Tuesday, December 14, 2010

MU CIGABA DA SON MATANMU BAYAN AURE

Akwai wani mutum mai suna Balarabe, yana
neman wata budurwa mai suna Ladidi da aure. Kullum
yana zuwa hira gidansu da yamma budurwar
tana kawo masa ruwan sha a duk lokacin
da ya zo gidansu hira.
Wata rana da yazo
sai kakar Ladidi ta ce mata: “Ga kunu mai
dumi ki kai wa Balarabe ko zai sha.” Ladidi ta ce to. Sai
ta zo ta tambayi saurayin cewa zai sha
kunu? Bayan ya yi dan murmushi ya ce "eh zan
sha", sai Ladidi ta koma cikin gida ta dauko
kunun da nufin ta kawo masa. Tana zuwa
kusa da shi sai santsi ya dauke ta ta zame ta
yi tangal-tangal ta fadi, kwanon kunun nan
ya kife a jikin sabon dinkin shadda da
wannan saurayi ya ci ado da ita. Hankalin
wannan budurwa ya tashi, ta rude ta rasa
me za ta ce masa. Amma shi gogan naka bai
damu da jika shi da kunu da ta yi ba,
hankalinsa yana kanta ne, yana cewa: “Ladi
di sannu, ina fatan dai ba ki ji ciwo ba?” Yana ta
kokarin daga ta da lallashinta, ita kuma da ta
tashi abin da ya fi damun ta shi ne yadda ta
bata masa ado da ruwan kunu. Nan take ta
je ta debo ruwa a buta tana zuba masa yana
wanke jikinsa, tana ta ba shi hakuri. Shi
kuma yana murmushi yana ce mata, ai ba
komai. Da ya ga Ladidi tana ta nuna
damuwarta kan abin da ya faru, sai ya nuna
mata alamun cewa za ta bata masa rai, ya za
a yi ta rinka damuwa kan abin da baitaka-
kara-ya karya ba! A haka dai abin ya wuce.
Bayan wani lokaci sai aka daura auren Balarabe
da Ladidi, Allah Ya azurta su da ’ya’ya guda
biyu. Wata rana da yamma Balarabe ya dawo gida
don yin wanka, sai Ladidi ta kawo masa
abinci. Bayan ta ajiye, sai ta je debo masa
ruwa a kofi da nufin idan ya gama cin abincin
ya sha ruwa. Bisa hadari sai ga babbar
rigar da Balarabe ya tube ta sarkafe Ladidi ta fadi
kasa, ruwan da ke kofin ya zube a jikin
Balarabe, ai sai ya mike tsaye ya rinka
bambami, kai ka ce wuta ta zuba masa. “Ke
dai wallahi ban san ranar da za ki yi hankali
ba! Sam ba ki da lissafi da natsuwa! Idan ban
da hauka da rashin hankali, me ya jawo
haka? Ke dai kam Allah wadaran ki........!”
Karshe dai wannan dalilin sai da ya janyo
Balarabe ya saki Ladidi.

Mu yi nazarin wannan abin da idon basira,
lokacin da Balarabe ke neman matarsa da aure,
ta yi masa barin kunu mai zafi a jikin sabbin
tufafinsa, amma bai nuna bacin ransa ba,
hasali ma yana nuna wannan abin ba komai
bane illa hatsari. Amma yau barin ruwan
sanyi ya zama tamkar ruwa narkakkiyar dalma! Mu duba
yadda ya damu da ita a wancan lokacin,
amma yau ba damuwarsa ne ta ji ciwo ko
ba ta ji ba, shi dai kawai laifin da ta yi masa
yake kallo.

Ya kamata Maza murin ka tuna baya lokacin da matayen mu suka saba mana ba kawai mu yanke hukunci a lokacin ba.

Bashir Ahmad
Bashirgy@yahoo.com
08032493020

Saturday, December 11, 2010

KISHI ASALI YA SAMO

KISHI dai wata damuwa ce da takan sami
zuciyar mutum, ko kuma shi mutum ya sa
kansa a cikin wata damuwa a lokacin da
yake ganin alamar zai rasa wani abu da
yake matukar kauna, wanda idan mutum
ma bai yi hankali ba sai ya shiga cikin wani
irin hali na kaka-nika-yi, har ma ya zo yana
da-na-sani.
Kodayake kishi iri-iri ne, amma wanda muka
fi sani, kuma muke magana a kai, shi ne
kishi na tsakanin matan da ke auren miji
guda. Shi kishi ya samo asali ne tun zamanin
kakanmu Annabi Ibrahim (A.S) A cewar
wasu Malamai, wai tsakanin matansa Saratu
da Hajara. A lokacin da Allah bai ba wa
Saratu haihuwa ba, sai Sarkin Masar ya bai
wa Saratu, Hajarah domin ta rika taya ta
aikace-aikace da wasu hidimomin gida.
Daga bisani ita Saratu ta shawarci mijinta
Annabi Ibrahim (A.S) ya auri Hajarah ko Allah
Zai ba shi haihuwa.
Allah, Mai hikima, cikin ikonSa, bayan an
daura aure da dan lokaci kadan, sai Hajarah
ta sami ciki. Hakan bai yi wa Saratu dadi ba,
ya kuma sosa mata zuciya. Cikin bakin ciki,
ta shawarci mijin nata da ya sa a huda wa
Hajarah kunnuwa da hanci. A cewarta, yin
hakan zai nuna cewar ita kuyanga ce. Bisa
ga ikon Allah sai Hajarah ta kara kyau da
wannan hujin kunne da hanci da aka yi
mata. Har wa yau Saratu ta ce a’a. A daura
wa Hajarah awarwaro, a sa mata ’yan
kunne. Yin haka ya sake kara mata kyau
wanda ma ko wucewa take sai an san
matar Annabi ce ke wucewa.
A karshe duk abin nan da ake yi bai gamsar
da Saratu ba, sai cewa ta yi, ta ga Hajarah
tana kumburi don haka maigida ya fitar da
ita a gidan, kada ta sa musu wata cuta. Allah
mai girma da daukaka Ya umurci Annabi
Ibrahim da ya dauki matarsa wato Hajarah
ya kai can wani gari (Makka) wanda a yau
ya zama tsarkakakken wurin da kowane
Musulmi ke burin ziyarta. Duka shawarwarin
nan da Saratu ta yi ta ba wa Annabi Ibrahim,
ta yi ne a bisa kishi.
To ashe ke nan kishi yana da asali, amma ba
wai ana nufin ya zama halas ba ne don ya
samo asali a wurin Saratu da Hajarah. Kishin
wannan zamani ya sha bamban, nesa ba
kusa ba da irin kishin da Saratu ta nuna. A
yanzu akan nemi a yi kashe–kashe da
asarar dukiya. Matar aure ta kan bi karuwa
gidanta, ta ci mata mutunci, wai don ta ji
labarin mijinta na neman ta. Haka kuma
budurwa ta bi matar aure gida ta ci
zarafinta. Ballantana tsakanin kishiyoyi abin
ba a cewa komai.
Abin tambaya a nan shi ne, shin me ake wa
kishi? To ra’ayin wasu matan dai ya yi nuni
da cewar mazan su ne umul aba’isin da ke
haddasa kishi, a lokacin da suka kasa yin
adalci tsakanin matansu. Alal misali kai ne ke
da mata biyu sai ka nuna fifikon wannan da
‘ya’yanta a kan daya, ka ga dole ne a nan za
'a samu damuwa, wadda ka iya haifar da
kishi tunda dukkansu soyayya ce ta sa ka
tara su, don haka dole ne ka yi adalci, a
tsakaninsu.

Wasu mazan kuwa na ganin wulakancin
matan ne kan ishe su, su shiga aure-aure.
Saboda a lokacin da mace take jin kai, sai ta
yi ta nuna wasu irin halaye daban-daban, a
inda ka yi gargadi ka gaji, dole ne ka nemi
wata wacce za ta kwantar ma da hankali.
Yin hakan kuma shi ke sosa zuciyar mata. A
takaice dai soyayya ake wa kishi.
To, wane lokaci ne ya kamata a nuna kishi?
Alal hakika idan mace ta ga an fita harkarta
kwata-kwata, wato, ba a yi da ita, ta yadda
miji bai kulawa da ita ko ‘ya’yanta, to, a nan
fa dole ne hankalinta ya tashi, saboda ganin
a da shi nata ne ita kadai, a yau kuma ya
koma nasu.
Kashi casa’in bisa dari na maza haka suke,
da zarar sun sami sabuwar amarya ko da ta
’yar tsana ce, sai kwata-kwata su juya wa
uwargida baya, har sai in ruwa ya kare wa
dan kada, sannan a dawo yana tsilla-tsilla a
gefen teku.
Bugu da kari akwai wata babbar matsalar
da ke addabar mata a wannan lokaci ta
yadda maza suke bata wa matansu na aure
suna a wurin abokansu. Misali miji ne ya
sami sabani da matarsa, maimakon ya yi
kokarin yi mata nasiha ko ya gaya wa
iyayenta, a’a, sai dai ka ga ya tafi wata
matattara da ake kira Chamber, yana yi wa
matarsa tonon silili. Wani ma, wallahi, har
yadda yake kwana da matarsa yake fadi.
Yin haka ya kazanta. A nan za a ba wa
namiji shawarar ya je ya kara aure. Auren
da zai yi ba wai don raya sunnar Manzon
Allah (SAW) ba ne, a’a, sai dai don ya ci
zarafin matar gida.
Haka kuma tun daga waje zai zayyana wa
budurwar irin halayen matarsa ta gida, in ta
dauro ma akan yi wa amaryar alkawarin da
zarar ta shigo za a kori ta gidan. A nan idan
ba a iya korarta ba, to, sai a yi ta zaman
kwari, kowa na ji da kanshi, a yi ta zuba
kishi iri-iri. Daga nan in ba a yi hankali ba sai
mazuga su shiga tsakaninsu, su tura su ga
halaka ta hanyar bin gidan bokaye don
neman asirin samun gindin zama a wurin
miji. Uwargida na neman kwatar ’yanci,
amarya na cewa sai ta fita ta bar mata gida.
To, boka na iya yi wa mutum abin da Allah
bai yi niyyar yi masa ba?
Har ila yau akwai wasu mazan da kansu da
kuma hannayensu bibbiyu suke rura wuta a
gidansu, su haddasa fitina, su hana zaman
lafiya, ta yadda namiji yake zana munafiki
tsakanin matansa. Shi wannan namijin, shi
zai ta kai da komowa tsakanin matansa,
wato, in ya je wurin wannan sai ya ce, ai ga
abin da waccan ta ce, ko take yi, sannan
idan ya koma wurin waccan sai ya ce, ai ga
abin da wannan ta yi, ga abin da ta ce. Shi
dai yana jin dadin ya ga kawunansu a
rarrabe, wato a yi ta fada saboda shi.
Jahilan maza har cewa suke in mata suka
hada kansu, namiji ba ya jin dadi. Mu kuma
a wurinmu mata ba abin da hakan ke
haddasawa sai koma baya, ga rashin
kwanciyar hankali, domin ko shi kansa mijin
a cikin fargaba yake a duk lokacin da ya
tunkari gida, sai dai idan ba gida daya ya
hada su ba.
Bari in ba mata misali na wani gida da nake
aminci da su. Kullum na kai ziyara zan iske
matan mutamin su uku tare da maigidansu,
wannan na yi mai, tausa, waccan na
mammatsa masa kafafuwa da sauransu. A
koda yaushe suna cikin farin ciki tsakaninsu
da maigidansu. Da na tambaye shi, ko wane
irin asiri ne ya yi wa matansa?. Sai ya nuna
cewa babu asiri a ciki, illa kawai, dukkan
matan nasa masana ne, kuma shi ba ya
auren mace face sai ya koyar da ita
tarbiyya, na yadda za ta yi zama tare da shi
da kuma kishiyoyi kamar yadda Annabi
(SAW) ya zauna tare da matanSa.
A karshe ina shawartar mata su yi hakuri a
kan maganar kishiya, tunda Allah ne da
kanSa Ya umurci maza da yin aure fiye da
daya. A Alkur’ani Allah Ya ce “Ku auri mata
bibbiyu ko uku, ko hudu, amma in kuna
tsoron ba za ku yi adalci ba, to, ku auri
daya” Suratul Nisa’i. Sannan Manzo Allah
(SAW) Ya ce “Ku yi aure ku hayayyafa,
domin na yi alfahari da ku ranar alkiyama”
Saboda haka aure fiye da mace daya ba
aibu ba ne, in dai an yi don raya sunnar
Manzo ne, tabbas Allah Zai taimaki bawanSa.
Ga mazan kuma ina shawartar ku da ku ji
tsoron Allah! Ku yi hattara! Ku guji
gamuwarku da Allah! Kada ku ga kamar
Allah Ya ba ku ’yanci na aure da saki, ku ce
za ku yi yadda kuke so. Mata amanar Allah
ne gare ku, matukar kuka ci amana, ko
shakka babu za ku tsaya a gaban Allah ku
fuskanci shari’a. Idan muka yi koyi da
yadda Manzon Allah (SAW) ya zauna da
matansa, tabbas za mu samu rayuwa mai
inganci da albarka daga mu har zariyarmu.

Haka nan ina kara shawara jama’a maza da
mata, mu dage mu nemi ilimin Islama,
musamman abin da ya shafi zamantakewar
aure, komai kake yinsa cikin ilimi ya fi dadi,
ya fi sauki. Allah Ya ba mu ikon yi, Ya kuma
sa mu dace da rayuwa mai albarka. Amin.

SIYASAR KANO, A ZABEN 2011

Siyasar Jihar Kano ta dade tana ba ’yan
kasar nan mamaki. Wannan shi ya sa ake yi
mata kirarin “siyasar Kano sai Kano” Wadansu kuma na da ra’ayin cewa “ba'a
mulkin Kano sau biyu” Tabbas kirarinta na
farko yana da muhalli ba a Kano kadai ba
har a Nigeria baki daya. Gwamna Ibrahim
Shekarau ya dakushe ra’ayin “Ba'a mulkin
Kano sau biyu” saboda zarcewar da ya yi,
inda shekara mai zuwa zai cika shekara
takwas a kan mulkin Kano.
A wannan karo za a raba rana ne tsakanin
jam’iyyun siyasa uku watau, Jam’iyyar ANPP
mai mulkin Jihar da Jam’iyyar CPC sai kuma
Jam’iyyar PDP da aka amshe mulki daga
hannunta a zaben 2003. Amma wasu na
ganin cewar tarnakin siyasar na nan
tsakanin Jam’iyyun ANPP da CPC ganin
yadda suke da magoya baya, amma wasu
na ganin cewa duk wanda yake ganin
Jam’iyyar PDP ba barazana ce ga sauran
Jam’iyyun biyu ba, to wata kila baya kasar
Kano lokacin da Jam’iyyar ta yi zagayen
motsa jam’iyya, inda dimbin magoya
bayanta suka tare ta a daukacin kananan
hukumomi 44 da jihar take da su.
Ba nan gizo ke saka ba musamman idan
muka yi la’akari da matsalolin da ke cikin
jam’iyyun uku a kan fitar da ’yan takararsu
a zaben raba gardamar jam’iyyun siyasa da
za a gudanar daga ranar 26 ga watan
Nuwamba zuwa 15 ga watan Janirun badi.
A Jam’iyyar CPC akwai ’yan takara a kalla
biyar da suka hada da: Kanar Lawal Jafaru
Isa, Tsohon gwamnan JiharKaduna da
Injiniya Magaji Abdullahi da Muhammad
Abacha dan marigayin shugaban kasa Janar
Sani Abacha da Dokta Auwal Anwar da kuma
Rufa’i Sani Hanga. Masu nazarin yadda
siyasa ke tafiya sun yi hasashen cewa
Kanar Lawal Jafaru Isa ne ya fi cancantar
jam’iyyar ta tsayar amma bisa dukkan
alamu akwai kishin-kishin cewa Rufa’i Sani
Hanga ne dan-lelen shugabannin jam’iyyar
da Ahmadu danzago ke jagoranta bisa
dalilin da ba su bayyana ba. Har ila yau
wasu na cewa akwai yarjejeniya ta
karkashin kasa tsakanin sauran ’yan takarar
3 ta cewar za su mara wa daya daga cikinsu
baya idan har aka ci gaba da nuna musa
bambanci wanda kuma hasashe jama’a ya
nuna Kanar Lawal Jafaru Isa na iya zama
zabinsu.
A ra’ayoyin mutane da dama suna gani
warware wannan matsala na iya kawo wa
Jam’iyyar nasara a zabe mai zuwa ganin
yadda jama’ar Kano suka yi na’am da
Jam’iyyar CPC , wasu kuma na ganin ko
babu komai farin jinin da Janar Buhari yake
da shi zai iya kawo musu babbar nasara
kamar yadda ya kafa Gwamnatin ANPP a
zaben 2003. Haka nan kuma ita kadai ce
jam’iyyar da ba ta taba mulki ba balle a ce ta
saba wa wani.
Idan muka waiwayi Jam’iyyar ANPP mai
mulkin Jihar Kano za mu ga yadda ’yan
takara da suka hada da: Salihu Sagir Takai Kwamishinan ruwa na jihar da Injiniya
Abdullahi Tijjani Muhammad Gwarzo,
Mataimakin Gwamna Ibrahim Shekarau da
Senata Kabiru Gaya da Lawal Sani kofar
mata da Malam Ibrahim Khalil, suka fito da
niyyar karawa da junansu a zaben raba
gardama. Tarnakin da suke fama da shi a
jam’iyyance sun hada da zargin da ake yi na
cewa Malam Ibrahim Shekarau ya fifita
Salihu Sagir Takai a kan sauran ’yan takarar
hudu wanda hakan ke neman kawo cikas a
jam’iyyar da har wasu ke tunani yi wa
jam’iyyar zagon kasa idan har aka yi musu
rashin adalci. Haka nan kuma akwai babban
kalubalen da ke fuskantar gwamnatin Jihar
Kano ta ANPP, shugabannin kananan
hukumominta sun shigar da kara kotu
saboda sauke su da aka yi daga kan mulki.
Akwai tunanin cewa duk wadanda aka yi
wa ba daidai ba zasu iya yi wa jam’iyyar
zagon kasa wanda wasu na ganin
wadannan shugabannin kananan
hukumomi da aka sauke sune ’yan siyasar
kwarai da ya kamata jam’iyyar rike.
Wasu kuma suna hangen cewa maganar da
Alhaji Mahmud Ado Bayero, Hakimin Fagge ya
yi a kan biyan diyya ga wadanda kwayar
maganin Troban ta kamfanin Pfizer ya
nakasa tamkar wani haske ne mai nuni
yiwuwar akwai takun saka tsakanin
masarautar Kano da gwamnatin jihar, kuma
ko da masarauta ba ta cika shiga siyasa kai
tsaye ba, suna da jama’a irin na su
musamman idan aka yi la’akari da irin
martaba da Sarkin Kano yake da ita ga
mutanen jihar.
Wani kalubalen da ake hange kuma shi ne,
idan har aka samu matsala a zaben raba
gardama tsakani Gwaman Shekarau da
mataimakinsa Alhaji Abdullahi Tijjani
Muhammad Gwarzo yana iya haifar wa
jam’iyyar matsalar da Allah kadai ya san
idan za ta tsaya musamman idan
mataimakin na shi ya samu goyon bayan
sauran abokan neman tsayawa takarar
gwamna da suka rasa.
Ita kuwa Jam’iyyar PDP, masu nazarin
siyasar Kano na ganin a aljihun tsohon
gwamnan jihar, Alhaji Rabi’u Musa
Kwankwaso ta ke, saboda har inda yau take
ba za a ce ga takamaiman dan takararta ba
sai dai akwai irinsu Kanar Habibu Shu’aibu
da suka bayyana niyyar tsayawa takararsu
da kuma shi kansa Dokta Rabi’u Musa
Kwankwaso, sai kuma wasu da ke jita-jitar
fitowar Hon. Faruk Lawal. Masu
hasashen siyasa na ganin cewar da wuya
PDP ta yi tasiri musamman idan aka yi
la’akari da dalilan da suka sa Kwankwaso ya
rasa kujerarsa a zaben 2003, watau
matsalar da ya samu da ’yan fansho da
sauran ma’aikata, sai kuma wasu da ke
ganin faduwarsa na da nasaba da rashin
jituwarsa gidan sarautar Kano.
Akwai kuma masu ganin cewa bai kamata a
tsayar da Kwankwaso ba saboda yana da
takardar tunhuma watau white Paper,
saboda haka suna son a fito da sabon dan
takara wanda ba shi da wata matsala da za
ta hana shi cin zabe, sai dai kuma wasu na
ganin wannan ba matsala ce ba tun da a
cewarsu ’yan majalisa sun wanke
Kwankwaso kuma gashi dan lelen Shugaba
Goodluck Jonathan. Duk da haka dai ana
ganin cewa kwankwasiya shugabannin
Jam’iyyar PDP suke yi wa biyyaya, haka nan
kuma ita ke da rinjayen magoya bayan
Jam’iyyar PDP a Kano.
Daga karshe dai masu fashin bakin siyasa
na ganin cewa idan har Jam’iyyar PDP ta
tsayar da Rabi’u Musa kwankwaso a
matsayin dan takararta to zai riga rana
faduwa saboda jama’a ba su san shi,
dalilinsu kuwa shi ne, ya gwada takara ba
sau daya ba yana faduwa kuma ya tsaida
dan takara ya fadi, sa’anan kuma ya kasa
gano inda yake da baraka balle ya dinke ta
ga shi kuma yana goyon bayan Shugaba
Goodluck inda wasu ke cewa sun ce ko
nawa za su kashe sai sun kawo Jihar Kano
A takaice dai guguwar siyasar ta fi kadawa
tsakanin jam’iyyun CPC da ANPP wanda
wasu ke ganin muddin Jam’iyyar CPC ta ba
Kanar Lawal Jafaru Isa takara ganin yadda
mutane ke son shi zai yi tasiri kwarai
wanda har ana yi masa kallon zama
gwamnan jihar, sai dai kuma wasu na ganin
cewar muddin Gwamna Ibrahim Shekarau
ya bari aka yi zaben raba gardama kamar
yadda dokar Jam’iyyar ANPP ta tanadar
akwai kamshin za su iya tabukawa wajen
samar da gwamna a jihar.

(Aminiya)

Thursday, December 9, 2010

FALLASAR WIKILEAKS NA NEMAN TADA HANKALIN HUKUMOMIN NIGERIA


Bayanai na baya-bayan nan da shafin
intanet na Wikileaks mai kwarmata
bayanan sirrin da aka tsegunta masa
ya wallafa, sun bayyana irin rawar da
Amurka ta taka a lokacin da
Goodluck Jonathan yake matsayin
mukaddashin shugaban Nigeria a
yayinda shugaba na wancen lokaci
Umar Yar'adua yake jinya.

Bayanan sun ambato Goodluck
Jonathan da cewar ya na kokarin
shawo kan jama'ar Arewacin Najeriya
wadanda ba su saki jiki da shi ba, ta
hanyar amfani da wasu manyan
mutanen yankin arewan, musamman
tsohon shugaban Nigeria
Abdussalami Abubakar wanda zai
lallashi iyalin 'Yar Adua, su saka shi, ya
yi murabus cikin daraja da mutunci.

Haka kuma zai bi shawarar Amurka ta
nisanta kansa da Olusegun
Obansanjo.
Jakadiyar Amruka a Najeriya a lokacin
Robin Saunders ta gana da
mukaddashin shugaban kasar
Najeriya a lokacin wato shugaban
yanzu Goodluck Jonatahan ranar 26
ga watan Fabrairun bana, jim kadan
bayan da marigayi shugaba 'Yar'adua
ya koma Najeriya daga Saudiyya inda
yayi jinya.

Jonathan ya kuma fada mata cewa a
saninsa jam'iyyar PDP ta zabe shi ne a
matsayin abokin takarar shugaba
'YarAdua a 2007 saboda yana
wakiltar yankin Niger Delta.
Ya ce "ba an dauke ni ba ne na zama
mataimakin shugaban kasa saboda
ina da wata kwarewa ta siyasa. Ba ni
da ita. Da akwai mutane da dama da
suka fi cancanta su zama mataimakin
shugaban kasa, sai dai kuma wannan
ba yana nufin wani zai iya juya ni ba.
Bayanan suka ce Goodluck Jonathan
ya ce yana kokarin shawo kan
jama'ar Arewacin Nigeria wadanda ba
su saki jiki da shi ba, ta hanyar amfani
da wasu manyan mutanen yankin
arewan, musamman tsohon
shugaban Nigeria Abdussalami
Abubakar wanda zai lallashi iyalin 'Yar
'Adua, su saka shi, ya yi murabus cikin
daraja da mutunci.
Hakan in ji Goodluck zai fi sauki a
madanin samun goyon bayan kashi 2
cikin 3 na majalisar ministoci mai
mutum 42. Ya kuma bayyana yadda a
wani zaman majalisar minitocin aka
tashi baram-baram inda aka yi ife-ife.


Goodluck ya dora laifin rudani a kan
mutane hudu
Goodluck ya dora laifin rudanin da
aka shiga a Najeriya a lokacin kan
mutane hudu dake kewaye da 'Yar
'Adua, wato uwargidansa Turai 'Yar
'Adua, da babban mai tsaron lafiyar sa
Yusuf Tilde da dogarin shugaba
'Yar'Adua Mustapha Onoe-dieva da
Tanimu Kurfi mai baiwa marigayin
shawara kan harkokin tattalin arziki.


Haka kuma ya ambaci Abba Ruma
ministan ayyukan noma da Adamu
Aliero ministan birnin Abuja a
matsayin wasu masu hana ruwa
gudu.


Goodluck Jonathan yace ya yarda
wadannan mutane suna da wata
muguwar aniya, tun da yayi imanin
cewa shugaba 'Yar Adua baya cikin
hayyacinsa.

A game da yadda zai tunkari warware
dambarwar siyasar Najeriya kuwa
mukaddashin shugaban kasa
Goodluck Jonathan ya ce zai mai da
hankali kan shirya zabe na fisa-bi-
lillahi.


Kuma baya tsinkayen zai tsaya
takarar shugaban kasa a 2011,
kodayake dai a cewarsa "idan suna so
in tsaya, to wannan wani abu ne da
zan nazarta".

Kuma jakadiyar Amruka ta bayyana
masa cewa wajibi ne ya sallami
shugaban hukumar zabe mai zaman
kanta wato INEC, Prof Maurice Iwu
saboda baya nuna wata alama ta
mutunta tsarin mulki na gari.
Jakadiyar ta yi barazanar cewa
muddin Goodluck bai kori Iwu ba, to
gwamnatin Amurka zata janye duk
wani tallafi na shirin zabuka a Nigeria.

Bayanan na Wikileaks sun ce
jakadiyar Amurka ta kuma baiwa
Mukaddashin shugaba Goodluck
shawarar nisanta kansa da tsohon
shugaban Nigeria Olusegun Obasanjo,
kuma Goodluck ya ce zai yi hakan.

(BBC HAUSA)
www.bbchausa.com

Monday, December 6, 2010

SHIN "TAKAI" ZAI TAKI SA'A A KANO A 2011 KUWA?

Malam Salihu Sagir Takai, babu tantama kan
cewa shi ne dan takarar Gwamna a karkashin
Jam ’iyyar ANPP. Gwamna Malam Ibrahim
Shekarau ke son ya zama magajinsa a zaben
shekara mai zuwa, hakan na nuni da cewa
Shekarau ya fi natsuwa da ganin cancantar
Takai kan sauran mabiyansa. Kamar
Mataimakin Gwamna Abdullahi T. M. Gwarzo da
Garba Yusuf da Sani Lawan kofar-Mata da
Injiniya Sarki Labaran da Musa Iliyasu
Kwankwaso da Malam Ibrahim Khalil.
Kafin zancen ya fito fili kan goyon bayan
Takai rahotannin sun nuna cewa mabiya
Malam Shekarau a jam ’iyyance sun ba shi
dama ya zabi duk wanda yake ganin ya fi
cancanta su yi masa biyayya. Amma da ya
buga gangar zuwa ga Takai, sai masu
sha ’awar takarar Gwamna da ’yan siyasa suka
yi tsaye, don rawar ba za ta yi daidai da kidan
ba, inda suka fara koke-koke da kokarin nusar
da Gwamna ya yi adalci wajen fitar dan
takara. A takaice suna kira da a yi zaben fitar
da gwani a jam ’iyyar don su zabi wanda suke
ganin ya fi dacewa ya gaji Gwamna Shekarau.
Takai ya taba zama Kwamishinan kananan
Hukumomi a gwamnatin Shekarau, Gwamnan
ya zabe shi ne bisa wasu dalilai na kashin
kansa, har yanzu bai fito ya bayyana wa
al ’ummar Jihar Kano dalilansa na fifita Takai a
kan sauran masu neman takarar Gwamna ba.
Shekarau ya yi amfani da wannan damar ce
ya tsayar da dan takara, don ya san cewa a
tsari na dimokuradiyya da wuya Gwamna ya
tsayar da dan takara, jam ’iyyarsa ba ta tsayar
da nata ba.
Jam ’iyyar ANPP a Jihar Kano ta yi farin jini,
masu son tsayawa takarar Gwamna a cikinta,
suna da yawa kwarai kuma jiga-jigai a
jamiyyar, irin su Mataimakin Gwamna
Abdullahi Tijjani Gwarzo da Sanata Kabiru Gaya
da Sani Lawan kofar-Mata da Malam Ibrahim
Khalil da Habibu Sale Minjibir da sauransu suna
nan.
A bisa tsarin jam’iyyu, a kan ba ’yan takara
damar yin sulhu a tsakaninsu, in hakan ta
gagara sai a sake ba su wata dama ta shiga
zaben fitar da gwani, a nan ne ake gwada
farin-jini da kwanji don samun wanda ya yi
nasara a tsakaninsu. Kukan da ’yan takara a
Jam’iyyar ANPP a Kano ke yi, don hanyar da
aka dauka ga dukkan alamu suna zargin ba za
a yi masu adalci ba ne.
Tuni mafi yawan ’yan takarar sun fito karara
sun bayyana rashin amincewa, da take-taken
Gwamna Shekarau na kin ba su dama ta
hanyar cusa nasa dan takarar. Sanata
Mohammed Bello ya fito ya bayyana wa
duniya cewa in har ba a ba shi damarsa ba, zai
fice daga jam ’iyyar da hakarsa ba ta cimma
ruwa ba, ya cika alkawari ya tafi Jam’iyyar
PDP. Haka kuma sauran ’yan takarar duk sun yi
magana da murya guda wajen kin yarda da
tsaida Takai da kuma mara masa baya.
Mene ne ya sa Gwamna Shekarau ya kafe a
kan Takai ne dan takara? Ko kuwa yana ganin
cewa shi ne zai ci gaba da manufofin
gwamnatinsa? Shin shi ne zai kawar da kai ga
masu bukatar a tono abin da ya binne bayan
ya bar mulki? Ko kuma yana ganin a tunani da
hangen nesa irin nasa Takai ya fi sauran masu
neman Gwamnan Jihar Kano cancanta ce?
Sauran ’yan takarar suna ganin sun cancanta,
sun kuma taimaka wa Shekarau a zaben
shekarar 2003 da 2007. Don haka, suna ganin
suna da goyon baya da masoya da magoya
baya da za su iya kai su gaci a zabe mai zuwa.
Wannan ya sa suka yi gangami, inda
kowanensu ya nuna wa duniya karfinsa a
siyasance.
Tsayar da Takai na fuskantar tirjiya, ba daga
’ yan takarar Gwamna kawai ba, har da sauran
’yan takara na kananan hukumomi da jami’an
gwamnati da masu fada-a-ji a Jam’iyyar ANPP.
Saboda wasu dabi’u da ake zargin Takai yana
da su, kamar rowa da rashin iya hulda da
jama ’a.
Shawara ga Malam Ibrahim Shekarau, idan har
yana son Jam ’iyyar ANPP ta taka rawar gani a
zabe mai zuwa, ya kamata a matsayinsa na
uba kuma jagora, ya hada kan ’ya’yan
jam’iyyar. Ya kuma zama mai yin biyayya ga
tsarin dimokuradiyya, ta hanyar ba kowa
damarsa, ta bari a yi zaben fitar gwani a
jam ’iyyar ba tare da fitowa karara yana mara
wa wani dan takara baya ba.
Gwamna Shekarau ya sani cewa idan ya matsa
sai Takai, hakika wadansu daga cikin
aminansa da abokan tafiyarsa a siyasa za su
iya yin tsalle su ma fice daga jami ’iyyar, da ma
ba ta gama farfadowa daga halin da ta shiga
ba sakamakon ficewar Janar Muhammadu
Buhari daga jam ’iyyar, sannan wadansu za su
iya kin ficewa daga jam’iyyar su kuma yi mata
zagon kasa.
Ya kamata Gwamna Shekarau ya tambayi
kansa, shin yana da tabbas in Takai ya zama
Gwamna ya samu biyan bukatunsa? Ba ya
kallon yadda ake kwashewa tsakanin
gwamnonin da suka sauka da wandanda suka
gaje su?
Shekarau kada ya manta akwai jan aiki a
gabansa, ko da ’yan jam’iyya kansu a hade
yake, kafin su iya lashe zaben shekarar 2011.
A kullum Jam ’iyyar PDP a Jihar Kano sai kara
karfi take yi ga kuma sabuwar Jam’iyyar CPC
da Janar Buhari ke ciki, in har sun tsaida dan
takaran Gwamna mai nagarta su ma za su iya
lashe zaben Gwamna a Kano a shekarar 2011.
Tsakanin Gwamna Shekarau da Takai da masu
adawa ba a san maci tuwo ba, sai miya ta
kare. Ko Takai zai taki sa ’a ya zama magajin
Shekarau? Lokaci ne kadai zai bayyana mana.
Shehu Mustapha Chaji

Friday, December 3, 2010

TAKAITACCEN TARIHIN BABAN SADIQ


Abdullahi Salihu Abubakar wato (Baban Sadiq) an haife shi a anguwar Hausawa, Garki Village dake karamar hukumar Birni (Munincipal) a cikin babban birnin tarayya Abuja, a shekarar 1976 shekaru 34 da suka wuce kenan.

Asalin kakannin Baban Sadiq dama wasu daga cikin mazauna anguwar Hausawa, Garki Village daga Kanon Dabo suka zo, shekaru sama da dari biyu (200) da suka gabata.

Baban Sadiq yayi karatunsa tun daga Firamare, Sakandare har zuwa Jami'a duk a cikin babban birnin tarayyar Nigeria Abuja.

A halin yanzu Baban Sadiq na da shedar digiri akan fannin tsimi da tanadi (Economics) sannan kuma har yanzu yana kan neman Ilimin Al-Qur'ani da sauran fannoni daban daban kan addinin Musulunci.

Abdullahi Salihu Abubakar (Baban Sadik) mutum ne mai sha'awar rubuce-rubuce da karance-karance da kuma son binciken ilimi kan fanni daban daban musamman Tsimi da tanadi (Economics) da kuma Fasahar Sadarwar Zamani (Information Technology) da sauran fannoni da dama.

Baban Sadiq mutum ne mai son ganin al'ummar Hausawa sun fahimci fasahar zamani, kuma Allah ya hore masa juriyar karatu da rubutu daidai gwargwado.

Saboda yadda yake son ganin Hausawa sun fahimci fasahar zamani suma an tafi dasu kamar kowacce al'umma kar a barsu a baya Baban Sadiq ya rubuta litattafai kan wannan harka mai muhimmanci ga kowacce al'umma. Duk da littatafan bai kammala su ba amma akwai "Fasahar Intanet A Saukake" cikin harshen Hausa wanda ke kan hanyar fitowa ko wane lokaci daga yanzu.

Sannan kuma sai wadanda yake rubutawa sun hada da: Tsarin Mu'amalar Da Fasahar Intanet da kuma Wayar Salula Da Tsarin Amfani Da Ita.

Duk da haka Baban Sadiq bai tsaya nan ba yana gabatar da kasida mai suna "Fasahar Intanet" a jaridar Aminiya duk mako, inda masu karatu ke aiko da tambayoyin abinda basu gane ba yake basu amsa nan take daidai yadda zasu gane.

Bayan haka Baban Sadiq na da makarantar Kimiya da Fasaha a shafin intanet mai suna "Makarantar Kimiyya Da Fasahar Sadarwa" wanda za'a iya samu a (http://fasahar-intanet.blogspot.com) wannan makaranta na da dalibai masu yawa a ciki da wajen Nigeria, kamar su Niger da Cameroon.

A karshe Baban Sadiq na da aure da 'yaya uku Sadiq, Nabilah da kuma Hanan.

Bashir Ahmad
Bashirgy@yahoo.com
+2348032493020