Friday, November 9, 2012

'Yan Kasa Ne Za Su Gyara Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya

Kamar yadda mu ka sani, Majilisar Dokoki ta kasa ta na shirye - shiryen sake yin gyare - gyare ga Tsarin Mulki na Shekarar 1999.

Wannan gyare - gyare sun shafi harkokin siyasa, tattalin arziki, zaman takewa da kuma tsarin yadda a ke tafiyar da Gwamnati. A cikin shirye - shiryen gyaran Tsarin Mulkin, Majilisar Wakilai ta Tarayya ta yanke qudurin cewa gyaran da za ta yi wa Tsarin Mulkin zai sami gudunmuwa daga Jama'ar kasa ne.

A bisa wannan ne Majalisar ta fitar da cewa duk abinda za'a yi gyara a kansa sai kowanne 'Dan Majalisa ya je Maza'barsa ya tattauna da Jama'ar da ya ke wakilta don jin ra'ayinsu a kan wa'dannan abubuwa. Idan ba'a sami ha'duwar ra'ayi ba sai a yi quri'a wanda ya fi rinjaye shi ne matsayin wannan Maza'ba a kan gyaran Tsarin Mulkin.

Bayan an kammala wannan tarurruka na Maza'bu, za'a tattara sakamako a kai Majalisa wanda wannan sakamakon ra'ayin Jama'a ne Majalisar Tarayya za ta yi amfani da shi a kan abubuwan da a ke son yin gyara a kan su.

Wa'dannan tarurruka na Maza'bu an ware ranar Asabar 10 ga Nuwamba, 2012 dan yin su a fa'din qasa ba ki 'daya a lokaci guda. An fitar da sanarwa ta musamman a gidajan radiyon yankuna - yankuna da sauran kafafan ya'da labarai dangane da wa'dannan tarurruka da kuma inda za'a yi su a kowacce Maza'ba ta Tarayya. Akwai bukatar mu halacci wa'dannan tarurruka a dukkanin Maza'bunmu dan ganin cewa ba mu bari wasu sun ari bakin mu sun ci ma na albasa ba.

No comments:

Post a Comment