta. Darasin da ke cin wannan nasara ta Oshiomhole shi ne hadin kan da jam'iyyar CPC da ACN suka yi har suka samu nasara.

Sai naga ashe da wadannan jam'iyyu na CPC da ACN da wasu sauran jam'iyyun da suke ikirarin suna yi ne don talakawa to da ashe a lokacin zaben 2015 da mun samu nasara, saboda Hadin Kan shi ne Tushen Nasara.

Monday, July 9, 2012

Shafin Sada Zumunta Na Facebook

Sunan Facebook ba boyayye bane ga matasan wannan zamani maza da mata, musamman masu mu’amala da fasahar yanar gizo. Domin kuwa koda mutum baya amfani da shafin ba zai kasa jin masu mu’amala da shi suna zancensa ba.

Duk da dai ba duk aka taru aka zama daya ba wato dai ba za’a rasa ‘yan tsirarun mutanen da basu san wannan shafi na Facebook ba, ko kuma idan sun san shi basu san wace irin mu’amala ake dashi ba, kai wasu ma suna amfani da shafin amma basu fahimce shi ba, domin kuwa idan zaka tambaye su menene amfanin Facebook, ka basu aiki ba karami ba. To idan kana daya daga cikin wanda basu san menene Facebook ba ko kuma kana daya daga cikin wadanda sun sanshi amma basu san amfaninsa ba, kai har ma da wadanda suka san shafin kuma suka san amfaninsa ku dan bani hankalinku na dan lokaci dan sanin menene Facebook, wa ya kirkire shi, don me aka kirkire shi, menene amfaninsa da sauran batutuwa makamantan hakan.

Facebook dai dandali ne na sada zumunta kuma yana daya daga cikin miliyoyin shafukan dake kunshe a rumbun yanar gizo wato Internet. Kamar irinsu shafukan Twitter, MySpace, Google+ da sauransu, sai dai shafin na Facebook ya banbanta da shafukan dana bayyana a sama ta hanyoyi da dama. Facebook shafi ne da wani dalibi mai suna Mark Zuckerberg ya kirkire shi tare da wasu abokan karatunsa su uku Eduardo Saverin, Dustin Moskovitz da kuma Chris Hughes, a ranar 4 February 2004. A makarantar Harvard a jihar Califonia dake kasar Amurka.

Wadannan dalibai sun kirkiri shafin ne don amfani dashi a makarantarsu kawai, don haka cikin dan lokaci kankani shafin ya baibaye ilahirin wannan makaranta, saboda irin farin jinin da shafin ya samu a wurin daliban makarantar Harvard ba’a dau lokaci mai tsawo ba shafi ya tarwatsu zuwa sassan manyan makarantun kasar Amurka baki daya. Kafin kace me tuni shafin ya tsallaka zuwa kasashen Canada da England, wajen shekarar 2005 shafin ya karade gaba dayan yankin kasashen turawa da yankin Amurka ta kudu.

A ranar 26 ga watan 9 na shekarar 2006 kamfanin Facebook ya bayyana cewar kowa zai iya mallakar shafin a duk inda yake a duniya indai ya haura shekaru 13 da haihuwa. Shafin Facebook shafi ne da kowa zai iya amfani dashi cikin sassakar hanya, shafi ne da masu amfani dashi ke samun damar haduwa da mutane kala kala daga kasashen duniya daban – daban, shafin yana da kayatarwa, nishadantarwa, ilimintarwa, shagaltarwa har ma da wa’azantarwa. Shafi ne daya hada al’ummatai kala – kala mabanbanta ra’ayi, kabila, addini, yare da kuma tarbiya. Haka yasa duk irin manufar da tasa mutum amfani da shafin yake samun ‘yan uwansa.

Facebook ya bawa masu amfani dashi dama wurin baje kolen ra’ayinsu, ba tare da tsangwama ko hana ‘yancin magana ba, wannan dalilin yasa Facebook ya tserewa dukkan wani shafi na sada zumunta wato social network a turance yawan masu amfani dashi. Kamar yadda kamfanin ya shaida cewar yana da sama da mutum miliyan 750 masu amfani da shafin a kiyashin da akayi a watan bakwai na shekara ta 2011.

YADDA AKE BUDE SHAFIN FACEBOOK

Da farko mutum zai tanadi adireshin email mai amfani ko kuma lambar waya, sannan sai mutum ya zarce kai tsaye wurin da yake shigar da adireshin gidajen yanar gizo idan zai nemo bayanai (browsing) a na’ura mai kwakwalwarsa (computer) ko kuma wayarsa ta hannu (handset). Sai ya shigar da adireshin shafin na Facebook kamar haka http://www.facebook.com idan kuma a wayar hannu ne sai ya shigar kamar haka http://m.facebook.com da zarar ka shiga zaka ci karo da inda aka rubutu SIGNUP sai a latsa nan daga nan kuma za’a aiko ma da form da zaka cike don zama daya daga cikin miliyoyin dake amfani da shafi.

Bayan an kammala cike form din gami da shigarwa, anan za’a bukaci ka tabbatar da email ko lambar wayar da kayi amfani dasu naka ne, wato kamfanin na Facebook zai turo sako ta cikin abinda ka zaba wurin budewar email ko lambar waya, hade da adireshin da zaka latsa ko lambobin sirri da zaka shigar don kammala rijistar Facebook din naka, da zarar ka shigar ko ka latsa adireshin da aka turo ma shi kenan ka zama daya daga cikin masu amfani da dandalin sada zumunta na Facebook.

Bayan nan kuma sai ka shiga shafin naka don sa hotonka gami da karasa cike ‘yan bayanai da suka dangance ka misali kamar: sunan garinku, addininka, abinda kafi sha’awa, yaren da kake ji, makarantar da kayi ko kake yi ko kuma wurin da kake aiki da sauran bayanai da suka shafe ka, domin saukakawa masu son mu’amula da kai ba dole sai suna tambayarka ba.

Daga Mujallar Duniyar Computer

Bashir Ahmad
Bashirgy@yahoo.com
08032493020

Ra'ayin Aminiya: Kalubalen Dake Gaban Sambo Dasuki


Mako biyu da suka gabata ne Shugaba Goodluck Jonathan ya bayar da sanarwar sallamar Janar Andrew Owoeye Azazi daga mukamin Mai Bayar da Shawara ga Shugaban kasa kan Harkokin Tsaron kasa (NSA). Kuma ya sallami Dokta Bello Haliru Muhammad daga mukaminsa na Ministan Tsaro. Kuma a take cikin sanarwar ya bayyyana nada wani Kanar din soja mai ritaya Alhaji Sambo Dasuki a matsayin Mai Bayar da Shawara kan Harkokin Tsaro na kasa don maye gurbin Azazi; sai dai ba a fadi wanda zai maye gurbin Dokta Halliru ba. Sauye- sauyen manyan shugabannin tsaron kasa sun zo a lokacin da kasar take fama da kalubale a bangaren tsaro. Don haka Sambo Dasuki ya san irin aikin da ke gabansa.

kalubalen Boko Haram na nan, wadda a fagen siyasa ake kallonsa a matsayin babbar barazana ga dorewar kasar nan a matsayin kasa daya. Tun shekarar 2009 kungiyar ta fara adawa ga hukumomin kasar nan inda a karshe ta kai ga kaddamar da hare-haren da suke jawo hankalin manyan kasashen duniya kan yadda Najeriya ke neman zama dandalin ayyukan ’yan ta’adda. Kuma a makon jiya sai ga sashin harkokin cikin gida na Amurka ya bayyana wasu fitattun ’yan Boko Haram uku a matsayin ’yan ta’adda. Yin hakan kowa wani cikasa ne ga kasar nan da al’ummarta. Sai dai ba Boko Haram ne kawai matsalar da ke barazana ga zaman lafiya a tsakanin ’yan Najeriya ba, kuma ke kawo gibi a tsakanin hulda tsakanin Najeriya da sauran kasashe ba.

Mugun aikin nan na sata da garkuwa da mutane don a samu kudi da aka fi yi a kudancin kasar nan shi ma matsala ce da ke damun kasar nan, kuma ga alama matakan da hukumomi ke dauka sun kasa kawo karshen lamarin. Matsalar ta fi kamari a yankin Neja-Dalta, inda babban dalilin yin hakan shi ne a kwakuli kudi ko ta halin kaka. A wasu lokuta wadanda aka yi garkuwar da su kan rasa rayukansu koda an biya kudin fansar. Fashi da makami ma wata mummunar matsala ce ga harkokin tsaron kasar nan.

A ’yan kwanakin nan an rika cuda ayyukan da suka shafi keta harkokin tsaro ta hanyar fashi da makami da batun Boko Haram, a wasu lokuta akan bayar da bayanan karya kan hakikanin barazanar kungiyar a wasu jihohi musamman a Arewa. Kuma babban bangaren da mabarnata suka fi baje kolinsu shi ne bangaren satar man fetur, inda kasar nan ke tafka asara daga gagarumar satar danyen manta. Ba abin mamaki ba ne da suka mayar da hankali wajen wannan aika-aika a yankin Neja- Dalta.

Manyan kamfanonin mai ciki har da Shell sun ruwaito mummunar sace danyen man fetur da ake yi wa Najeriya. Wasu su kiyasta ana sace danyen man ganga dubu 400 a kullum. Muhimmancin kawo wadannan bayanai ita ce, duk da kasancewar jami’an tsaro a daidaikunsu da kuma a hade ta hanyar Rundunar Musamman ta Soja (STF) da ke suke aiki domin dakile wadancan barayi, satar tana ci gaba da gudana, inda barayin ke samun biliyoyin Dala a shekara, kuma akwai yiwuwar da hadin bakin jami’ai ko hukumomin tsaron. Idan aka tattaro irin wadannan matsaloli za a ga cewa Sambo Dasuki zai fuskanci matsaloli masu yawa kuma masu wahala da suka shafi tattalin arziki da siyasa ba sun takaita ga ayyukan Boko Haram na zubar da jini kadai ba ne.

Yana da kyau Dasuki ya fahimci yanayin hadakar al’ummar Najeriya da dalilan da suke kawo irin wadancan miyagun ayyuka a tsakanin jama’a, domin nemo maslahar da ta dace. Akwai matsalolin da suke da tushe daga siyasa saura kuma daga kuncin rayuwa. Mafi yawansu kuma tantagayyar ayyuka ne na miyagu. Kowanne zai bukaci magani na daban; fahimtar tushensu zai sa a samu maganin da ya dace wajen kawar da su. Wajibi kuma Dasuki ya koyi darasi daga kura-kuran Azazi, babba daga ciki dabi’ar bangaranci da ya kawo a yayin gudanar da aikinsa na Mai bayar da Shawara kan Harkokin Tsaro na kasa. A lokacinsa, tunanu da inda yake zuwa sun takaita ne ga halartar tarurruka da al’amuran da suka shafi tsaro idan wurin da ake taron yana yankin Kudu maso Kudu. Ya shuka tare da rainon tunanin cewa matsalar tsaro abu ne a tsakanin Arewa da sauran sassan kasar nan, ya daukaka matsayin Boko Haram zuwa babbar ko ma ita ce kadai barazana ga mulkin Shugaba Jonathan ta kokarin kakabata ‘ga ’yan siyasar Arewa da janar-janar masu ritaya.’

Babu wani bayani da ya nuna Azazi ya taba ziyartar wuraren da aka yi artabu a Arewa, musamman Damaturu a Jihar Yobe da Maiduguri a Jihar Borno, tunda aka fara kai hare-haren bama-bamai shekara biyu da suka gabata, domin gane wa idonsa akalla koda ya fahimci irin kalubalen da ake fuskanta. Ta hanyar zuwa wuraren a Alhamis din makon jiya, Dasuki ya nuna ya yi niyyar gano bakin zaren wannan matsalar. Kuma wajibi ne ya tafi Kudu ya duba wurare masu matsaloli ya auna abubuwa da kansa kafin ya zauna don fuskantar wannan babban kalubale ba tare da ya jefa kansa a cece-ku-ce marasa amfani ba.

Daga Jaridar Aminiya

Sunday, July 8, 2012

Seydou Keita Ya Bar Barcelona Zuwa China


Seydou Keita dan kasar Mali ya bar kungiyar Barcelona bayan shekaru hudu a kungiyar.

Dan wasan tsakiyar ya sanar da cewa ba zai cigaba da bugawa kungiyar wasa a kakar wasanni mai zuwa ba. A nata bangaren kungiyar Barcelonan ta yabawa Seydou Keita a kan gudummawar da ya baiwa kulub din a shekarun da suka gabata tare kuma da yi ma sa fatan alheri a rayuwarsa ta wasan kwallon kafa da kuma harkokinsa na rayuwa.

Keita wanda ya dauki kofuna goma sha hudu da Barca ana ganin ya na shirin komawa kasar China da wasa a kungiyar Dalian Aerbin. Keita dan shekara 32 ya koma Barcelona ne daga kungiyar Seville a 2008 kuma shi ne na farko da Pep Guardiola ya fara dauka da ya zama kocin kungiyar.

A shekara ta 2014 ne kwantiragin dan wasan zai kare da Barcelona, amma a bisa yarjejeniyar da suka kulla , ya na da damar barin kulub din idan ba a sa shi a farkon wasannin kungiyar ba a akalla rabi na kakar wasannin da ta gabata.

Guardiola ya rika sanya dan wasan a matsayin canji na tsawon lokaci, kuma Keita ya taimakawa kungiyar ta sami nasarar daukar kofunan Laliga uku da na zakarun Turai biyu da Kofin Sarki (king's cup) guda biyu da sauransu. Seydou Keita ya bugawa kungiyoyin Marseille da Lorient da Lens dukkanninsu a Faransa kafin ya tafi Spain inda ya yiwa Seville wasa na shekara daya sannan daga bisani ya koma Barcelona, wadda ita ma yanzu ya bar ta.

Yanzu dai Keita ya bi sahun Didier Drogba da Frederick Kanoute da Yakubu Aiyegbeni wajen komawa China don wasa.

Daga BBCHausa.com

Sunday, July 1, 2012

Kukan Kurciya: Tattaunawa Tsakanin Malam Habu Da Malam Jatau Game Da Kudirin Kayyade Haihuwa


Malam Habu! Malam Habu!! Dakta Habu!!! Malam Ha.......

Na'am! Na'am!! Malam Jatau, ina zuwa haka da ranan nan?

Hhmm! kafin na baka amsar tambayarka, anya lafiya kuwa ka zauna kake irin wannan tunani, nayi ta kiranka kusan sau hudu kafin ka amsa?

Malam Jatau kenan, ni fa da kai duk 'yan Nijeriya, kuma zan iya cewa ba zai zama abin tambaya ba, ga duk dan Nijeriyar da ka gani ya dukufa ya bata lokaci mai tsawo yana tunani, saboda a wani lokaci da muke ciki ko kankanin yaron da bai san menene tunani ba, za ka ganshi lokaci lokaci yayi shiru baya cewa da kowa komai, da kuwa za kayi katarin tambayarsa mai yake damunsa? Amsar da za ta fito daga bakinsa zai ce ma "Halin da Nijeriya ke ciki" to ka ga kuwa ni ma idan ka ganni cikin wannan hali bai kamata ka daga hankalinka ba.

Malam Habu kenan gwanin iya sarrafa zance, to kai yanzu menene ya saka wannan dogon tunani game da Nijeriyar?

Hhmm zahiri abubuwa ne marassa adadi suke damuna da hana zuciyata sukuni game da wannan kasa tamu, yau kwana uku kenan ina yin tattaki har gidanka, domin mu zauna mu tattauna akan wannan al'amari daya ta so, amma bana yin sa'ar samun ka, kullum sai mai dakinka ta bayyana min cewa tun sassafe ka tafi gona, kuma ba cika dawowa ba sai daf da Magriba.

Eh haka ne kam, ka san manomi da zarar ruwan damuna ya sauka ba shi da wani lokaci na kashin kansa da ya fi ya je ya ziyarci gonarsa, koda kuwa ba shi da wani muhimmin aiki a gonar. Kuma wani abin mamaki duk bacin ran dake addaba ta da zarar na isa gonata, sai kaji komai ya zama tarihi. Ku ba kun tsaya ba, wai ku 'yan boko sai zuwa Office, da yaki da biro da takardu, kun manta da cewa noman dai shi ne gatanmu. Mu bar dai wannan zance, Malam Habu menene al'amarin da kake son mu tattauna akansa?

Malam Jatau ba komai ya tayar min da hankali ba, sai wata magana da shugaban Jamhuriyar nan, wato shugaba Mai Bakar Malafa ya yi game da maganar kayyade iyali, kuma ka san fa wannan ba karamin laifi ba ne addininmu, kai har ma a addinin nasu, babban laifi ne, aikata wannan kuduri na shugaban.

To ban da abinka Malam ko nace Dakta Habu menene zai daga maka hankali akan hakan, har ka shiga irin wannan tunani?

Ba komai ya daga min hankali ba, sai gaskata maganar Mai Malafar da nayi, saboda kuwa duk abinda ya furta cewar zai yi to fa sai ya yi, ko da kuwa ana muzuru ana shaho, ma'ana idan shi kadai ya yanke hukuncin zai yi abu kaza, ko duk kasar nan za su nuna rashin goyon bayansu, bai dame shi, kai ko jama'ar kasar za su shiga wani hali, an yi irin haka da shi ba sau daya ko sau biyu ba, idan za ka tuna janye tallafin albarkatun man fetur da yayi, ko karin kudin wutar lantarki daya yi, duk 'yan kasa sun nuna kin amincewarsu, majalissun kasa ma duk biyun basu amince ba, kungiyoyin da bana gwamnati ba har zanga - zanga cin amincewa suka yi tayi amma duk a banza, yayi kunnen uwar shegu sai da ya aiwatar da kudirinsa.

Maganarka tana kan hanya domin a baya bayan nan ma, sai daya canja sunan Jami'ar Legas, duk ba tare da yardar kowa ba, to amma idan haka ne ai akwai wani alkawari daya dauka amma ya kasa cika shi.

Wannan wane alkawari ne kuwa, amma dai zai amfani talakawa ko?

Sosai ma kuwa, alkawarin da yayi na kawo karshen kungiyar Boko Haram a watan June, ga shi har mun yi bankwana da watan mun shigo watan July, kai wani abin mamaki ma, kungiyar kamar karfi ta kara a cikin watan June din, maimako a murkushe ta kamar yadda shugaban ya dauki alwashi.

Hahahahaha! Malam Jatau har ka bani wata budurwar dariya, ai daman shi shugaba Mai Malafa a yadda masu bibiyar al'amuran yau da kullum da ya shafi kasar nan suka bayyana shi baya nuna bajintarsa da matsawarsa, a komai sai inda talakawan kasar nan za su shiga wani mawuyacin hali, kuma idan kayi nazari za ka gane wannan batu haka yake babu ja ko kadan.

To a karshe menene matsayinka a game da kudirin kayyade haihuwar da kace yana yunkurin yi?

To daman ai Malam Jatau neman da nake yi ma kenan har kwana uku don naji ra'ayinka da shawararka akan kudirin?

Malam Habu da ma baka wahalar da kanka wurin jigilar nema na ba, domin kuwa ni tuni na dade da daina tofa albarkacin bakina a komai daya danganci kasar nan, saboda kuwa sai mutum ya je ya sanyawa kansa hawan jini ya tafi ba tare da lokacin tafiyar tasa ya yi ba. Kai bari ma na karashe ma maganar tun ruwan farko na baiwa Malam Mati makocina rediyo na kyauta, hankalina kacokan yanzu ya koma kan gonata, fatana Allah ya ba mu damuna mai albarka. Ga ga tafiya ta, sai an jima!

Malam Jatau! Malam Jatau!! Malam Jatau!!! Malam Jatau...... (Zancen zuci) Kai lalle Malam Jatau ya watsar da al'amuran Nijeriya sai ka ce ba shi ne kullum ba shi da zancen daya fi na Nijeriyar ba. Kai anya nima kuwa ba tattarawa zanyi na hakura da bata lokaci akan tunanin gyaruwar NIJERIYAr ba? To idan kuma muka daina yunkurin gyaruwar kasarmu, wasu za su zo daga wata kasar ne su gyara mana kasar tamu sannan su koma kasarsu? Tunda nake karanta tarihin kasashen da suka ci gaba, ban taba karanta tarihin kasar da baki suka zo suka daidaita kasar bayan ta rikice ba, ko suka kawo mata ci gaba a lokacin da take sahun koma baya. Amma dai zanyi tunani akai kafin na yanke hukuncin karshe.

To 'yan uwana Maza da Mata 'yan DANDALI sai mu taru mu taya Malam Habu yin tunaninsa na karshe kafin ya yanke hukunci ci gaba ko daina tunani akan makomar kasarsa anan gaba.

Shin ya kamata ya ci gaba da tunanin gyaruwar Nijeriyar ko ya hakura ya fuskanci harkokin da ke gabansa?

Tuesday, June 26, 2012

Tashin Hankali: Tashin Bama - Bamai A Unguwarmu


Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un!!!

Tashin hankali ba a sa maka rana, yau kam unguwarmu Goron Dutse Dala/Gwale Kano mun shiga tashin hankalin da ba mu taba samun kanmu a ciki ba, abin da muke jin labari a da a kasashen duniya da suke fama da yaki, sai gashi ana tafe ana tafe ya zo kasarmu a yankinmu na Arewa, to sai kuma ga shi a yau ya zo mana har gida, daman masu iya magana na cewa idan gemun dan uwanka ya kama ta wuta sai kayi kokarin sanyawa naka ruwa, tabbas wannan magana haka take a yammacin yau sai da aka shafe sama da awa daya rabi ana rugugin wata da tashin bama - bamai a unguwar tamu, wanda wasu 'yan bindiga suka fara daga bisani kuma sai ga jami'an tsaro da tankokin yaki suma suka fara nasu lugudan wutar, wanda hakan ya sanya hankalinmu ya yi bala'in tashi domin ji muke yi kamar a cikin dakunanmu da tunda aka fara tashin hankalin muka shiga muka kukkule, muna jiran yadda Allah zai yi damu.

Haka za gaji karar tashin bam kamar dakin da kake ciki zai ruguzo a kanka, kafin wani dan lokaci tuni titi da layukan unguwarmu sun zama kamar ba a taba halittar bil'adama ba. Sai dai wani abin haushi da na rasa yadda zan yi sai kawai da dakko radio na kunna domin ko zan ji halin da muke ci, saboda kuwa a lokacin da za a yi min tambayar cewa Bashir a wane hali kake a yanzu? Wallahi amsar da zan bada ita ce Allah a'alamu, saboda kuwa ba zan iya cewa ga halin da nake ba. Amma maimakon na ji gidajen radion dake cikin fadin kwaryar jihar Kano sun sako wani abu daya danganci halin tashin hankalin da muke ciki, sai na ji akasin haka, kowace tasha na murdo sai kawai na ji ana ta shan kida, kamar ma ba su san mai ke faruwa a jihar ba, abin ya bani haushi na kashe radion na dakko wayata na budo shafin Facebook nan na dan ji sanyi a zuciyata, domin kuwa sai naga kowa ba a abinda yake rubutawa sai batun halin da muke ciki, ga kuma 'yan uwa sai addu'a suke ta taya mu, duk da dai na kasa cewa komai a Facebook din amma na dade ina ta kallon abubuwan da jama'a ke bayyanawa game da mu, gami da saurin cewa "amin" idan naga wani ya taya mu da addu'a akan halin da muke ciki.

To dai a halin yanzu komai ya lafa, babu karar harbe - harbe kamar da zu, sai dai dan kadan da za ka dan ji nan da can, sai dai sanarwa da muka samu cewa da zarar munyi sallar Isha'i to kowa ya koma cikin gida ya kwanta, domin kuwa tuni an jibge manyan tankokin yaki da tarun jami'an tsaro a wasu sassa na unguwar tamu. Ni kuwa daman da yake wannan shi ne karon farko da na taba samun kai na a cikin irin wannan hali tun da aka fara abin na shiga gida, sallar Magriba ba a cikin gidan nayi, ba don tsoron mutuwa ba sai don tunanin wahala, saboda kuwa mutuwa dai daya ce kuma na san zan mutu koda ina so ko ba na so, da lokacin ya yi zan koma ga Mahaliccina Allah.

A karshe ba abin da zance sai godiya ga 'yan uwa da suka taya mu da addu'a, musamman wadanda suka yi ta kirana a waya suna tambayar lafiyata, Allah ya saka da alheri, ya kuma bar zumunci.

Ya Allah ka kawo mana karshen wannan tashin hankali a kasarmu. Ka bayyana dukkan masu hannu a ciki, koda kuwa suke rike da madafan ikon kasar nan. Na gode!

Wednesday, June 20, 2012

Addu'a: Hanyar Kawo Karshen Halin Da Muke Ciki A Kasar Nan


Aminci a gare ku ya ku 'yan uwana Musulmai maza da mata, yara da manya, kasarmu Nijeriya na cikin wani mummunan hali, halin da idan ya ci gaba da faruwa to nan gaba komai na iya faruwa.

Wani abin bakin ciki kuma abin da ya fi tayar min da hankali shi ne tun lokacin da wannan mummunan abu ya fara faruwa a shekarar 2009, 'yan uwanmu Musulmai Hausa/Fulani su abin ya fi ritsawa da su, amma kullum kuma mu ake zagi da zargar cewa mu muke haifar da komai, hakan ta sa kullum ake kara tsanarmu, ana zagi da aibanta addininmu.

To mu dai kowa ya sani ba mu da takobi, ba mu AK47 balle kuma jirgin yaki, amma dai duk da haka addininmu ya sanar da mu muna da makaman yakin da ya fi duk wadannan makamai, saboda haka lokaci yayi da zamu maida hankalinmu kan makamanmu, mu dakko shi mu fara amfani da shi, haka ne kadai zai kawo mana daidaituwar wadannan al'amura.

Wannan makami namu ba boyayye ba ne, a wurinmu hasalima, dukkan mu mun iya fafata yaki da shi, kuma mu samu nasara akan abokan gabarmu, ba tare da mun ji rauni ko kwarzane ba, sai dai kawai mantuwa da koyaushe take hana mu fafata yakin da shi.

ADDU'A ita ce makamin namu, wadda kuma ya kamata a tsakaninmu mu dauki wani adadi daga cikin wadanda Al Qur'ani mai girma ya koya mana har sai mun yi nasara, saboda haka mu kudure a cikin zuciyoyinmu daga yanzu kullum muke karanta "HASBUNALLAHU WA NI'IMAL WAKIL" sau miliyan daya (1,000,000.00) da zummar Allah (SWT) ya taimake mu, ya kawo mana karshen wannan hali na rashin tsaron da muke ciki, sannan Allah ya tona asirin duk wanda suke shirya wannan al'amari, koda kuwa Musulmai ne ko kirista Allah ya wargatsa shirin su.

Idan kowanne daga cikin mu zai karanta adadin 1000 a kullum, to tabbas za mu haura yawan adadin miliyan dari ma. 'Yan uwa mu taimaka mu aikawa sauran 'yan uwanmu maza da mata wannan sako, sannan mu sanarwa yara kanana su ta karantawa. Allah ya taimake mu ya amsa addu'o'inmu.

Monday, June 18, 2012

Shin Gaskiya Ne Shahararriyar Jarumar Fim Din Nan Nafisat Abdullahi Ta Rasu?


Tambaya: "Shin gaskiya ne shaharriyar jarumar shirin fina-finan Hausan nan Nafisat Abdullahi ta rasu?" Wannan tambaya ko nace jita - jita, ta dade tana zagayawa a tsakanin al'ummar kasar nan musamman masu sha'awar finafinan Hausa. Hakan kuwa ya samo asali ne tun bayan hadarin da Nafisan daya rutsa da ita da abokin sana'arta Adam A. Zango.

Shahararriyar 'yar wasan kwaikwayon, ta kawo karshe wannan jita - jita da bakinta a wata tattaunawa da tayi da wakilin jaridar RARIYA, inda take cewa "Ina nan da raina a daina cewa na mutu".

Domin karanta cikakken labarin sai a nemi jaridar RARIYA ta ranar Juma'an nan wadda ke kasuwa a halin yanzu, kuma za a iya samun jaridar a dukkan wuraren saida jaridu dake sassan kasar nan.

Sunday, June 17, 2012

Wa Ke Da Alhakin Tashin Bama - Bamai A Kaduna?


Yau mutanen arewacin Kaduna sun ga tashin hankali, sakamakon tashin wasu bama bamai a wasu majami'u a birnin Zaria da cikin garin Kaduna, wanda hakan ya haifar da asarar rayuka da dokiyoyi masu yawa, dalilin faruwar wannan al'amari ya sa wasu matasan kiristoci sanya shingaye akan titunan da zasu dawo da matafiya Kaduna daga Abuja, da suna daukar fansa, saboda a zargin su Musulmai ne suke da alhakin faruwar al'amarin. Duk kuwa da cewa ba sau daya ko sau biyu ba ana kama kirista da bam na kokarin sanyawa a coci.

Bayan isar wannan mummunan labari cikin kunnuwa na, ba komai zuciyata ta fara tuno min da shi ba, sai wata magana da shugaba Goodluck Jonathan ya bayyana a kwanakin baya da yake tabbatarwa 'yan Nijeriya cewa gwamnatinsa za ta kawo karshe da murkushe kungiyar nan ta Boko Haram, wadda ake zargi da irin wannan aika aika a sassan kasar nan daban daban, a watan June da muke ciki a yanzu.

Ina tunanin ba komai ya sa zuciyata ta yi saurin tuno min da wannan magana ba sai don sanin ba kowa za a zarga da yin wannan aika aika ba sai kungiyar ta Boko Haram, ba don komai ba, sai don kaurin sunan da tayi akan hakan kamar yadda na fada a baya.

To ana cikin haka, sai wani tunanin ya kara kunnuwa cikin zuciyar tawa hade da tambaya. Shin tunda Boko Haram ta zo karshe a wannan wata, kamar yadda shugaba Jonathan ya dau alwashi, kuma kaso mafi rinjaye na al'ummar kasar nan suka gastata maganar tasa, to wa kuma yake da alhakin kai hare - haren bama baman yau din a Kaduna?

Ya Allah ka kawo mana zaman lafiya a kasarmu.

Saturday, June 16, 2012

Ta Tabba Faruk Lawan Ya Karbi Cin Hanci: Wane Hukunci Ya Cancanci A Yanke Masa?


Wannan takaddama tayi daidai da abinda bahaushe ke cewa "Mai Dokar Bacci Ya Buge Da Gyangyadi" ba komai yasa na bude wannan maganar ba, sai game da takaddamar da ke kai kawo a kasar nan ta Hon. Faruk Lawan shugaban kwamitin bankado badakalar tallafin man fetur, wanda ya tsaya tsayin daka, ya kuma jajirce ba tare da jin kunya ko nuna tsoro ba, yayin tafiyar da aikin da aka dora masa a kwamitin nasa, ya gudanar da aikin nasa ba tare da nuna abokan taka ba, duk irin barazanar da shi da sauran 'yan kwamitin nasa suka sha, hakan bai hana su gudanar da ingantaccen bincike ba akan duk wani dake da hannu a cikin badakalar ta tallafin man fetur din ba. Kai na dai takaice jawabina duk wannan kwanci tashin da Faruku da sauran abokanan aikinsa suka sha a karshe sai da suka bayyana sunan duk wani da suka samu da hannun cikin badakalar, ba tare da ware 'yan lele ko abokanai ba. Wannan sakamakon bincike da kwamitin suka bayyana ba karamin burge 'yan Nijeriya suka yi ba, kuma ya karawa jama'ar kasar nan kwarin gwiwa, da jinjina a gare su domin ba wanda ya taba tunanin cewa za a samu gwarzaye marasa tsoron da za su iya jagoranta wannan jan aiki har su kai ga nasara.

Sai dai kuma bayan wasu 'yan satuttuka da bayyanar sakamakon duk kafin a kai ga hukunta wadanda aka gano da laifuka, sai ga reshe na neman juyewa da mujiya, domin kuwa sai ga sanarwar zargin jagoran kwamitin kamo masu laifi ana zarginsa da laifi makamancin irin wanda ya jagoranci bankadowa. A takaice shi ma dai a karshe an bankado ta sa badakalar da ake zarginsa da karbar cin hancin zunzurutun kudi har dalar Amurka $6000,000, da wani kamfanin hada hadar man fetur wanda ba a tantance sunansa ba ya ba shi, kuma a karshe zargin ya tabbata gaskiya sakamakon wasu shaidu da aka gabatar ciki har da faifai hoto mai motsi wato Video, wanda har hakan ya jawo sauke jagoran bankado masu badakala ya bayyana da bakinsa cewa ya karbi na goron, amma domin ya zame masa wukar gindi wurin gurfanar da wadanda suka yi masa tayin na goron a gaban hukumar yaki da cin hanci da yiwa dukiyar kasa zagon kasa wato EFCC. Daga karshe dai wannan tabargaza da jagoran ya tafka ta jawo sauke shi daga dukkan wasu mukamai da yake jagoranta a majalisar ta wakilai.

Baya ga haka, su kuma jami'an hukumar 'yan sanda suka garzayo don gudanar da aikinsu akan Faruku, wato dai tuni suka yi awon gaba da shi don ci gaba da binciken kwakwaf, har su gano gaskiyar lamarin.

To abin tambaya anan shi ne, shin idan masu binciken kwakwaf sun sake gano Faruku da laifi dumu dumu, wane irin hukunci ya cancanci a yanke masa don ya zama darasi ga masu irin halayyarsa?

Na san ni da sauran masu karatu ba za a rasa tarun amsoshin wannan tambaya a cikin kwakwalenmu ba, to amma kafin azo kan amsa tambayar ina labarin baragurbin da kwamitin da Faruku ya jagoranci bankado almundahanar da suka tafka akan tallafin man fetur? Shin su tunda an tabbatar da laifukansu an yanke musu hukuncin da yayi daidai da laifinsu? Idan ba a yanke ba har yanzu, to shin mai ake jira?

A karshe zan bawa hukumomin shari'a da abin ya shafa shawarar ya kamata suyi amfani da maganar da Janar Muhammad Buhari ya fada akan masu hannun a badakalar tallafin man fetur din, inda yake cewa "Da ni ne shugaban kasa, da zan yankewa duk masu hannun a cikin badakalar hukuncin kisa, ko hukuncin dauri a gidan yari" tabbas Janar ya fadi gaskiya kuma bana tunani akwai wani hukunci da za a yanke musu da ya fi hakan dacewa. Kuma da tun farko ana daukar irin hukuncin akan duk wani da aka samu da hannun dumu dumu akan cin hanci da karbar rashawa, da tuni sai an share gumi wurin binciko mutum daya da za a samu da irin makamancin laifi, saboda kuwa duk kasashen da suka yi kaurin suna wurin cin hancin irin hukunci ake amfani da shi ake kawo karshe mummunan aikin.

Thursday, June 14, 2012

Majalisar Wakilai Ta Kira Zaman Gaggawa


Majalisar wakilai ta kasa za ta gudanar da wani zama na ba zata a gobe Juma'a. A wata sanarwa da akawun majalisar, M. A. Sani-Omolori ya rabawa manema labari a daren jiya, ya bukaci daukacin 'yan Majalisar wakilan da su halarci zaman majalisar da za a fara da misalin karfe 10 na safe.

Ana kyautata zato dai zargin badakalar karbar cin hancin da ake zargin Hon. Faruk Lawal ya yi shi ne batun da zai mamaye tattaunawar da wakilan za su yi.

Wani hamshakin dan kasuwa mai safarar mai, Femi Otedola ne yayi zargin cewa, dan majalisar, Faruk Lawan ya karbi cin hanci dangane da binciken kudaden tallafin da majalisar tayi.

Koda a baya dai majalisar dokokin Najeriya ta sha aukawa cikin badakalar cin hanci da rashawa.

Daga BBCHausa.com

Wednesday, June 13, 2012

Sanusi Lamido Sanusi Ya Koma Bakin Aiki Sanye Da Kayan Sarauta


Gwamnan babban bankin kasa CBN Malam Sanusi Lamido Sanusi wanda a ranar Juma'a da ta gabata Mai martaba Sarkin Kano Alhaji Dr. Ado Bayero ya nada shi a matsayin Dan Majen Kano ya koma bakin aiki birnin tarayya Abuja cikin kayan sarauta, wato sanye da babbar riga da alkyabba gami da rawani mai kunnuwa biyu sanye a kansa, ga kuma sandar ban girma rike a hannunsa na dama.

Da shigarsa wurin aikin nasa sauran abokan aikinsa da suke karkashinsa sun zo sun karbi gaisuwa irin yadda ake yiwa sarakuna a yankin kasar Hausa.

Muna kara yiwa Malam Sanusi Lamido Sanusi addu'ar Allah ya taya shi rikon wannan sarauta, Allah kuma ya sa wannan sarauta mataki ce a gare shi.

Darasin Da Nijeriya Za Ta Koya Daga Kasar Brazil Ta Fuskar Bunkasar Noma

Za mu iya daukar darasi daga kasashe irin su Brazil, Indonisiya da Malesiya. Duk da cewa, wadannan kasashe su na samar da mai, arzikin noma ne daya bunkasa su da al’ummarsu bakidaya.

Amurka ta siffanta Brazil a matsayin kasa mafi karfin arzikin noma a duniya. A bangarori da dama Brazil ta na kamanceceniya da Nijeriya. Kowacce ta na da yawan al’umma da fadin kasa. Brazil ta na da yawan mutanen da ya kai miliyan 190, yayin da Nijeriya ke da miliyan 167. Dukkanninsu su na da mai da kuma kasar noma, amma shugabanci ne ya bambanta kasashen biyu.

Llokacin mulkin kama-karya a Brazil an yi sakaci da aikin noma, amma tun lokacin da mulkin dimokuradiyya ya dawo kasar, aikin noma, wanda ya ke bai wa mafi yawa aikin yi sai ya sami bunkasa. Cikakkiyar hikima ita ce dimukradiyya ta bayar da yanayi na sauyi (ban da a Nijeriya), domin komai na dimokurad-iyya ya ta’allaka ne ga mutane. An bai wa noma muhimmanci a Brazil, dalilin da ya sa ya kenan kashi daya bisa uku na masu aikin yi a kasa shi ke ba su aiki.

Sakamakon ba wai ya tsaya ne kawai a kan cewa Brazil ta dogara da kanta ta fuskar ciyar da kai ba ne, a’a, ta na cikin kasashe ne ma mafi fitar da kayan amfanin gona. Brazil ta fi kowacce kasa fitar da rake, kuma ta na daya daga cikin mafi fitar da koko, waken soya da lemo. Kiwo ma ya na da fadi a kasar. Kayan noma su ne kashi 35 cikin 100 na abinda kasar ke fitarwa waje. Brazil ce mafi fitar da jan nama a duniya, rake, kofi, waken soya da kaji.

Arzikin noma na Brazil ya haura na kowacce kasa ne saboda aniyar shugabanninta; sun kafa manyan gidajen gona, yayin da kuma su ka karfafa kananan gonaki, bincike, bude kasuwanci a faifai da kuma amfani da dabarun noma na zamani. Gonakin Brazil su na da girman da ya fi yawancin gonakin Amurka, kuma a na kallon manomansu a mataki na duniya, ba wai cikin kasarsu kadai ba. Babu wani dalili da zai hana yin amfani da salon ’yan Brazil a Nijeriya. Dogaron da a yanzu mu ke yi da kananan manomanmu ba zai kai mu ko’ina ba. Za mu iya aikata abinda ya fi haka. Ba Ina cewa, gwamnatocin jihohi ko ta tarayya su mallaki gidajen mar da gona ba, amma dai su samar da filayen noma domin yin abinda ya ke a can din. Karfin gwiwa ne kadai zai iya samar da hakan. Ya kamata gwamnatoci su sayo iri masu kyau, kuma a samar da matsaya a kasuwannin duniya.

Ya kamata gwamnatin tarayya ta shigo ciki ta hanyar babban bankin Nijeriya, domin samar da rance da kuma noman kansa. Bambancin shi ne, Brazil ta na da filin noma hekta miliyan 76.7, yayin da a ke da fadin kasa na miliyan 170. Don haka ba abin mamaki ba ne don shanun Brazil sun kai miliyan 190, yayin da shanun Nijeriya ba su wuce miliyan 10 zuwa 15 ba. Kai kamar kowane abu ma dai, Nijeriya ba ta da kididdigar yawansu.

Brazil ta na fiye da hekta miliyan 23 da a ke girbe waken soya kadai. Masara ta na da hekta miliyan 12, rake na da miliyan 7, sannan shinkafa na da miliyan 2.5.

Malesiya ma wata abar misali ce. Ta na fiye da hekta miliyan hudu na noman kwakwa. A bara kadai ta sami Dala biliyan biyu a fitar da kwakwa waje. Saboda hazaka da zakakuranci, Indonisiya ta zo ta sha kan Malesiya wajen fitar da kwakwa. Wadannan kasashen fa su na da mai, amma kawai su na da shugabanni na nagri ne fiye da Nijeriya. Akwai lokacin da Nijeriya ce kasa mafi fitar da gyada waje a duniya da manja, roba da koko. Kuma a lokacin mu na cikin kasashen da ke kan gaba wajen fitar da auduga, karo, fata, kashu da sauran kayan amfanin gona.

Ya kamata gwamnatin tarayya, jihohi da kananan hukumomi su fara tseren noman a junansu. Ya kamata gwamnatocin jihohi, musamman ma na Arewa tunda sun fi fadin kasar noma, su samar da akalla hekta 500,000 a kowanne yankin mazabar sanata (jihohi da dama za su iya samar da fiye da hakan), sannan su shigar da matasan da ke barazana ga tsaro cikin tsarin aikin yi a gidajen gona. Ya kamata a dawo tsarin wa’adin filaye da hukumar nan ta NALDA (Nigerian Agricultural Land Development Agency), wacce Janar Babangida ya kafa, amma saboda wawanci gwamnatocin da su ka gaji tasa ta rushe.

Ya kamata shugaban kasa ya fara aiki na hakika kan sha’anin noma, ya daina damun mu da batun biredin rogo haka nan.

Tuesday, June 12, 2012

Gidauniyar Rochas Okorocha Za Ta Gina Jami'ar Kyauta A Kasar Nan


Gidauniyar ci gaban ilmi da samar da shi kyauta ga masu karamin karfi ta Rochas Okorocha, ta bayyana kudirinta na gina Jami'ar farko a kasar nan da za ta ke bayar da ilmi kyauta ga masu karamin karfi.

Gidauniyar a halin yanzu na da mallakin makarantun sakandare har guda biyar a fadin kasar nan, wanda duk ake bawa masu karamin karfi ilmi a kyauta a cikin su, makarantun akwai su a bangarorin kasar nan daban daban, akwai a Ogboko jihar Imo, Owerri, Kano, Ibadan da kuma Jos.

Lalle Rochas ya jiri tuta a fadin tarayyar kasar nan, ya kuma zama abin kwatance, da za a samu masu tausayin talakawa kamar sa guda goma a cikin masu mulki da masu arzikin da ke dunkule a kasar nan da ilmi bai gagari 'yan talakawa ba.

Wannan gidauniya ta dade tana tuttula ilmi ga 'yayan da iyayen su ba za su iya daukar dawainiyar biyan kudade karatun 'yayansu ba, kuma wani abin sha'awa tun kafin ya samu mulkin jihar Imo da yake kai a halin yanzu gidauniya ta ke, kuma take yin aikin alkhairai daban daban da suka shafi fannin samar da ilmin zamani.

Sunday, June 10, 2012

Ana Zargin Faruk Lawan Da Hannun Dumu - Dumu Wurin Karbar Cin Hancin $600,000


Ana zargin shugaban kwamitin bincike kan badakalar tallafin man fetur Hon. Faruk Lawan da hannu dumu - dumu wurin karbar cin hancin zunzutun kudi dala mai dukan dala har dalar Amurka $600,000 daga wurin wani kamfanin man fetur da baida suna.

Hon. Faruk an ce da farko ya musanta zargin sai bayan da yaga takardu tsirara dauke da bayanin da ake zarginsa a kai. Tuni majalisar wakilai ta gayyace daya garzaya gabanta domin kare kansa daga wannan zargi.

Rahotonni sun nuna cewa ita ma dai hukumar nan mai yaki da yiwa arzikin kasa zagon kasa wato EEFC ta shirya tsaf domin gayyato Faruku don yi mata bayanin dalla dalla yadda akayi hakan ta faru.

Idan har wannan zargi ya tabbata gaskiya ne Faruk Lawan ya amshi wannan makudan kudade, lalle mu talakawan Nijeriya sai mu fara ja da baya, da rage tunanin cewa nan gaba kasar nan za ta zama daidai, da kuma daina murna da farin ciki duk lokacin da muka samu labarin anyi kokari kawar da wani laifi a kasar nan.

Ba komai ya sani fadin haka ba, sai tunowa da nayi lokacin da Faruk Lawan ya bayyana rahotonsa karo na farko, game da irin yadda kwamitinsa yayi aiki tukuru ba tare ba rana sai aka gano yadda wasu 'yan tsirara suka rinka wadaka da rabebeniya da dukiyar al'ummar kasar nan, da yadda Faruk ya rinka daukar alwashin ba zasu rufawa kowa suka samu da laifi asiri ba. Hakan tasa talakawa suka fara yiwa juna barka da fara tunanin lalle kakarsu ta fara yanke saka, sai kuma gashi kwatsam ana zargin mai dokar bacci da bugewa da gyangyadi. Allah ya kyauta.