Sunday, October 21, 2012

Gwamnonin Kasar Nan Da Suka Fi Bajinta

Sakamakon binciken da wata kungiya mai suna Eagle Eyed Youth Association of Nigeria tare da hadin gwiwar kungiyoyin sa kai fiye da 100 da kuma jin ra'ayoyin jama'a a sassan kasar nan daban - daban, ya bayyana sunayen gwamnoni a kasar guda 10 da suka fi yiwa talakawansu aiki. Gwamnonin su ne: 1) Dr. (Barr) Ibrahim Shehu Shema, na jihar Katsina. 2) Barr. Babatunde Raji Fashola na jihar Lagos. 3) Chief Rochas okorocha na jihar Imo. 4) Alh. Aliyu Wamakko na jihar Sokoto. 5) Eng. Rabi'u Musa Kwankwaso na jihar Kano. 6) Alh. Tanko Al Makura na jihar Nasarawa. 7) Dr. Rotimi Amaechi na jihar Rivers. 8) Rear Admiral Murtala H. Nyako na jihar Adamawa. 9) Alh. Sule Lamido na jihar Jigawa. 10) Comrade Adams Oshiomole na jihar Edo. Shin a naku ra'ayin wannan sakamako yayi daidai ko da son zuciya a cikinsa? Idan akwai son zuciya a naka ra'ayin wane gwamna ya kamata ya zama a matakin farko?

No comments:

Post a Comment