Tuesday, August 30, 2011

Barka Da Sallah Daga Bashir Ahmad

A yau ne (30 August 2011) daukakin al'ummar Musulman Nigeria suka bi sahun takwarorinsu Musulmai dake sassan duniya daban - daban wurin gabatar da bikin Sallar Idi karama, bayan sauke azumin watan Ramadan.

Allah mai iko! Kamar ko yaushe an samu wasu 'yan tsirarun mutane da su kayi Sallar Idin su tun jiya, saboda sabanin ra'ayi. Abin mamaki wasu mutanen kuma sai gobe 31 August 2011 zasu gabatar da Sallar Idin tasu. Wannan ba shine farko ba, kusan kowane lokacin daukar Azumi da sauke shi hakan tana faruwa, saboda banbancin akida ko kuma rashin ganin wata bai dayawa, ko kuma wasu idan basu ga watan da idonsu ba basa yarda su dauki Azumin ko sauke shi. Fatanmu dai Allah ya kawo mana hadin kai a addininmu na Musulunci, wadda zai kawo samuwar magana da murya daya. Amin!

A karshe zanyi amfani da wannan dama na mika sakon taya murna da barka da shan ruwa ga ilahirin 'yayan kungiyoyin Tsanyarar Alheri, Muryar Talaka, Zauren Shawara Facebook, Gizago Club, Dandalin Siyaya, Nigerian Youth Forum, da sauran kungiyoyin matasa da suka sadaukar da kawunansu wurin fafutukar ganin cigaban kasarmu abar alfarinmu Nigeria.

Duk da tuni na mika wannan gaisuwa tunda da sanyin safiya amma zankara mika wannan gaisuwa a yanzu saboda muhimmancinta ga dukkan abokanaina da nake zaune tare dasu, a gida da makaranta, sannan ga daukakin abokaina dake shafukan sada zumunta na yanar gizo musamman na shafukan Facebook, Twitter, 2go. Bazan taba mantawa daku ba masu ziyartar matattarar tunani wato DANDALIN BASHIR AHMAD. Nagode! Allah ya saka muku da alheri abokaina, ko yaushe addu'ata a gare ku itace Allah ya biya muku bukatunku na Alheri.

Allah ya karbi ibadunmu na watan Ramadan, Allah yasa muna cikin bayin da aka 'yanta akayi musu gafara. Allah ya maimaita mana. BARKA DA SALLAH!

Bashir Ahmad
bashirgy@yahoo.com
+2348032493020

Tuesday, August 23, 2011

Abin mamaki ko abin dariya? Sa'insa tsakanin Obasanjo da Babangida

Chief Olusegun Obasanjo, da General Ibrahim Badamasi Babangida tsofaffin shugabannin kasar nan ne, kuma suna daga cikin dattawan kasar nan da ake ganin girmansu saboda irin mukaman da suka rike da kuma gwagwarmayar da suka sha game da yakunkunan basasar kasar nan, da kuma kokarinsu na ganin kasar ta zauna a matsayin tarayya guda mai cikakken iko.

Abin mamaki ko nace abin dariya duk da dattijantaka irin ta wannan bayin Allah wadanda duk sun haura shekaru 60 a duniya, amma bai hana barkewar zazzafar sa'insa a tsakaninsu ba, ko sun manta da cewa 'yayansu dasu zasuyi koyi oho.

Obasanjo ya bayyana Babangida a matsayin wawa a shekaru 70, kuma bai amfanarwa kasar nan komai ba a shekaru 8 da yayi na mulkin soja. Dalilinsa kuwa, yace yayi amfani da izu na 26 aya ta 4 da ta 5 na cikin littafin Karin Magana (Proverbs).

Shi ma Babangida ya bayyana mulkin da Obasanjo yayi tsakanin 1999 zuwa 2007 ba za'a kira da komai ba sai bata lokaci domin kuwa bai tsinanawa kasar nan komai ba sai ci baya. Ya kuma bayyana Obasanjon a matsayin mai karancin tunani da hangen nesa.

Nan shi ma Obasanjon ya cigaba da cewa IBB yana da damar gina tashoshin wutar lantarki, lokacin da yake kan mulki, saboda irin kudin da kasar ke dasu a lokacin, kamar yadda shi ya gina Jebba dam, da Shiroro dam kuma ya fara shirin gina Egbin wanda Shehu Shagari ya gina a lokacin mulkinsa.

Obasanjo yace "Na gina dam guda biyu saboda muhimmancinsa, kowa yasan wutar lantarki ita ce kashin bayan ci gaban duk wata kasa mai tasowa. Tun lokacin da aka gina tashar Egbin har na dawo mulki a 1999 babu wata tasha wutar lantarkin da aka sake ginawa, kusan shekaru 20 kuma Babangida yayi shekaru 8 a lokacin yana mulki, wannan ba karamin rashin cigaba bane.

Bayyana mulkina na 1999 da 2009 da IBB yayi a matsayin bata lokaci da koma baya, ya kamata ya nemi afuwar fadin hakan. Na karanta inda yake cewa a lokacin mulkinsa ya bada ribar demokradiya, duk da ya nuna nadamarsa, to amma masu iya magana na cewa wawa a shekaru 40, wawa ne har abada. Ni kuma nace nadama a shekaru 70, makararriyar nadama ce, kuma nadama ce ta kabari".

A martanin da Babangida yayi ta bakin mai magana da yawunsa, Prince Kassim Afegbua yace "wannan ba dabi'ar Babangida bace ya shiga irin wannan sa'insa marar ma'ana. Tarihin Obasanjo a bude yake, lokacin da ya roki IBB ya bashi damar kara wa'adin mulkinsa, IBB ba wawa bane sannan. Lokacin da aka sake shi daga kurkuku, aka yi masa wanka aka bashi kayan alfarma ya saka a karshe ya zama shugaban kasa, IBB ba wawa bane sannan, sai yanzu da yakai kololuwar tunaninsa, zai cirewa IBB zani a kasuwa, ya kira shi da wawa"

Anan dai ya kamata talakawan Nigeria wadanda suka ga mulkin wannan dattijai guda biyu suyi alkalancin wanene wawa, Babangida ko shi kansa Obasanjon?

A matsayina na wanda naga mulkin Obasanjo na 1999 zuwa 2007, idan nine alkali zan kira Obasanjo ne wawan ba IBB ba, idan nayi duba da irin mulkin kama karyar da ya shinfida a kasar nan. Yayi ikirarin ya gina tashoshin bada wutar lantarki guda biyu a mulkinsa na soja, amma kuma ya zo ya lalata wutar kasar nan a mulkinsa na farar hula, shin wannan ba wawanci bane? Ya zo ya samu man fetur a kasa da naira 30 lita daya, ya maida shi sama da naira 60, shin wannan ba wawanci bane? Ya zo ya samu kasar nan da tsaron da kasashen waje ma na tsoronsa, amma ya kori manyan sojoji, ya lalata tsaron, idan su al'ummar kasar ma ke masa barazana, wannan ba wawanci bane?

Amma kuma kai tsaye ba zance Obasanjo wawa ba, saboda ko kadan bansan yadda shi IBB ya gudanar da nasa kalar mulkin ba ko nace nasa kalar wawancin. A wannan sa'insa aikinmu kadai kallo, inda akayi abin dariya, muyi dariya. Inda akayi abin mamaki, muyi mamaki. Inda akayi abin haushi muyi Allah wadai.

A karshe, fatanmu Allah ya kawowa kasarmu dauki. Ya fatattaki duk wasu azzalumai, Ya canja mana adalai a madadinsu.

Bashir Ahmad
Bashirgy@yahoo.com
08032493020, 08050600160

Sunday, August 21, 2011

Rebel entered Tripoli and Gaddafi's son has been captured by forces

Rebel fighters streamed into
Tripoli as Muammar Gaddafi's
forces collapsed and crowds
took to the streets to celebrate,
tearing down posters of the
Libyan leader.

A convoy of rebels entered a
western neighborhood of the
city, firing their weapons into
the air. Rebels said the whole of
the city was under their control
except Gaddafi's Bab Al-Aziziya-
Jazeera stronghold, according to
al-Jazeera Television.

Gaddafi made two audio
addresses over state television
calling on Libyans to fight off the
rebels.

"I am afraid if we don't act, they
will burn Tripoli," he said. "There
will be no more water, food,
electricity or freedom."

Gaddafi, a colorful and often
brutal autocrat who has ruled
Libya for over 40 years, said he
was breaking out weapons
stores to arm the population. His
spokesman, Moussa Ibrahim,
predicted a violent reckoning by
the rebels.

"A massacre will be committed
inside Tripoli if one side wins
now, because the rebels have
come with such hatred, such
vendetta...Even if the leader
leaves or steps down now, there
will be a massacre."

NATO, which has backed the
rebels with a bombing campaign,
said the transition of power in
Libya must be peaceful.
After a six-month civil war, the
fall of Tripoli came quickly, with
a carefully orchestrated uprising
launched on Saturday night to
coincide with the advance of
rebel troops on three fronts.

Fighting broke out after the call
to prayer from the minarets of
the mosques.

Rebel National Transitional
Council Coordinator Adel
Dabbechi confirmed that
Gaddafi's younger son Saif Al-
Islam had been captured. His
eldest son Mohammed Al-Gaddafi
had surrendered to rebel forces,
he told Reuters.

Only five months ago Gaddafi's
forces were set to crush the
rebel stronghold of Benghazi, the
leader warning in a television
address that there would be "no
mercy, no pity" for his
opponents. His forces, he said,
would hunt them down "district
to district, street to street, house
to house, room to room."

The United Nations then acted
quickly, clearing the way for
creation of a no-fly zone that
NATO, with a campaign of
bombing, used ultimately to help
drive back Gaddafi's forces.
"It's over. Gaddafi's finished,"
said Saad Djebbar, former legal
adviser to Libyan government.
Al Jazeera television aired images
of people celebrating in central
Tripoli and tearing down posters
of Gaddafi, which had
dominated Libyan cities for
decades.

In Benghazi in the east,
thousands gathered in a city-
center square waving red, black
and green opposition flag as
news filtered through of rebel
advances into Tripoli.

"It's over!" shouted one man as
he dashed out of a building, a
mobile telephone clutched to his
ear. Celebratory gunfire and
explosions rang out over the city
and cars blaring their horns
crowded onto the streets.
Overhead, red tracer bullets
darted into a black sky.

"It does look like it is coming to
an end," said Anthony Skinner,
Middle East analyst, Maplecroft.
"But there are still plenty of
questions. The most important is
exactly what Gaddafi does now.

Does he flee or can he fight?"
"In the slightly longer term, what
happens next? We know there
have been some serious
divisions between the rebel
movement and we don't know
yet if they will be able to form a
cohesive front to run the
country."

Gaddafi, in his second audio
broadcast in 24 hours, dismissed
the rebels as rats.
"I am giving the order to open
the weapons stockpiles," Gaddafi
said. "I call on all Libyans to join
this fight. Those who are afraid,
give your weapons to your
mothers or sisters.

"Go out, I am with you until the
end. I am in Tripoli. We will ...
win."

A Libyan government official
told Reuters that 376 people on
both sides of the conflict were
killed in fighting overnight on
Saturday in Tripoli, with about
1,000 others wounded.

A diplomatic source in Paris,
where the government has
closely backed the rebels, said
underground rebel cells in the
capital had been following
detailed plans drawn up months
ago and had been waiting for a
signal to act.

That signal was "iftar" -- the
moment when Muslims
observing the holy months of
Ramadan break their daily fast.

Via ABC News.

Monday, August 15, 2011

Tsangayar Alheri ta kai ziyara asibitin Kananan Yara

Kungiyar Tsangayar Alheri ta kai ziyara a karon farko tun bayan yiwa kungiyar kwaskwarima daga Sansanin Samari da 'yanmata, kuma shine karon farko data fitar da irin wannan alheri zuwa ga sauran jama'a, ba kamar da da alherin kungiyar ke tsayawa a tsakanin 'yayan kungiyar kadai ba.

Tsangayar Alherin ta kai ziyarar ne zuwa asibitin kananan yara na Hasiya Bayero dake Kofar Kudu a birnin Kanon Dabo. A yayin wannan ziyara kungiyar ta rarraba sabulan wanka da omon wanki ga masu zaman jinya a asibitin.

A jawabin shugaban kungiyar na kasa Abdulqadir Sardauna ya bayyana makasudin kawo wannan ziyara, sannan ya jawo hankalin iyaye da su rinka amfani da hanyoyin rigakafin kariya daga kamuwa da cututtuka musamman gidan sauro mai magani. Shugaban ya kuma bayyana aniyar kungiyar na kara kai wasu ziyarorin zuwa gidan Marayu da gidan Yari (prison) nan bada dadewa ba.

A martanin da wakiliyar ma'aikatan asibitin tayi Dakta Ummu Badaru, ta nuna farin cikinta da kuma godiya ga wannan kungiya, sannan ta bayyana samuwar irin wadannan kungiyoyi a wannan al'umma ba karamin ci gaba bane. Sannan ta kara da cewa suma a matsayinsu na likitoci Musulmai suna da makamanciyar irin wannan kungiya mai suna Islamic Medical Association (ISMA) wadda take taimakawa marassa lafiya masu karamin karfin wadanda basu da yadda zasu yi wurin siyan magunguna. A karshe tayi fatan Tsangayar Alheri zata tafi kafada da kafada da kungiyar tasu ta ISMA.

Bayan kammala ziyarar duba marassa lafiya ne, kai tsaye tawagar Tsangayar Alheri ta nufi wurin da aka tanada dan buda baki (shan ruwa) wanda kungiyar ta shiryawa 'yayanta a karo na biyu bayan wanda akayi a baya ranan 5 Ramadan / 5 August, kuma daya daga cikin 'yayan kungiyar Usman Aminu Alqadiri ya dauki nauyi kamar yadda na bayan ma 'yar kungiyar Shamsiyya Habib ta dauki nauyi. Kuma a ranan 25 Ramadan kungiyar zata gabatar da shan ruwan da ta shirya karo na karshe, wadda shi ma daya daga 'yayan kungiyar Abubakar Abdullahi Kofar Na'isa yayi alkwarin daukar nauyi, fatanmu Allah ya kaimu lokacin da rai da lafiya.

A wurin shan ruwan, an ci an sha anyi hani'an, an kuma yi wasanni da dariya, sannan shugabannin kungiyar na kasa dana reshen jihar Kano suka gabatar da jawabansu, kuma aka bawa wasu daga cikin 'yayan kungiyar suka tofa albarkacin bakinsu. Su ma Malaman kungiyar ba'a barsu a baya ba, sun gabatar da addu'o'i ga kungiya da 'yayanta baki daya. Daga nan aka gabatar da sababbin 'yayan kungiya. A karshe bayan gabatar da Sallan Isha'i kowa ya kama gabansa.

Bashir Ahmad
Acting National Secretary
08032493020, 08050600160.

Saturday, August 13, 2011

Jama'a Ga Mujallar Muryar Arewa

Ina farin cikin gabatar muku da sabuwar mujallar MURYAR AREWA!

Muryar Arewa sabuwar mujalla ce da kamfanin Northern Media Link LTD ke tsarawa da wallafawa wata - wata (monthly) domin samun cikakken labarun da suke faruwa game da yankinmu na Arewa dama kasa baki daya. Babbar manufar Muryar Arewa shine gano matsalolin dake addabar yankin Arewa da kuma kokarin samo hanyoyin magance su, ta hanyar labarai da rahotonni gami da bayar damar fadar ra'ayi, hirarraki da fitattun shugabanni, talakawa, ma'aikata, yan siyasa, malamai, mata da matasa baki daya, duk don samowa Arewa mafita da ci gaba.

Muryar Arewa ta dauki alwashin ganin dukkan jinsunan da ke wannan yanki na Arewa sun hada kansu ba tare da nuna banbanci addini, darika, yare, kabila, sashe ko nuna wani bangaranci ba a tsakaninsu, Muryar Arewa na da burin ganin duk dan Arewa daga kowane bangare ya zauna da kowa lafiya a matsayin uwa daya uba daya.

Ana wallafa Muryar Arewa da harshen Hausa, harshen da kullum yake kara habaka da bunkasa yake a sassan duniya kamar wutar daji.

Kabir Assada shine daraktan gudanarwa kuma babban edita na wannan mujalla, sai kuma kwararrun abokanan aikinsa irinsu: M. K. Muhammad, Ibrahim Basit Ahmad, Sheriff Sidi. Ga kuma wakilai a kusa dukkan jihohin Arewa, sannan kuma ga hazikan marubuta na musamman kamar su Ado Ahmad Gidan Dabino, Yusuf Dingyadi, Binta Spikin, Bashir Ahmad, Nasir Abubakar da sauransu.

Muryar Arewa na da tsari na daban da zai zama abin burgewa da sha'awa ga kowa, inda komai aka tsarashi daki - daki yadda zai kayatar da fahimtar da masu karatu, misali zaka samu rukuni - rukuni a mujallar kamar haka: Labarai, Rahotonni, sharhi, tattaunawa, ra'ayi, taskar al'adu, hirar musamman, tsokaci, kimiya da fasaha, rigar yanci, tsumagiya, nasiha, duniyar finafinan Hausa, adabi, duniyar mata, da sauran shafuka masu ilmintarwa, fadakarwa gami nishadantarwa. Kai abin dai sai wanda ya gani. Sannan kuma akwai shafukan da aka tanada dan talla, don tallar hajar masu karatu.

Kash! Saura kadan na manta da shafin da yafi kowane kayatarwa wato shafin tsakiya, shafin da ya kunshi..... Bari dai na hakura haka, kar na cikaku da surutu, kuma masu iya magana na cewa gani ya kori ji, don haka kayi kokarin mallakar taka don kaima ka samu damar bada labari.

Wannan mujalla an samar da ita don mu Hausawa yan Arewa, saboda haka ya kamata mu bada gudunmawar da zamu iya bayarwa wajen ganin wannan jan aiki da mawallafanta suka dauko an samu gagarumar nasara.

A karshe sako guda daya ko biyu da nake son aikawa ga wannan mujalla shine, ya kamata a samar da filin da masu karatu zasu ke aikowa da gajerun ra'ayoyinsu ta wayar hannu, sannan kuma a samu wani shafi da za'a ke tattaunawa da kungiyoyi don jin manufofinsu da irin ayyukan da suka aiwatar. Hakan zai kara kusanta wannan Mujalla da jama'a na sassa daban - daban. Sannan idan wannan sako nawa ya samu isa cikin nasara, ina fatan wannan mujalla zata bawa kungiyarmu ta TSANGAYAR ALHERI damar bayyana manufofinta ga al'ummar duniya baki daya.

Kafin na ajiye abin rubutun nawa za'a iya samun Muryar Arewa a dukkan wani wurin sai da jaridu da mujallu a kudanci da arewancin kasar nan baki daya, akan kudi kalilan.

Ya Allah ga Mujallar Muryar Arewa don ci gaban Arewa da al'ummar Arewa da ma kasar Nigeria baki daya!

Bashir Ahmad
Bashirgy@yahoo.com
08032493020, 08050600160

Saturday, August 6, 2011

TSANGAYAR ALHERI TA SHIRYAWA YAYANTA SHAN RUWAN AZUMI

Kungiyar Tsangayar Alheri reshen jihar Kano ta shiryawa 'yayanta Shan Ruwan Buda baki ranar 5 Ramadan 1432 wanda daya daga cikin 'yayan kungiyar Shamsiyya Habib ta dauki nauyin shiryawa.

Taron ya samu halartar 'yayan kungiyar da dama ciki har da sabbin yan kungiya, duk da ruwan sama da ya hana wasu zuwa. Wadanda suka halarta sun hada da:
Ali Adamu Jauro
Usman Aminu Alqadiri
Alhaji Nafiu Sharifai
Abubakar A. Kofar Naisa
Auwal M. Danlarabawa
Haruna Adam
Abubakar Suleiman Dan Auta
Muhd Ahmad Idris
Bashir Abdullahi El Bash
Shamsu Ibrahim
Al Jamil Ahmad
Bala Garba Kumbotso
Abdussalam Saidu
Musa Abdullahi DZ
Shamsiyya Habib
Bashir Ahmad
Jummai Shu'aibu
Kamal Muhammad
Balarabe Yusuf Babale Gajida

Aminu Abdu Bakanoma

An tashi daga taron cikin farin ciki da annashiwa, kowa na yiwa kowa fatan alheri.

A karshe Allah ya baiwa wannan baiwar Allah da ta shirya wannan aikin lada, ladan ciyarwa cikin watan azumin Ramadan.

Bashir Ahmad
bashirgy@yahoo.com
08032493020

Wednesday, August 3, 2011

Hamza Al-Mustapha ya fasa kwai a bainar Jama'a

Dogarin tsohon Shugaban kasar Nijeriya Marigayi General Sani Abacha, Major Hamza Al-Mustapha ya fasa kwai game da yadda shugabannin yankin Kudu maso yammacin kasar nan wato yankin Yarabawa, suka karbi cin hancin makudan kudi bayan kashe tsohon babban dan kasuwa kuma dan siyasa M.K.O Abiola.

Al-Mustapha ya baiyana hakan ne a babbar kotun jihar Lagos, yayin da ya baiyana don kare kansa game da zargin kisan Hajiya Kudirat Abiola matar tsohon marigayin, tun a shekarar 1998 ba tare da an yanke masa hukunci ba. Ya kuma kara baiyana cewar tsohon Shugaban kasa General Abdulsalam Abubakar ya sa an tsare shine domin tsoron kar ya baiyana irin badakalar da aka tafka a kisan na Abiola.

Al-Mustapha yace ai baiwa shugabannin Yarabawan sama da dalar Amurka miliyan 200 inda ya shaida cewar ya dade yana son baiyana wannan ta'asa amma saboda tsoron tashin hankali ya hakura sai yanzu da yaga ba mafita sai yayi hakan. A karshe ya shaidawa kotun a zama na gaba zai baiyana fefan bidiyo domin ya zama sheda.

Fatanmu Allah ya taimaki dukkan mai gaskiya akan azzalumai.

Bashir Ahmad
Bashahmad29@yahoo.com
08032493020, 08050600160

Monday, August 1, 2011

Jadawalin Alfijir dana Shan Ruwa (Ramadan 2011)

Wannan lokutan ya shafi jihar Kano ne sai wasu bangarori na Jihohin Jigawa, Katsina da Kaduna kawai, za'a iya samu kari ko ragi a wasu jihohin dake nesa da Kano, kamar Nasarawa +5 Lagos +20 Kebbi +18 Zamfara +17 Yobe -14 Bauchi -4 Taraba -10 Jos -4 Maiduguri -19 da sauransu.

Ga lokutan kamar haka:-

Alfijir === Shan Ruwa
1. 4:58am = 6:52pm
2. 4:58am = 6:51pm
3. 4:58am = 6:51pm
4. 4:58am = 6:51pm
5. 4:59am = 6:50pm
6. 4:59am = 6:50pm
7. 4:59am = 6:50pm
8. 5:00am = 6:49pm
9. 5:00am = 6:49pm
10. 5:00am = 6:48pm
11. 5:00am = 6:48pm
12. 5:01am = 6:47pm
13. 5:01am = 6:47pm
14. 5:01am = 6:47pm
15. 5:01am = 6:46pm
16. 5:02am = 6:46pm
17. 5:02am = 6:45pm
18. 5:02am = 6:45pm
19. 5:02am = 6:44pm
20. 5:02am = 6:43pm
21. 5:03am = 6:43pm
22. 5:03am = 6:42pm
23. 5:03am = 6:42pm
24. 5:03am = 6:41pm
25. 5:03am = 6:41pm
26. 5:03am = 6:40pm
27. 5:04am = 6:39pm
28. 5:04am = 6:39pm
29. 5:04am = 6:38pm

Allah ya karbi Ibadunmu, kuma karmu manta da yiwa juna addu'a ta gari, gami da kasarmu Nigeria baki daya.

Bashir Ahmad
Bashirgy@yahoo.com
08032493020, 08050600160