Wednesday, June 8, 2011

KUNGIYAR TSANGAYAR ALHERI

TSANGAYAR ALHERI kungiya ce mai zaman kanta wato ba ta gwamnati ce ko ta siyasa ba, wasu mutane ne hazikai masu kaifin basira da hangen nesa, Allah ya basu ikon kirkirarta domin fahimtar da al'umma game da abubuwan da suka shafi al'amuranmu na yau da kullum da kuma irin matsalolin dake fuskantarmu a wannan zamani, mai cike da rikita-rikita, da karancin jin tsoron Allah a zuciyoyin jama'a, inda babba ke danne karami, mai kudi ke danne talaka wato zaman kashin dankali kenan.

Manyan Manufofin wannan kungiya sune: Ilmintar da al'umma game da halin wannan rayuwa, sada zumunta, taimakawa masu karamin karfi, ziyartar asibitoci, gidan marayu da kuma gidan yari (prison) don ganin irin halin da suke ciki. hakan tasa kungiyar taci sunan TSANGAYAR ALHERI sannan kaso 75% na aikin wannan kungiya na lafiya ne a shafukan Yanar Gizo kamar Yahoo Groups, Facebook da sauran shafukan sada zumunta, ta wannan hanyar ne kungiyar ke samun damar aika sakon da take son aikawa ga al'umma.

TSANGAYAR ALHERI kungiya ce ta kowa da kowa (wato Maza da Mata, Matasa, har ma da Dattijai) musamman yan arewacin Najeriya (Nigeria). Sakamakon mafiya yawan yan wannan kungiya Hausawa ne, hakan tasa kungiyar ke gabatar da harkokinta da harshen Hausa gami da koyarwar addinin Musulunci. Amma haka ba yana nuna cewa kawai Musulmi dan arewa ke da damar shiga kungiyar ba. Indai mutum dan asalin Nigeria ne da ya haura shekaru 18+ yana da damar shiga kungiyar kai tsaye tare da yardar shugabannin kungiyar.

Kungiyar na zama meeting dan tattaunawa sau biyu a duk sati. Ranar Talata da Ranar Juma'a, ranar Talata shugabannin wannan kungiya na zama don tattauna abin da ya dace a gabatar ranar Juma'a (Agenda) wato zasu duba ne a cikin satin da ya gabata wane abu ne ya faru da ya dace a tattauna akansa don samun mafita. Idan ba abin da ya faru cikin satin shugabannin cikin irin basirar da Allah ya hore musu zasu kawo wani abu da yake damun jama'a don tattaunawa.

Ranan Juma'a ranan ne za'a hadu da dukkan dan kungiya daga jihohi daban-daban a fadin kasar nan, anan za'a tattauna abin da shugabannin suka yanke ranar Talata. Daga karshe kuma a bawa kowa dama da yayi tambaya akan abubuwan da aka tattauna ko wani abu da ya shige masa dahu a cikin wannan kungiya. Sannan bayan tambaya sai a bawa masu kawo shawara dan cigaban kungiya dama da su fadi shawarwarinsu.

Na san za ayi mamakin jin cewa ana haduwa meeting da mutanen jihohi daban-daban, to wannan meeting dai ana zamansa ne cikin iska, wato ta wayar hannu (Handset) da misalin karfe 12:30 na dare (Free Call / Conference Call) sannan kuma wasu johohin masu members da yawa suna yin meeting cikin sati biyu biyu, amma wannan ba ta waya ake yin shi. A zahiri yan kungiya ke haduwa don tattauna abubuwa da dama game da kungiyar.

Ga duk mai sha'awar zama daya daga cikin dan wannan kungiya to kofa a bude take kuma cikin sassaukar hanya, misali idan mutum na amfani da shafin sadarwa na Facebook ko Yahoo Groups zai iya binciko kungiyar ta hanyar rubuta sunanta (TSANGAYAR ALHERI) anan zaiyi rijista/joining sannan ka/ki aje numbarka/ki ta MTN wadda za'a kiraka/ki yayin meeting na kungiya. Kuma idan mutum baya amfani da shafin Facebook ko Yahoo Groups zai iya zama dan wannan kungiya ta hanyar tuntubar wadannan bayin Allah:-

Jibrin Muhammad Yusi - Bajoga - 08034760327

Abdulqadir Sardauna - 08039644376

Ali Adamu Jauro - 08032950453

A cikin wadannan mutane duk wanda mutum ya tuntuba zasu yi masa cikakken bayani game da wannan kungiya daidai yadda mutum zai gamsu. Anan bazan wuce ba sai nayi amfani da wannan damar amadadin kai na nake godiya da addu'ar Allah ya karawa wadannan jajirtaccun mutane hikima da basira ya kuma daukaka su a dukkan al'amuransu, sannan ya cika musu wannan buri nasu na fahimtar da al'umma, kamar yadda suke yi ba dare ba rana. Allah ya saka da alheri.

Fatana Allah ya daukaka wannan kungiya da dukkan yayanta baki daya. Allah ya yalwata alheri a cikinta. Allah ya kara hada kanmu, Ya cika mana burinmu game da wannan kungiya ta TSANGAYAR ALHERI amin.

A karshe ina kira da jama'a masu irin wannan akida da son ci gaban al'umma da su shigo wannan tafiya, su ma su bada tasu gudunmawar ga al'umma. Da irin Ilmin da Ubangiji ya hore musu. Don shi aikin alheri baida kadan, kuma mutum bai san wane aiki Ubangiji zai duba daga cikin ayyukansa yayi masa Rahma da Gafasa ba. Don duk abin da kayi shi don Allah ba don wani ya gani ya fadi ba to tabbas Allah zai baka mafificin lada. Allah ya shige mana gaba a dukkan al'amuranmu na yau da kullum, amin!

Bashir Ahmad
bashirgy@yahoo.com
08032493020, 08050600160