Tuesday, March 27, 2012

Mulkin Soja Ya Fi Na Farar Hula Cancanta Da Amfani Ga Nijeriya


MULKIN SOJA - Mulki ne da wasu daga cikin rundunar sojoji ke kwatar sa da karfin bindiga, sannan suna shimfida mulkin nasu ta yadda suka ga dama ba tare da bada damar fadin albarkacin baki ga wadanda suke mulka. Soja na gudanar da mulkin sa ba tare da kundin tsarin mulki ba, babu wakilci jama'a a cikin gwamnatinsa.

MULKI FARAR HULA - Mulki ne da jama'a ke zaben mutumin da zai jagorance su, sannan akwai damar fadin albarkacin baki, mulkin farar hula na tafiya tare da ra'ayin wadanda ake mulka. Akwai kundin tsarin mulki a mulkin, sannan da wakilan jama'a ake gudanar da mulkin.

Kasar Nijeriya wadda ta samu 'yancin kai daga turawan Burtaniya a shekarar 1960, tayi amfani da duk irin wannan tsarin mulki guda biyu, wato mulkin na soja dana farar hula.

Na dade ina yiwa kai na tambayar tun da Nijeriya tayi amfani da duk wadannan tsarukan mulki to "Shin tsakanin Mulkin Sojan dana Farar Hula wanne ya fi cancanta ga Nijeriya, kuma wanne ya fi amfanarmu a matsayinmu na 'yan kasar" amsar dana ke baiwa kai a duk lokacin dana yiwa kai na irin wannan tambayar itace "Mulkin Soja" to amma ba na gamsuwa da wannan amsa ba don komai ba sai don ban san mulkin soja sosai kamar yadda na san mulkin farar hula ba.

Wannan dalili ya sa na fara hada 'yar majalisar tattaunawa tsakanin 'yan ajinmu lokaci lokaci a makaranta, amma abin mamaki a duk karshen kowace tattaunawa sakamako na nuna Mulkin Soja ya fi cancanta, amma dai duk da haka zuciyar tawa ta taki yarda da hakan, saboda mafi yawan wadanda muke tattaunawar dasu, su ma ba su yiwa mulkin sojan kyakkyawan sani ba.

Daga karshe na yanke shawarar rubuta wannan tambaya a shafin sada zumunta na Facebook, saboda sanin wannan ce hanya kadai da zan samu gamsasshiyar amsar tambayata, domin kuwa shafin na Facebook ba irin mutanen da bai tattara ba. A yammacin ranar 27/03/2012 na rubuta wannan tambaya a shafin wannan Dandali da ke shafin na Facebook da kuma wasu majalisu na tattaunawa (Groups ) duk a shafin na Facebook, cikin abinda bai fi sa'a (awa/hour) daya ba mutane sama da 100 suka mai da martani akan wannan tambaya tawa.

A sakamakon dana tattara bayan wani dan lokaci ya nuna fiye da kaso tamanin da biyar cikin dari (85%) duk amsar da suka bada daidai ce da wadda na dade ina bawa kai na da kuma wadda 'yan ajinmu suka dade suna fada min. Wato Mulkin Soja ya fi Mulkin Farar Hula.

Dalilan da mafiya yawa daga cikin wadanda suka bayyana cewa mulkin soja ya fi na farar hula shi ne sun ce a mulkin soja an fi samun ingantaccen tsaro, ba a samun yawaitar fashi da makami, ba tashe - tashen hankula, ba tashin bama - bamai, sannan an fi samun wutar lantarki, kayan masarufi sun fi araha, rayuwa ta fi sauki ga talakawa, akwai wadataccen man fetur a gidajen mayuka akan kudi mai rahusa.

A daya bangaren kuma kasa da kaso sha da biyar (15%) din da suka bayyana cewa mulkin farar hula ya fi na soja, sun bayyana hakan ne saboda dalilin akwai damar fadin albarkacin baki a mulkin farar hula, wanda kuwa a mulkin soja babu wannan dama kwata - kwata. Har ma wani bawan Allah yake cewa ai a wannan tattaunawar da muke yi ma na daya daga cikin amfanin mulkin farar hula, wanda da mulkin soja ne bamu isa muyi hakan ba.

To a karshe koma dai taya ya ne, akwai gagarumin kalubale ga shugabannin farar hula dake jan ragamar mulkin kasar nan a halin yanzu, saboda da shugabannin farar hular suna gudanar da mulkin su kamar yadda yake a tsarin kundin mulkin kasar nan to da na san ko kusa ko alama mutane ba zasu ke bayyana cewa mulkin soja ya fi na farar hula cancanta da amfanarsu ba.

Bashir Ahmad
bashirgy@yahoo.com
08032493020

Saturday, March 24, 2012

Abinda Ya Faru A Kasar Mali Zai Iya Faruwa A Nijeriya - Nasir El-Rufai


Tsohon ministan birnin tarayya Abuja, kuma daya daga cikin manya a jam'iyyar CPC Malam Nasir El Rufai ya bayyana cewa abinda ya faru a kasar Mali zai iya faru a kasar idan shugabanni suka ci gaba da shimfida mulki zalunci ga talakawan da suka zabe su.

El Rufai ya bayyana hakan ne a turakarsa dake shafin bayyana ra'ayi na Twitter, inda wani daga cikin mabiyansa (followers) yayi masa tambayar "Shin yana tunanin abinda ya faru a kasar Mali zai iya faruwa a kasar nan idan shugabanni basu kula da bukatun talakawan da suka zabe su ba?" nan take Malam Nasir El Rufai ya maida masa da amsar cewa yana tunanin hakan zai iya faruwa.

Idan ba'a manta ba a ranar Laraba da ta gabata ne sojoji suka yi juyin mulki a kasar ta Mali, kasar da aka shafe tsawon lokaci ana yakin basasa.

A karshe ya kamata hukumomin Nijeriya su yi duba ga irin halin da talakawan da suka zabe su, suke ciki domin kaucewa hasashen na Malam Nasir El Rufai.

Malam Nasir El Rufai a kullum yana ware lokaci domin tattaunawa da jama'a akan matsalolin da suke fuskantar kasar nan a turakarsa ta Twitter. Za ka iya biyo shi akan @elrufai domin samun damar bayyana ra'ayinka tare da shi.

Wednesday, March 21, 2012

Lionel Messi Ne Da Wasan Kwallon Kafa Da Ya Fi Kowane Dan Wasa Samun Kudin Shiga A Duniya


Lionel Messi dan kasar Argentina, mai takawa kungiyar Barcelona ta kasar Spain leda, shi ne dan wasan kwallon kafa da yafi kowane dan wasa samun kudin shiga a duniya. Messi yana samun €33m a duk shekara.

Ga jerin 'yan wasa goma da suka fi samun kudin shiga a duniya.

1. Lionel Messi - Barcelona - Argentina - €33m.

2. David Beckham - LA Galaxy - England - €31.5m.

3. Cristiano Ronaldo - Real Madrid - Portugal - €29.2m.

4. Samuel Eto'o - Anzhi Makhachkala - Cameroon - €23.3m.

5. Wayne Rooney - Manchester United - England - €20.6m.

6. Sergio Aguero - Manchester / Argentina - €18.8m.

7. Yaya Toure - Manchester City / Ivory Cost - €17.6m.

8. Fernando Torres - Chelsea / Spain - €16.7m.

9. Ricardo Kaká - Real Madrid / Brazil - €15.5m.

10. Philipp Lahm - Bayern Munich / Germany - €14.3m.

Tuesday, March 20, 2012

Mun Rufe Kofar Tattaunawa Da Gwamnati - Boko Haram


Kungiyar jama'atu Ahlussunah
lidda'awati wal jihad da aka fi sani
da suna, Boko Haram a Najeriya, ta
ce a yanzu ta rufe kofar duk wata
tattaunawa da gwamnatin kasar
domin a ganinsu ba da gaske
gwamnatin take ba.

Kungiyar ta kuma tabbatar da cewa,
da yawunta majalisar kula da
al'amuran shari'a a Najeriya ta fara
tattaunawa da gwamnatin Najeriya,
tattaunawar da ta rushe a karshen
makon da ya gabata.

Wani dake ikirarin magana da
yawun kungiyar da ake wa lakabi
da Abu Qaqa ne ya bayyana haka a
hira da manema labarai a birnin
Maiduguri.

Mai magana da yawun kungiyar ta
Boko Haram ya ce sun ga ya wajaba
ne su yi wannan karin bayani, ganin
cewa batun tattauanawar su da
gwamnatin tarayya ya mamaye
kafofin yada labarai a 'yan
kwanakin nan.

Abu Qaqa ya ce, sun amsa kiran da
Dr Datti Ahmad, shugaban majalisar
kula da al'amuran shari'ar Musulunci
a Najeriya ya yi musu na a tattauna
ne, saboda suna ganin kimar sa,
amma tun asali suna da shakku
akan ko da gaske gwamnati take
kan batun tattaunawar.

Mai magana da yawun kungiyar
Boko Haram din ya ce, ba da jimawa
bane shugaban Najeriya Goodluck
Jonathan ya yi kira ga kungiyarsu
da ta fito a tattauna da su, su kuma
bayyana bukatunsu, bukatun da ya
ce sun bayyana wadanda suka
kunshi sako musu dukkan 'yan
kungiyar su da aka kama ba tare da
gindaya wani sharadi ba.

''ABIN KAICO NE''

Ya ce an fara ganawa tsakaninsu da
gwamnati, amma gwamnati ta sa
aka kama daya daga cikin 'ya'yan
kungiyar Abu Darda wanda suka
tura ya wakilce su.

Kuma tun daga lokacin suka ga
cewa ba za su iya sake amincewa
da gwmanatin Najeriya ba.

Sai dai sakamakon rokonsu da wasu
muhimman 'yan Najeriya da suke
matukar girmamawa suka yi, sun
amince su tattauna, amma abin
kaico ne ganin an bata shirin tun bai
je ko ina ba.

A don haka Abu Qaqa ya ce ba za su
kara saurarar duk wasu da suka ce
su zo su sasanta su da gwamnati ba,
don haka jami'an tsaron gwamnati
su yi duk abinda suka ga za su iya,
su ma za su maida martani da tasu
iyawar.

Dangane da wani dan jarida da ya
yi ikirarin ana barazana ga rayuwar
sa kuwa, mai magana da yawun
kungiyar ta Boko haram ya ce, dan
jaridar shi ne silar hada su da
kwamitin Dr Datti Ahmed, a don
haka suna shawartarsa da sauran
'yan jaridu da kada su razana da
duk wata barzana.

A karshen makon da ya gabata ne
shugaban Majalisar kula da
al'amuran shari'ar musulunci a
Najeriya Dr Datti Ahmad ya fitar da
wata sanarwar da a cikinta ya ce ya
janye daga tattaunawar da suke
kokarin kullawa tsakanin gwamnati
da kungiyar Boko Haram, saboda in
ji shi, suna zargin bangaren
gwamnati da tseguntawa 'yan
jaridu batutuwan da ake tattaunawa
cikin sirri.

Daga shafin BBC Hausa

Monday, March 19, 2012

Shin Idan Kai Ne Shugaban Nijeriya Taya Za Ka Tafiyar Da Mulkin Kasar Yadda Zaiyi Daidai Da Bukatun Talakawa?


Nijeriya na daya daga cikin kasashen wannan duniya, wadda Allah ya bawa matsuguni a yankin yammacin nahiyar Afrika, kasar na da al'umma mai tarun yawa sama da 160 miliyan. Allah ya horewa kasar yalwar arziki kala - kala, ciki har da man fetur mai matukar daraja.

Kamar sauran kasashe Nijeriya tayi shugabanni daban - daban wasu daga cikin su turawa ne, a lokacin mulkin mallaka daga kasar Burtaniya, wasu sojoji ne da suka kwaci mulkin da karfin bindiga, wasu kuma fararen hula ne da talakawa suka zabe su ta hanyar kada kuri'a.

Duk yawan shugabannin da kasar Nijeriya tayi amma har yanzu talakawan kasar basu yi sa'ar samun wanda ya fitar dasu daga cikin kangin wahalhalun rayuwar da mafiya yawa daga cikinsu ke fuskanta ba. Duk lokacin da aka samu canjin shugaba a kasar, sai kaga talakawa na ta murna da yiwa juna barka, sai dai kash! Tun kafin tafiya tayi nisa sai kaga ana fadin ai kwara na jiya dana yau, kuma kullum haka abin yake babu canji, ko mai ya kawo hakan? Amsa ita ce OHO!

To TAMBAYA anan ita ce "Shin idan kai ne shugaban na Nijeriya ya zaka bullowa al'amarin, ya zaka tafiyar da mulkin kasar yadda zai yi daidai da bukatun talakawan kasar?"

Bukatun talakawan Nijeriya, ba abubuwa ne boyayyu ba, a fili suke wanda duk shugaban da yazo da kokon bararsa kafin talakawa su zabe shi, da su yake jan hankalinsu da tabbatar da cewa da zarar an zabe shi ya dare karagar mulkin kasar, ta kansu zai fara. Amma da zarar talakawan sun zabe shi sai ya kasa tabbatar da koda alkawari daya daga cikin wanda ya dauka, yayi fatali da bukatun talakawan har sai maganar tazarce ta taso.

Bukatun talakawan Nijeriya sune: Samarwa 'yan kasa aikin yi, samar da wutar lantarki, kyautata harkar noma, kawo gyara a bangaren ilmi, samar da hanyoyin sufuri masu inganci, samar da wadatattun magani a bangaren lafiya, samar da tsaro a kowane bangare, samar da wadataccen man fetur a farashi mai rahusa, samar da ruwan sha mai tsafta birni da karkara, saukake harkokin rayuwa ga talakawa, dawo da TALLAFIN MAN FETUR.

Bana tunanin akwai wasu abubuwa da talakawan Nijeriya ke bukata a wuraren jagororin kasar sama da wadannan, amma shekaru aru - aru, an kasa samun shugaba guda daya da zai bugi kirji ya samarwa talakawan Nijeriya koda daya daga cikin bukatun nasu.

Ya Allah ka kawo mana shugaban da zai dubi wadannan bukatu namu kuma ya yi mana maganinsu.

Domin bada amsa ziyarci shafin wannan Dandali a Facebook. facebook.com/dandalinbashirahmad

Saturday, March 17, 2012

Tattaunawar Sulhu Tsakanin Boko Haram Da Gwamnati Taci Tura


A Najeriya, shugaban Majalisar koli ta shari'ar Musulunci ya ce sun janye daga tattaunawar sulhu da suka fara gudanarwa da jami'an gwamnatin kasar da kuma 'yan kungiyar nan ta Jama'atu Ahlis Sunnati Lidda Awati wal Jihad, da aka fi sani da Boko Haram.

A wata sanarwa daya fitar, shugaban Majalisar koli ta shari'ar Musulunci Dr. Ibrahim Datti Ahmad ya ce shi da sakataren majalisar sun yanke shawarar janyewa daga tattaunawar ce saboda sun ga alamar cewa jami'an gwamnatin kasar bada gaske suke ba a tattaunawar da aka fara yi da shugabannin kungiyar ta Boko Haram.

Shugaban Majalisar kolin ya kuma bayyana takaicinsa da yadda bangaren gwamnatin kasar ta ki amfani da wannan damar na baiwa tattaunawr sulhun muhimmanci wanda zai kaiga kawo karshen tashe tashen hankulan da ake fama dasu a kasar.

Sanarwar dai tace ganin irin yadda ake ta fuskantar matsalar tashe tashen hankula a kasar musumman ma a arewacin Najeriyar ne, yasa shugabannin majalisar kolin suka fara lalubo hanyoyin da zasu kaiga kawo karshen tashe tashen hankulan, wadanda ake dangantawa da kungiyar Boko Haram.

Sanarwar ta kara da cewa bayan da 'yan Majalisar koli ta shari'ar Musuluncin suka gudanar da bincike ne, suka gano wani dan jarida a kasar wanda kuma suka tabbatar cewa, ya kan tattauna da shugabannin kungiyar Boko Haram wajen gudanar da ayyukansa a matsayin dan jarida, hakan yasa suka yi amfani da dan jaridar wajen mika sakon neman sulhu ga 'yan kungiyar.

Shugaban Majalisar koli ta shari'ar Musulunci ya kara da cewa, a ranar 5 ga wannan watan ne shi da sakataren Majalisar a madadin sauran mambobin Majalisar kolin, suka tuntubi jami'an gwamnatin kasar don gabatar musu da shawarwarin fara tattaunawa da 'yan kungiyar ta Boko Haram.

To sai dai a cewar sanarwar, bayan da gwamnatin kasar ta umurci wani babban jami'inta ya kasance wakili a tattaunawar tsakanin shugabannin Majalisar kolin da kuma 'yan kungiyar ta Boko Haram, duk wasu batutuwa na sirri da bangarorin suka tattauna da jami'in gwamnati, sai kwatsam suka yaddu a jaridun kasar, abin da cewar Dr Ibrahim Datti Ahmed, shugaban Majalisar koli ta shari'ar Musuluncin, hakan yasa suka fara shakkun cewa ko anya kuwa da gaske gwamnatin kasar take na tattaunawar.

Sai dai wata majiya daga bangaren shugabannin Majalisar kolin ta shari'ar musuluncin tace janyewar da shugabannin Majalisar suka yi a tattaunawar bai rasa nasaba ne da abin da suka fassara a matsayin rashin bada muhimmanci ga tattaunawar daga bangaren gwamnatin kasar, sabannin tattaunawar da a baya gwamnatin Najeriyar ta yi da 'yan kungiyar MENDS masu fafutika a yankin Neja Delta, wadanda a cewar majiyar takanas, gwamnati kan bada jirgin sama a dauko jami'an kungiyar ta MEND zuwa fadar shugaban kasar inda aka tattauna dasu.

BBC tayi kokarin jin martanin gwamnatin Najeriyar kan wannan batu inda an tuntunbi kakakin shugabar kasar Dr Ruben Agbati ta wayar tarho amma bai amsa ba.

Ko a baya lokacin da shugaban Najeriyar Goodluck Jonathan yayi kira da 'yan kungiyar dasu fito su bayyana kansu tare da fayyace bukatunsu domin a tattaunawa da su amma 'yan kungiyar sun yi watsi da kiran saboda a cewarsu, a baya sun turo wani jami'in kungiyar don ya tattauna da jami'an gwamnati, amma aka kame shi.

Daga BBC Hausa

Thursday, March 15, 2012

Na Duke Tsohon Ciniki - Da Arzikin Noman Mutanen Arewa Aka Samar Da Man Fetur A Nigeria


Idan muka dubi can baya lokacin da kasar nan bata da man fetur (fuel) ko nace kafin a tono man fetur, an dauki yankin AREWA da matukar muhimmanci, musamman a wurin shugabannin kasar nan na wancan lokacin. Ba don komai ba sai don da arzikin noman dake yankin ke samarwa kasar NIGERIA ta ke gudanar da komai, da wannan noma ake samun duk wani kudin shi, kai a lokacin Nigeria ta dogara baki daya, da wannan arziki na noma. A wannan lokaci ba rigingimu a Arewa ba BOKO H.... Kan duk wani dan Arewa a hade yake, ba a lakari da addini ko kabila, kowa ya dauki kowa a matsayin dan uwa.

Da wannan arzikin na noma aka yi duk wani wahalhalu na hako man fetur din da muke amfana a yanzu, da shi aka biya ma'aikatan da sukayi wannan gagarumin aiki.
Da shi aka gina matatan man fetur din da muke da su.

Amma wani abin mamaki sai ga shi a wannan lokaci yankin AREWA ne yafi kowanne yanki kaskanci da koma baya a kasar nan, har ma a wani kiyasi da akayi kwanan nan wai yankin ne yafi kowanne TALAUCI da FATARA, saboda yanzu an samu man fetur an yarda noma, an dauki MANOMA wawaye wadanda basu san mai suke yi ba, an dauke su a matsayin jahilai da basu waye ba. Gwamnatin a wancan lokaci tana tattalin Manoma tana samar musu da ingantattu kayan noma kamar su: motocin noma, iri, maganin kwari, takin za
mani da sauransu.

A karshe fatan za muyi karatun ta nutsu don samarwa rayuwarmu da ta 'yayanmu da zamu haifa nan gaba mafita.

Ya Allah ya taimaki AREWA da jama'ar AREWA, Ya Allah ya taimaki NIGERIA.

Bashir Ahmad
Bashahmad29@yahoo.com
08032493020, 08050600160

Wednesday, March 14, 2012

Wasu Saurari da Budurwa Masoyan Juna Sun Mutu a Lokaci Daya a Cikin Mota


ABIN AL'AJABI - Da sanyin safiyar ranar 14 March, 2012 ne wani abin al'ajabi ya faru a yankin unguwar Kundila dake cikin kwaryar birnin Kano. An samu gawar wasu bayin Allah su biyu, Abubakar Abba da Ummulkhair Muhammad, saurari da budurwa a cikin karamar mota kiran Peugeot 406, mallakin saurayin Abubakar Abba.

Matasan guda biyu, wadanda aka bayyana cewa dukkansu dalibai ne, dake karatu a makarantar Kwalejin Sa'adatu Abubakar Rimi, sannan dukkansu suna kan ganiyar samartakarsu da basu wuce shekaru 25 ba. Kuma sun dade suna son juna, wanda har iyayensu sun shiga maganar soyayyar tasu.

ASP Magaji Majiya, jami'in hulda da Jama'a na hukumar 'yan sandan jihar Kano, ya tabbatar da faruwar wannan al'amari, kuma yace har yanzu ba'a san menene musabbabin rasuwar matasan ba. Sannan ya bayyana cewa a halin yanzu hukumar 'yan sanda tana kan bincike.

Ya Allah ya jikan wadannan MATASA masoyan juna, ya kai rahma kabarinsu.

Jama'a Ga Jaridar RARIYA Matatar Gaskiya, Domin Samar Da Labaran Gaskiya


Aminci a gare ku! Ya ku al'ummar kasar Nijeriya, musamman Hausawa da kuma masu amfani da harshen. Cike da farin ciki da annashuwa nake gabatar muku da sabuwar jarida mai suna RARIYA wadda ake yi wa lakabi da MATATAR GASKIYA.

Wannan jarida sabuwar fitowa ce da aka samar domin al'umma, kuma zahiri jaridar ta zo a daidai lokacin da al'umma ke bukatarta, ba don komai ba sai don yadda al'amura a kullum suke kara cabewa gami da dagulewa musamman a harkokin yada labarai, sanin kowa ne mafi yawa daga cikin jaridun wannan zamani ba kawo sahihin labarai ne ya dame su ba, abin da suka fi mai da hankali shi ne wane labarai zasu kawowa makaranta ya samu karbuwa su samu riba mai yawa, ko da kuwa ba su da tabbacin sahihancin gaskiyar labarin.

RARIYA ta zo da salo ne na daban da ya sabawa irin na wadannan jaridu na zamani, wannan dalili ya sa ta samu lakabin MATATAR GASKIYA, kafin ta kawowa masu karatu labari sai ta bi diddiginsa sannan ta tato gaskiyarsa ta bayyanawa al'umma. Samuwar RARIYA zai zame wa masu karatu wata wukar gindi, sannan RARIYA ta yi alwashin kawo labaran da zasu inganta rayuwar al'umma, cikin hanya mafi dacewa da yanayin rayuwar zamani. Tabbas RARIYA ta samu ne bisa kishin kasarmu da al'ummarmu a matsayin wata jagora da zata nuna mana mafi ingancin rayuwa tagari abar alfahari.

Jaridar RARIYA na kunshe da bangari daban - daban masu Ilimintarwa, Fadakarwa, Wa'azantarwa, har ma da nishadantarwa. Kadan daga cikin wadannan bangarori sun hada da:

NIJERIYARMU A YAU - wannan bangare ne da yake dauke da muhimman labarai da suka shafi kasar nan baki daya.

MU KEWAYA JIHOHI - daga jin sunan bangaren ba bukatar dogon bayani, bangaren na lekawa jihohin kasar nan 36 da birnin tarayya Abuja, domin zakulowa masu karatu sahihan labarai masu inganci.

DUNIYA LABARI - A wannan bangaren kuma labarai ne kala - kala daga sassan duniya daban - daban, domin sanin wainar da ake toyawa.

BABBAN BAKO - A wannan bangare RARIYA na kurdawa cikin kasar nan ta lalubo wani babban bako masani, domin yin fashin baki akan wasu al'amura da zasu amfani masu karatu da sauran al'ummar kasa baki daya.

KULIYA MANTA SABO - Nan kuma bangare ne daya shafi harkokin shari'ah, domin kawowa masu karatu ingantattun labarai daga bangaren na Shari'ah.

SHAFA LABARI SHUNI - Shafin na kawo labarai na nishadantarwa da fadakarwa, wanda masu karatu ke aikowa da kansu, domin daukar wani darasi.

TASKAR FIM - Bangare ne a cikin jaridar dake kawowa makaranta irin wainar da ake toyawa a masana'antar fina-finan Hausa har ma da takwarorinsu na kudanci kasar nan (Nollywood) dama na sauran kasashen duniya irin su Amurka da India.

YABON GWANI - Bangaren na kawowa masu karatu tarihin wani kwazo, haziki kuma gwani a wani bangare na rayuwa, da irin gudunmawar da ya bawa al'umma.

SIYASA ROMON BAKA - Wannan bangaren kuma dandali ne na 'yan siyasa da magoya bayansu, shafin ya kunshi duk wani batutuwa da suka danganci siyasa.

LIKITA BOKAN TURAI - Nan kuma bangare ne da aka ware domin kiwon lafiya, da bada shawarwari ga makaranta ta yadda zasu kare kawunansu daga cututtuka.

TABA KA LASHE - Bangare ne da Amina Galadanci ke tsakurowa masu karatu dadaden labari daga litattafan Hausa kala - kala na da dana zamani.

WASANNI - Bangare ne domin matasan zamani, bangaren na kawo labarai ne game da wasanni kala - kala musamman a fannin kwallon kafa a ciki da wajen kasar nan.

To wannan kadan kenan daga cikin bangarorin da wannan jarida ta RARIYA ta kunsa, amma fa kamar yadda na fada ba duk bangarorin na bayyana ba, kadan daga ciki na bayyana, akwai bangarori da dama da ban bayyana ba irin su: Ra'ayin Rariya, Kowa Ya Debo Da Zafi, Allah Daya Gari Bambam, Jiya Ba Yau Ba, Tafarki Madaidaici, Tallata Hajarka, Adon Gari, 'Yar Kwalisa, Ma'aunin Hankali, Ciki Da Gaskiya, Daga Majalisar Tarayya, Hangen Nesa, Cinikayya, Asan Mutum, Girkinki Sirrinki, Sakonnin Masu Karatu da kuma GYARAN GANGAR AZBINAWA wanda babban edita da kansa wato Ashafa M. Barkiya yake gabatar da bangaren, inda yake yin tsokaci game da al'amuran da suka shafi siyasar kasar nan dama duniya baki daya.

Kai amma da yawan mantuwa nake, tunda na fara wannan rubutu nake son yin bayani akan wani bangare saya fi kowane daukar hankali na kuma na san ku ma shafin zai dauki hankalinku kuma ya burge ku, amma ban tuna ba sai da ruwan alkalamin da nake wannan rubutu yazo daf da karewa, hakan tasa idan na fara bayanin bangaren ba zan kai karshe ba ragowar ruwan rubutun zai karasa, kuma nasan ba za ku ji dadin hakan ba, saboda haka bari na bada satar amsar shafin, shafin yana kusa da shafin tsakiya, kuma shafin yana daya daga cikin shafukan da aka fi kawatawa, kai bari dai na dakata anan, domin ganewa idonka abin da shafin ke kunshe da shi yi saurin mallakar taka kwafin jaridar RARIYA, hakan zai baka damar fahimtar sauran abubuwa sama yadda zan yi muku bayani, har ma ku ma ku samu damar bawa wasu labari.

A karshe kamfanin RARIYA MEDIA SERVICES LTD. Shi ne yake daukar nauyin tsarawa da buga wannan jarida a kowane sati biyu a karkashin jagorancin Alhaji Dr. Aliyu Modibbo Ph.D, domin karin bayani za'a iya tuntubar hukumar gudanarwar kamfanin dake lamba 7, titin Thaba - Tseka, kusa da British Village, Wuse II, Abuja ko lambobin waya: 09-8701707, 09-8701708, 08034269830 email: rariyajarida@yahoo.com

Monday, March 12, 2012

Shin Wai Za'a Rufe Shafin Sada Zumunta na Facebook?


Shin yaushe za'a rufe shafin Facebook? Shin wai za'a rufe shafin Facebook? Ranar 15 March, 2012 shafin Facebook zai daina aiki. Zan koma 2go ko Twitter idan aka rufe Facebook. Abokaina na yafe muka, zan koma 2go tunda za'a rufe shafin Facebook. Wannan kadan kenan daga cikin irin rubututtukan da na rinka cin karo da su a shafin sada zumunta na Facebook, wasu kuma kai tsaye suka kira ni a waya suna tambayata gaskiyar lamari akan maganar rufe shafin na Facebook.

Wannan dalili yasa na shiga binciken gano gaskiyar al'amarin. Abinda ya bani mamaki shi ne wannan jita - jita an yada ta ne tun shekarar da ta wuce a watan January 2011, sai ga shi an dawo da ita a wannan shekara ta 2012.

FARKON AL'AMARI - A ranar 9 January, 2011 wata jarida mai suna Weekly World News dake kasar America, ta buga wata mukala a shafinta na Yanar Gizo (Internet) dauke da cewa "Za a Rufe Shafin Sada Zumunta Na Facebook ranar 15 March, 2011" a cikin mukalar an bayyana dalilan da zasu sa a rufe shafin kamar haka: Mark Zurkerberg shugaban kamfani kuma wanda ya kirkiro shafin ya bayyana cewa shafin ya fi karfin hankalinsa, ya kuma ruguza masa rayuwarsa, saboda haka yana so rayuwarsa ta dawo kamar yadda take a da kafin bude shafin na Facebook. Sannan Mark Zuckerberg ya kara da cewa shafin Facebook ya shagaltar da mutane inda ba sa iya yin abokanai ko kawaye a zahiri sai dai a shafukan Yanar Gizo, saboda haka duk wanda ya ajiye hotunansa a ma'ajiyar hotuna (Album) a shafin na Facebook yayi kokarin canja musu ma'ajiya kafin ranar 15 March, 2012 daga ranar mutum ba zai sake ganinsu ba.

Wannan kadan kenan daga cikin dalilan da jaridar ta Weekly World News ta bayyana zai sa a rufe shafin na Facebook, a wannan lokacin wannan mukala ta tada hankulan jama'a musamman wadanda suka sadaukar da lokutansu ga shafin na Facebook (Facebook addicted).

Ana cikin wannan hali ne sai gidan television na CNN ya yi rahoto na musamman akan jita - jitar, wanda suka bayyana cewa sun samu cikakken bayani daga hukumar gudanarwar kamfani na Facebook dake tabbatar da labarin da jaridar Weekly World News ta buga karya ce tsagwaranta.

A tsakiyar wannan sati ranar 13 January, 2011 shafin Facebook ya fito da sanarwa ta musamman akan cewa ba gaskiya ba ne, maganar cewa za a rufe shafin, kuma suka tabbatar da cewa babu wani dalili da zai sa a rufe shafin har abada.

Wannan suna kadan daga abubuwan da suka faru a shekarar da ta gabata, sai kuma wannan shekarar ma aka sake dawo da jita - jitar, wadda wasu ke kwafo abubuwa da suka faru a shekarar da ta gabata suna yadawa.

A karshe gaskiyar al'amari akan wannan magana ta rufe shafin na Facebook ba gaskiya ba ce. Idan bamu manta ba a watannin baya da suka gabata kadan shafin na Facebook ya saka lallar hajojin kamfanin a kasuwa. Sannan a watan December na 2011 aka bayyana shafin Facebook a matsayin na biyu a duniya wurin samun maziyarta a kullum bayan shafin bincike na Google.

Ziyarci Dandalin Bashir Ahmad a shafin Facebook (http://facebook.com/dandalinbashirahmad)

Bashir Ahmad
bashahmad29@yahoo.com
08032493020

Friday, March 2, 2012

Shafin Dandalin Bashir Ahmad ya Samu Wuri a Duniyar Facebook


Aminci a gare ku! Tare da albishir a gare ku masoya da makaranta wannan Dandali, Ina mai farin cikin gabatar muku da shafin wannan dandali a shafin sada zumunta na Facebook, mai suna DANDALIN BASHIR AHMAD wanda za'a iya samu kai tsaye akan http://facebook.com/dandalinbashirahmad duk da har yanzu ban kammala tsara shafin ba, na sanar da kune domin abin naku ne, don ku aka kirkire shi, fatan zaku so shi kamar yadda kuka so wannan Dandali.

Dalilina na budewa wannan dandali a Facebook shi ne domin samun wani wuri da makaranta dandalin za suke baje kolinsu, kuma nayi hakan ne saboda amfani da shawarar da wasu daga cikin ku makaranta suka ba ni.

Sannan shafin zai kasance wurin bani shawara ta kai tsaye kamar yadda kullum nake maraba ta kowace irin shawara daga wurinku.

A karshe ina godiya da kulawarku a gare ni a koda yaushe, musamman wadanda suke kira na a waya ko aiko min da sakonni. Allah ya bar zumunci.