Tuesday, September 11, 2012

Hukuncin Wanda Yayi Kisan Kai Bisa Gangaci: Sheikh Ja'afar Mahmud Adam


Ya yan uwa musulmi, yana daga cikin manufofin shari'ar musulunci tsare rayukan bil'adama tsare jinin su, don haka ne nassoshi suka zo acikin alkurani mai girma da abin da ya inganta na hadisan manzon Allah salallahu alaihi wasallam, wadan da suke nuna haramcin jinin bil'adama mu samman dan adam musulmi.

Ubangiji ta'ala ya yi wannan bayani ta hanyar salon zance da ban da ban, ta hanyar nau'ikan magana da ban da ban, Salon zan ce na farko. Ubangiji ta'ala ya wajabta kisasi (ramuwar gayya) ga dukkan wanda ya kashe musulmi da ganganci, hukuncin sa shi ne a kashe shi, dukkan wani mutum da ya kashe musulmi da ganganci ya yi amfani da wani abu wanda ya iya zare rai, ya nufi dan uwan sa musulmi ya aiwatar da wannan makamin akan sa har ya kashe shi, to shi ma akamashi a kashe shi ko shi kadai ne, ko su da yawa ne, sai dai fa idan dangin wanda aka kashe musu dan uwan su suka ce sun yafe, zasu karbi diyya, to sai a basu diyya.

To amma idan ba hakaba hukuncin su da Ubangiji Ta'ala ya nassanta shi ne kisasi, ko da mutum daya ne, ko biyu, ko uku, ko sama da haka, sukayi taron dangi suka kashe mutum daya, kuma hakan ya tabbata, ta hanyara tabbatar da laifi a addinance, a musulunce, hukuncin su shi ne akamasu a kashe su gaba dayan su; Kamar yadda aikin Umar bin Khaddab ya nuna lokacin da wani adadi na wasu mutane suka yi taron dangi suka kashe wani mutum daya su kadai, Umar ya ce a kashesu su duka, wadansu suka yi masa inkari da cewa ya ya za a yi ace a kashe rayuka da dama bayan rai daya suka kashe, Umar ya ce wallahi inda mutanan birnin san'a za su hadu su kashe rai daya to wallahi da na kashe su gaba daya.

Hikimar hakan cikin shari'ar musulunci, shi ne in da ace ana yin kisasi ne kadai idan mutum ya kashe mutum daya za'a kashe shi, sai wanda zai yi kisan ya raba goran gayyata ga abokansa, ko yan uwansa, su je, su kashe wane, don sun san insunyi baza a kashe suba, gobe kai ma idan kana jin hashin wani sai karaba goran gayyata ga wadan da zasu taya ka fada domin kuje ku kashe wane. Wannan sai ya bayu zuwa ga hasarar rayuka, amma idan mutum biyu ko uku ko sama da haka sukayi haka aka kashe su,wannan zai sa dukkan wani da da wani ya rabawa goron gayyata cewa zaka rakani in kashe wane to bazai je ba saboda yasan idan ya aikata hakan to zai bayu zuwaga akashe shi, don haka sai rayukan mutane su zauna cikin aminci. Allah ta'ala yana cewa "lallai kuna da tabbatacciyar rayuwa a cikin kisasi matukar an tabbatar da kisasi a bankasa, wanda duk ya kashe wani da ganganci da kowanne irin dalili cikin dalilai to shi ma za'a kama shi a kashe shi" to wannan sai ya bayu zuwa ga tsare rayukan mutane, kisa ba zai yaduba a bankasa da kowanne irin dalili cikin dalilai. wannan salon magan na farko kenan.

Salon magana na biyu, Ubangiji Ta'ala ya saukar da narkon azaba da firgitarwa da rudarwa da kidimarwa ga dukkan mutumin da ya kashe mumini da ganganci yana ji yana gani sakamakon sa wutar jahannama, zai dawwama a cikin ta ubangiji ta'ala ya yi fushi da shi, ya tsine mashi, sannan yayi masa tanadin azaba maigirma. kaji irin wannan firgici, ka ji irin wannan razani, ka ji irin wannan tsawa, da ya sauka cikin suratul Nisa'i domin aja hankalinka aja hankalina kada kayi dukkan wani yunkuri na zubar da jinin dan uwanka musulmi bisa ganganci.

Salon magana na uku, Ubangiji Ta'ala ya nuna cewa duk wanda ya kashe mumini da ganganci, to baya cikin siffofin muminai nagari, wadan da ubangiji ta'ala ya jero siffofin su a cikin suratul furqan a inda Allah ta'ala yace "sune wadan da basa kiran wani tare da Allah, suna kiran Allah ne kadai dan jawo amfani ko dan ko dan dauke musu wata cuta, sannan ba sa kashe wata rai da Allah ya haramta kisan ta sai ta hanyar gaskiya da adalci”. Sannan kuma cewa mumini baya kisan kai, wannan dalili ne da yake nuna cewa idan kuna son kalmar adalci ta tabbata a kanku to kuyi iyakar kokarinku na tsare jinin yan uwan ku musulmi.

Sannan salon magana na gaba, Ubangiji ta'ala ya danka amana ko ya bayara da iko a hannu wadan da aka kashe wa dan uwa da ganganci, dangin duk wanda aka kashe bisa ganganci. Haka ya ce ya basu iko duk wanda aka kashe bisa ganganci ya bada dama ga yan uwan sa, a hannun dangin sa ko makusantan sa, wannan iko kodai su nemi a basu diyya, ko su nemi a kashe wanda da ya kashe musu dan uwansu, Allah ya basu kowacce daya daga cikin biyun nan a matsayin zabi in suka zabi na farko ya yi in suka zabi na biyu ya yi.

Bayan haka ubangiji subahanahu wata'ala, ya nuna tsare jinin mumini, tsare jinin musulmi, kare jinin dan uwanka musulmi, wannan daya ne daga cikin wasiyyoyi guda goma da Allah ya kebanci al-ummar manzon Allah dasu, wadan da suka zo a jere cikin "suratul An'am" Ya ‘yan uwa musulmi! Manzon Allah sallalahu alaihi wasallam, ya labarta mana cewa dukkan wani mutum da ya kashe dan uwansa da ganganci, to za a zo dasu, ranar alkiyama sai wanda aka kashe ya rike wanda ya kashe shi, hannun sa yana kan zankonsa ya ja shi sutafi gaban Ubangiji Ta'ala ya ce ya ubangiji tambayi wane, me nayi ya kasheni? Alokacin da zai fadi haka jijiyoyin wuyan sa suna furzar da jini domin a halartowa da makshin munin hotan abin da ya akata a gidan duniya, yace tambayi wane me nayi ya kashe ni akan wanne dalili? banbancin siyasa, ko addini, ko manufa, zai ce ya ubnagiji tambayi shi me nayi ya kashe ni. Haka hadisi ya tabbata acikin Sinanu Nisa'i wanda ya ke hadisi ne sahihi.

Ya yan uwa musulmi, addinin musulunci a lokacin da yake haramta kisan kai, ba wai yana haramta zubar da jinin muminai ba kadai! a a hatta daga cikin kafirai wanda shariar musulunci ta kare masu jinin su da dukiyoyinsu, to in ya zamto dokokin Allah da ya saukar ta haramta zubar da jinin wanda bai furta kalmar shahada ba, jinin wanda ya ce Allah uku ne, wanda ya ce Uzairu Binullah! To ya ya kima da daraja da tsada ga jinin wanda ya ce ya shaida babu abin bautawa bisa cancanta da gaskiya sai Allah, kuma Annabi Muhammad Manzan Allah ne.

Haka kuma, kafiri wanda kuka yi yarjejeniyar zaman lafiya tsahon wasu shekaru kan cewa ba za ku yaki juna ba a iya wannan sheakarun na yarjejeniya, to haramunne ka kashe daya daga cikin su ko ka kwace dukiyar sa, sai wadan da kuka yi yarjejeniyar basu rushe ko wanne irin sharadi ba na yarjejeniyar, kuma baku tallafawa wasu ko wani akan ya yake su ba. To, irin wannan, ku tsare masu alkawarin su na tsahon lokacin da kuka yi alkawarin da su, alokacin inda zaku kashe wani kafiri to wanda yayi kisan, Manzan Allah ya ce tsakanin sa da Al-jannah tshon tafiyar shekara dari biyar, haka ya bayyana acikin hadisi sahihi, ga shi kuma arne ka kashe ba musulmi ba, to ina ga dan uwanka musulmi! Ka dauki bindiga da kowanne irin dalili cikin dalilai ka rabashi da rayuwar sa, to kai kuma kayi me a bankasa? kuma mu duba muga "Al-mu'utamalun" wadan da yaki tsakanin ku da kasar su wanda akace inda daya da ga cikin su ya nemi izinin zuwa kasar ku, kuma ku ka bashi dama ya zo yayi iya ka kwanakin da zai yi, to wajibine ku tsare masa jinin sa da dukiyar sa har ya gama iyakar kwanakin da zaiyi, kuma ku yi masa rakiya har sai kunje inda zai ji ya amintu daga gare ku. Wannan ya na nuna kulawar shari’ar musulunci da dokokin Allah dangane da tsadar rayuwar biladama, ko da ya ki da aka shar’anta mana ba wai an halarta mana shi ne kawai don malalar da jinin kafirai ba, manufar shar’anta yaki ne idan kafirai suka furta kalmar shahada bisa ga zabin su sai a kyale musu jinin su, wannan tasa idan kafirai sukaki su furta kalmar shahada amma zasu shiga cikin "amman dinku" wato karkashin gwamnatinku, ku kyale su akan addinin su, baza ku kashe su ba. Ashe da manufar itace kisa to da idan amfito sai an kashe mutum koda ya yi kalmar shahada, sai ace ai anriga anfito lokaci ya kure me yasa yaki yi kafin a fito, da manufar itace kisa to da babu yadda za'a ce an samu wasu kafiran amana wadan da zasu zauna karkashin daular musulunci, kuma a tsare musu jinin su da dukiyar su ba tare da anribace su ba.

To wannan ya nuna cewa addainin musulunci addini ne da yake kare rayuwa, ba na salwantar da rayuwa bane, duk wanda dokokin addini suka ce a salwantar da rayuwarsa, to idan ka duba zaka ga babu abin da yafi dacewa sama da a salwantar da ratuwar sa, shi yasa kafirai duk kafircin su duk barnar da sukayi a bankasa, Allah ya ce idan sun tuba ta hanyar furta kalmar shahada sun bayar da zakkah, kar a kashe masu rayukansu kar a ribace su, to ina ga dan uwanka musulmi wanda ba tuba ya yi ba, dama can shi musulmi ne, bawai tuba yayi ba, yana sallah, yana zakkah, yana karatun al-qurani, da salati da istigfari gwargwadon iko, yana yi, tare da haka kace zaka rabashi da rayuwar sa da wanne dalili cikin dalilai.

Ya yan uwa dalilan da suke sanya mutane kisan kai suna da yawa, amma ga misali, yan fashi da makami wanda zasu kashe mutum don su kwace dukiyar sa sawa'un a cikin gidan sa ko akan hanya lokacin da yake tafiya a kashe shi don a kwaci dukiyar sa, to wadannan Allah ya fadi sakamakon su acikin Al-qurani hukuncin su shi ne akashe su ko a tsire su ko a yan ke musu kafar dama da hannun hagu ko kuma akore su daga kasar musulmi.

Haka kuma, ‘yan ta’adda wadan da su ba dukiyarka suke da bukata ba, rayuwarka kawai suke son dauka, saboda kawai wata manufa ta duniya da suke fatan samu, sannan da tunanin watakila kana iya zamar musu barazana wajen samun abinda suke son samu.

Wannan dai Khudba ce da Marigayi Shiekh Jafar Adam ya gabatar a masallacin Juma’a na Dorayi a lokacin da yake raye. Muna addu’ar Allah ya kai rahama gareshi, ya kyauta makwancinsa.

No comments:

Post a Comment