Wednesday, July 25, 2012

Gajeren Sako Ga Makaranta Wannan Dandali

Aminci A Gare Ku!!!

Ina taya mu murnar shigowarmu watan Ramadan mai Alfarma, Allah ya gafarta mana, ya biya mana bukatun mu alfarmar wannan wata, ya sa muna daga cikin wadanda za a 'yanta a cikin wannan wata.

Nayi wannan rubutu ne a yanzu sakamokon kirana da wasu bayin Allah da suke karanta abubuwan da nake rubutawa a wannan Dandali, a waya suke tambaya ta ko lafiya kwana biyu ban cika yin rubutu ba kamar yadda na saba yi a da?

Na san wasu za su iya sanin dalilin yin hakan, ba komai bane kuwa sai don shigowar wannan wata, saboda akwai bukatar idan watan ya shigo duk wani abu da mutum yake yi ya dakatar da shi ya kusanci Allah, yayi ta rokon gafara da rahama, saboda kuwa idan wannan dama ta wuce sai kuma Allah ya kaimu wata shekarar, wanda kuma hakan ne babu tabbacin ko zamu sake ganin wani Ramadan din na gaba.

Ya Allah ya amshi ibadunmu.

No comments:

Post a Comment