Sunday, July 8, 2012

Seydou Keita Ya Bar Barcelona Zuwa China


Seydou Keita dan kasar Mali ya bar kungiyar Barcelona bayan shekaru hudu a kungiyar.

Dan wasan tsakiyar ya sanar da cewa ba zai cigaba da bugawa kungiyar wasa a kakar wasanni mai zuwa ba. A nata bangaren kungiyar Barcelonan ta yabawa Seydou Keita a kan gudummawar da ya baiwa kulub din a shekarun da suka gabata tare kuma da yi ma sa fatan alheri a rayuwarsa ta wasan kwallon kafa da kuma harkokinsa na rayuwa.

Keita wanda ya dauki kofuna goma sha hudu da Barca ana ganin ya na shirin komawa kasar China da wasa a kungiyar Dalian Aerbin. Keita dan shekara 32 ya koma Barcelona ne daga kungiyar Seville a 2008 kuma shi ne na farko da Pep Guardiola ya fara dauka da ya zama kocin kungiyar.

A shekara ta 2014 ne kwantiragin dan wasan zai kare da Barcelona, amma a bisa yarjejeniyar da suka kulla , ya na da damar barin kulub din idan ba a sa shi a farkon wasannin kungiyar ba a akalla rabi na kakar wasannin da ta gabata.

Guardiola ya rika sanya dan wasan a matsayin canji na tsawon lokaci, kuma Keita ya taimakawa kungiyar ta sami nasarar daukar kofunan Laliga uku da na zakarun Turai biyu da Kofin Sarki (king's cup) guda biyu da sauransu. Seydou Keita ya bugawa kungiyoyin Marseille da Lorient da Lens dukkanninsu a Faransa kafin ya tafi Spain inda ya yiwa Seville wasa na shekara daya sannan daga bisani ya koma Barcelona, wadda ita ma yanzu ya bar ta.

Yanzu dai Keita ya bi sahun Didier Drogba da Frederick Kanoute da Yakubu Aiyegbeni wajen komawa China don wasa.

Daga BBCHausa.com

No comments:

Post a Comment