Saturday, September 1, 2012

Buhari Ya Ziyarci Kwankwaso


Tsohon Shugaban kasa kuma dan takarar Shugaban kasa a zaben bara a karkashin Jam’iyyar CPC Janar Muhammadu Buhari ya kai ziyarar jaje ga Gwamnan Jihar Kano Dokta Rabi’u Musa Kwankwaso dangane da tashe-tashen hankula da jihar ke fama da su,

inda ya nemi Gwamnatin Tarayya ta yi duk abin da za ta iya don kawo karshen rashin tsaro da ke dada tura mutane cikin ‘bakin talauci’ a Arewa.
Janar Buhari wanda ya ziyarci Gwamna Kwankwaso a shekaranjiya Laraba ya bayyana rashin tsaro a Jihar Kano da wasu jihohin Arewa a matsayin “Babban abin bakin ciki,” inda ya ce ya yi matukar kawo nakasu ga kasuwanci da sauran harkokin tattalin arziki.
Janar Buhari ya ce: “Na zo ne domin in gaida Mai martaba Sarkin Kano kuma in yi muku jaje kai da shi kana bin bakin cikin da ke faruwa na tashin bama-bamai da kuma tsauraran matakan tsaron da ake dauka da suke takura wa jama’armu.”
Janar Buhari, wanda ya je jihar don bude sakatariyar Jam’iyyar CPC ya ce, Kano wadda a baya ta yi suna a duniya wajen harkar kasuwanci a yanzu tana neman komawa kufai. “Wannan babban abin bakin ciki ne, kuma ina fata za ku kawo karshen hakan cikin gaggawa,” inji shi.

A cewar Buhari, duk da macewar kamfanoni da matakan tsaron da ake dauka a Kano, ba kowa ne daga farko ya fahimci tabarbarewar al’amuran tattalin arziki a kasar nan ba, “said a matsalar Borno da Yobe ta yi kamari,” inji shi.
“Kasancewar na yi Gwamna a yankin, na san a kullum akalla motoci 200 ke barin nan zuwa Maiduguri wasu kuma su yiwo nan. Kuma a Maiduguri za ka iske ’yan kasuwa daga kasashen Kamaru da Chadi da Nijar. Wanna yanzu ya zama tarihi. Ku tsaya ku yi nazari dimbin ’yan Najeriya musamman na wannan yanki da a yanzu aka jefa su a cikin mummunan talauci. Don haka ina fata gwamnatin tsakiya za ta yi duk abin da za ta iya wajen an magance matsalar cikin gaggawa,” inji shi.

Daga nan sai Janar Buhari ya ce Jam’iyyar CPC za ta bude sakatariyarta a Kano ne, domin ta kintsa tare da taka rawar ’yar adawa ganin an riga an kawo karshen rikicin cikin gida da ke damunta.

A nasa jawabin Gwamna Rabi’u Kwankwanso ya ce, gwamnatinsa tana aiki da hukumomin tsaro don janye shigayen duba ababen hawa, domin ba jama’ar damar walawa da shiga da faitar da kaya daga jihar.

Gwamna Kwankwaso ya yaba wa Janar Buhari kan samun lokaci ya kai masa ziyarar girmamawa duk da bambancin jam’iyya da suke da shi. “Abin da Janar ya yi shi ne abin da ya kamata dukkan ’yan siyasa su rika yi, saboda bambancin siyasa ba yana nufin zama abokan gaba ba ne.”

A yayin da yake gabatar da jawabi a harabar sakatariyar jam’iyyar, shugaban rikon Alhaji Muhammad Ahmad ya bayyana farin ciki da ziyarar ta Janar Muhammadu Buhari, a inda ya ce “ziyarar tana da muhimmanci wajen tabbatar da kawo gyara a cikin jam’iyyar, tare da tabbatar da hadin kai a tsakanin mabiyanta a jihar.”
Sai dai Janar Buhari wanda ya isa wajen taron a cikin bakar mota kirar Jeep, bai samu sukunin fitowa daga cikin motar ba, sai dai ya fito da kansa ta tagar rufin motar, inda ya rika karbar gaisuwa, tare da daga hannunsa ga cincirindon jama’ar da suka taru, sannan ya bar wurin.

Daga cikin wadanda suka yi masa rakiya akwai Shugaban Jam’iyyar CPC na kasa Yarima Tony Momoh da dan takarar Gwamnan Kano na jam’iyyar a zaben bara Janar Lawal Ja’afaru Isah da tsohon Shugaban Majalisar Tarayya Aminu Bello Masari da Alhaji Faruk Adamu Aliyu da Alhaji Sule Yahaya Hamma da Alhaji Buba Galadima da Alhaji Nasiru Baballe Ila da Abdulmajid dan Bilki Kwamanda da Kantoman Jam’iyyar CPC na Jihar Kano Dokta Mohammed Ahmed da sauran jami’an jam’iyyar na jihar da na kasa.

Daga Jaridar Aminiya

No comments:

Post a Comment