Thursday, September 27, 2012

Nigeria: Zan Cika Shekaru 52 Bayan Samun 'Yancin Kai Na

Kwanaki uku ya rage na cika shekaru 52 bayan samun 'yancin kai na daga hannun turawan mulkin mallakar kasar Burtaniya. Zan yi murnar zagayowar ranar ne kawai saboda ta cancanci hakan, amma ba don ina da 'yancin kan nawa ba, domin kuwa a tarihin rayuwa ta ban taba shan wahala, da rayuwa marar 'yanci ba kamar bayan samun 'yancin kan nawa da ake ikirarin wai na samu. Hmmm ta bangare na dai ba wani 'yanci da zan iya cewa na samu, sai dai samuwar rayuwar bauta da na sake samun kai na a ciki. To ku kuma 'yayana, mai za ku ce da wannan rana ta 1st October? Na san kalilan daga cikin ku suna murna da ranar har bukukuwa suke yi sakamakon zagayowarta. Amma dai bari na ji amsa daga gare ku. Shin kuna farin ciki da zagayowar ranar? Ku ziyarci Dandali Domin ba da amsoshinku.

1 comment:

  1. Hmm ko kusa ko alama, yanci kawai na masu mulki ne.

    ReplyDelete