Sunday, February 22, 2015

GARABASA DAGA mACADEMY

Ilimintar da kanka, bunkasa takardun kwarewarka (CV) sannan ka samu damar cin kyauta.

mAcademy, wata hanyar koyo ce ta hanyar amfani da wayoyin hannu, mAcademy na bada damar koyar samu da darussa 150 kuma mafi yawancin su duk a kyauta. Burin wannan makaranta ne su ilimintar da al'umma musamman marasa galihu, tana da hadin guiwa da kamfanin sadarwa na MTN da kafar yada labarai ta Sahara Reporters, sannan nan gaba kadan da yardar Allah, za ta kulla dangantaka da wannan kafar yada labarai #HAUSA24.

mAcademy, tana bada damar koyo cikin yarukan Turanci, Larabci da kuma Hausa, tana ayyukan ta a sama da kasashe biyar a nahiyar Afrika.

Aika ACADEMY zuwa 131 ko duba wannan hoton don ganin yadda za ku shiga gasar, da yadda za a fitar da wadanda suka yi nasara, ba wannan ce gasa ta farko da mAcademy din ta saka ba, a baya ta sa irin wannan gasa kuma mutane da dama sun samu nasara.

Cancantar shiga gasar:

- Idan kana daya daga cikin wadanda suka taba lashe kyauta daga mAcademy watanni shida baya, ba zaka iya shiga gasar a wannan lokaci ba, jira wani lokacin nan gaba.

- Idan ka shiga gasar, ya zama dole ka aika/raba rubutun shiga gasar zuwa ga sauran abokanka daga shafin Facebook na mAcademy (www.facebook.com/bilyak).

- Gasar za ta kare ranar 13, ga watan Maris, 2015.

...Ka shirya? Shiga gasar yanzu don gwada sa'arka.

HAUSA24 za ta yi alfahari idan aka samu daya daga cikin makarantan ta ya lashe gasar, muna yi muku fatan alheri.

A LURA CEWA: Kamfanin Bilyak Consulting Limited ne ya dauki nauyin gasar ba MTN ba.

Tuesday, February 10, 2015

HOTO: Sarkin Kano, Sanusi Da Iyalansa



Sarkin Kano, Alhaji Muhammadu Sanusi II, tare da matansa uku da 'yaya 12. Wannan shi ne hoto na farko da Sarkin ya dauka da iyalansa baki daya, tun baya bikin bashi sandar girma da ya gudana a ranar Asabar 7 ga Fabrairu, 2015.

Allah ya taya Mai Martaba riko!

Thursday, February 5, 2015

AREWA MUN FARKA DAGA BACCI: Jonathan Ya Sa Mun Fara Hada Kan Mu

Masha Allah, yanzu kam zan iya cewa watakila Arewa mun farka daga dogon baccin da muka dade muna yi.

Sakamakon zaman majalisar zartarwa na kasa da aka kammala dazu ya kara min karfin guiwa kan lalle Arewa wannan karon da gaske muke yi.

Kamar yadda wani da yake da masaniyar yadda zaman majalisar ya gudana yake shaida min a waya yanzu, ya ce bayan Jega ya tashi yayi jawabinsa a gaban majalisar, inda ya bayyana cewa INEC ta shirya gudanar da zabe a ranakun 14 da 28 na watan nan, gwamnatin tarayya da 'yan kanzaginta sun nemi kin amincewa da hakan, sai dai gwamnonin APC su 14 da suka halarci taron, da Janar Buhari da kuma Hon. Aminu Tambuwal duk sun goyi bayan maganar ta Jega.

Haka kuma wasu daga cikin gwamnonin PDP daga yankin Arewa su ma sun nuna goyon bayan su ga Jegan, abinda ba a yi tsammanin hakan daga wurin su ba.

Da na nemi ya fada min wadanne gwamnoni ne daga Arewa sai yace na bari na karanta a jarida idan labarin ya fita, amma akwai gwamnan jihar J... da kuma B... haka kawai ya fada min bai karasa min sunan ba.

Yanzu dai zabe zai gudana a ranar 14 da 28, zabi ya rage gare mu, ya zama dole mu fita mu karbi katin zaben mu na dindindin don zaben shugabannin da muke gani za su yi mana abinda za mu zabe su don su.

...Ni dai na yake shawara tuntuni, a zaben shugaban kasa, Janar Muhammadu Buhari, na jam'iyyar APC zan zaba kamar yadda na saba, zabensa tun daga 2003.