Saturday, December 13, 2014

Yakin Neman Zaben Sam Nda-Isaiah: An Fara Da Murmushi An Kammala Da Murmushi

MASHA ALLAH! MASHA ALLAH!! Godiya ta tabbata ga Allah (SWA), an fara da murmushi an kammala da murmushi.

Yau 11/12/2014 APC ta kammala babban taronta na kasa, inda wakilan jam'iyyar suka zabi dan takarar shugabancin kasa a zaben 2015 na jam'iyyar, kuma Allah ya bawa Janar Muhammadu Buhari nasara da gagarumin rinjaye.

Maigidana Sam Nda-Isaiah na daya daga cikin masu neman takarar su biyar, sai dai Allah bai bashi nasara ba, a zahiri, amma a badini yayi nasara (duk wanda ya san tsakanin su da Buhari zai fahimci hakan).

Kusan watanni 10 ana wannan aiki, tun da aka fara Allah cikin ikonsa ya sa an shiga cikin lafiya, kuma yau ga shi an kammala cikin lafiya.

Bayan na mika dukkan godiya ta ga Allah, ina kuma godewa iyaye na da dukkan 'yan uwana da suka bani cikakken goyon baya, sai kuma edita na Al-Amin Ciroma (Leadership Hausa), da dukkan abokaina masu daraja, kwarai na samu muhimmiyar gudunmawa daga gare ku, kuma ina godiyar sosai da sosai Allah ya sanya alheri. Kullum ina kara godewa Allah da ya ba ni abokai irin ku.

Ina rokon ku addu'ar Allah ya sanya wa abinda zan sa anan gaba ya kasance mai alheri na gare ni da addinina.

...Ina taya Baba (Janar Muhammadu Buhari) murnar wannan gagarumar nasara, kuma in sha Allah zan bada duk wata gudunmawa da zan iya, da dukkan abinda Allah ya hore min don ganin Buhari da APC sun yi nasara a 2015!

Wednesday, December 10, 2014

TA'AZIYYA: Rasuwar Ibro Ta Sani Hawaye

Kamar mafi yawan lokuta, yau ma karar kiran wayata ne ya tashe ni daga bacci, bayan na tashi na duba wayar na ga sabuwar lamba ce, da na amsa wayar sai na ji wata baiwar Allah ce daga Sokoto, bayan mun gaisa sai tace "Don Allah wai Dan Ibro ya rasu?, an fada min cewa ya mutu, amma ban yarda ba sai na ji daga wajen 'yan jarida". Kai tsaye na bata amsa da cewa "A'a". Ba tare da tunanin ya kamata na bincika gaskiyar labarin ba, dalilina anan shi ne kusan sau biyar kenan a sani na ana yada jita-jitar Ibro ya mutu, yayi hatsarin mota, amma daga baya sai Ibro ya fito ya karyata labarin.

"Ban mutu ba, amma idan lokacin amsa kira ya zo, zan tafi" wannan amsa ce daga bakin Ibro, a wani lokaci a baya da aka yada irin wannan jita-jitar cewa ya rasu.

Bayan mun kammala waya da Malama 'yar Sokoto, ban ajiye wayar ba, sai na shiga Facebook, har ga Allah ko a zuciyata ban shiga don tabbatar da labarin mutuwar Ibro ba, saboda a zuciya ina da yakinin cewa bai mutu ba, kawai abin da aka saba ne na yada jita-jita akan sa.

Rubutun da na fara cin karo da shi ne ya sanya bugun zuciyata tsayawa cak, rubutun edita na Al-Amin Ciroma (Editan Leadership Hausa) na gani, inda yake bayyana labarin rasuwar ta Ibro, wannan rubutun kadai ya tabbatar min lalle Ibro lokaci yayi (Allah ya jikansa). Ina yin kasa sai ga rubutun Ado Ahmad Gidan Dabino, Auwal Danlarabawa da wasu da dama duk suna nuna alhinin su da addu'ar Allah ya gafartawa Ibro.

Kafin na ankara sai naji idanuwana sun cika da kwalla, sai kuma hawaye ya biyu kumatu da daga baya. Ba komai ya sa zuciyata ta kara cikin kankanin lokaci ba, sai tsoron Allah da ya kara shiga jikina. Na kara tabbatar da cewa idan lokacin mutuwar mutum bai yi ba, ko duk mutanen duniya za su so ya mutu ba zai mutu ba, amma da zarar lokacin yayi to fa 'babu tsumi kuma babu dabara' kamar yadda mawaki Aminu Ala yake fada a cikin wata wakarsa.

Allah ya jikan Rabilu Musa Ibro, Allah ya gafarta masa, Allah ya bawa iyalansa hakurin jure wannan babban rashi. 

Da ba don dan Adam akwai shi da saurin mantuwa ba, da zan iya cewa har abada ba za a iya mantawa da Rabilu 'Dan Ibro' ba.

Friday, December 5, 2014

TAYA MURNA GA 'YAN KADUNA KAN NASARAR EL-RUFAI

Kafin na taya Malam Nasir el-Rufai murnar nasarar zama dan takarar gwamna, sai na fara taya mutanen Kaduna murna, saboda hanyar da suka hau ta samun shugaban da zai sake dawo da martabar Kaduna a idon duniya. 

 Maganar gaskiya ba karamin farin ciki nayi ba, da nasarar el-Rufai, Kaduna uwa ce ga Arewa, amma tuntuni martabarta ta dusashe a idon duniya. 

 Idan 'yan Kaduna suka zabi el-Rufai ba shi suka yi wa alfarma ba, kan su suka yi wa, kamar yadda Janar Muhammadu Buhari ya bayyana lokacin kaddamar da takarar ta el-Rufai. 

Ina matukar kishin el-Rufai ba dan Kano ba ne, da dan Kano ne.... Fada ma bata baki ne. 

 Allah ya bawa el-Rufai nasara a Kaduna!

Sunday, October 12, 2014

Abin Da Janar Buhari Ya Fada Min

Janar Muhammadu Buhari, bai da mantuwa, ya fada min magana kusan shekaru biyu, jiya muna haduwa, ina gaida shi, ya sake maimaita min wannan magana.

Mun hada da Janar jiya a Owerri jihar Imo, wurin daurin auren 'yar Gwamna Rochas Okorocha, a lokacin da naje gaida shi na yi tunanin ya manta sunana, ashe bai manta ba, yana kallo na ya ce Bashir, na durkusa na gaida shi, na tambaye shi kanwata Fatimatu Buhari (Karamar 'yarsa) ya ce tana lafiya.

Ga mamakina sai na ji ya ce "Bashir, Nijeriya fa ta ku ce" maganar ta ban mamaki sosai, saboda ba a lokacin ya taba fada min hakan ba, sannan ya ci gaba da cewa "dole ku so ta, ku sa ta a zuciyarku, ku kyautata mata, sannan ku yi sadaukarwa a gare ta, haka ne zai sa ita ma a nan gaba ta kyautata muku".

Duk da ba kowa ya ji maganar da yake fada min ba, sai wadanda suke kusa da shi, shugaban jam'iyyar APC, Cif John Oyegun da matarsa, su kuma ba Hausa suke ji ba, amma na ga idanun mutane, cikin har da gwamnoni suna kallon mu... Ban sani ba ko tunani suke Baba Buhari yana cewa Bashir kai zaka gaje ni... (Dariya)!

Ba iya wadannan maganganun Buharin ya fada min ba, amma sauran na dauke su a matsayin sirri, ya fada ne a kaina, ni kuma ina gani idan na fito na fadi, wasu za su ga kamar na yi alfahari...

...Allah ya karawa Janar Buhari lafiya, Ya kara masa nisan kwana mai amfani.

Monday, September 29, 2014

Taya Murna Ga Ado Ahmad Gidan Dabino MON

Lambar Girmamawa Ta MON Da Aka Karrama Gidan Dabino Da Ita

Gidan Dabino Yayin Wasu Daga Cikin Tafiye - Tafiyensa A Kasashen Turai

Alhamdulillah! Masha Allah!! A madadin dukkan wani Bahaushe mai son ci gaban harshen da burin ganin daukakarsa, ina taya shugaba na kuma malami na, Ado Ahmad Gidan Dabino MON, murnar babbar lambar girmamawa da kasar mu Nigeria ta ba shi a yau (29/09/2014) a matsayin dan ta, da ya sa ta alfahari a bangaren da ya dauka na rayuwa.

Shugaba Goodluck Jonathan ne ya mannawa Gidan Dabino lambar mai suna MON.

Ga wanda bai san wane ne Gidan Dabino ba, ko kuma ya san shi yake bukatar karin bayani akansa ga kadan daga cikin tarihin rayuwarsa, wanda na tsakuro a turakar Marubutan Hausa.

An haifi Ado Ahmad Gidan Dabino a Danbagina Karamar Hukumar Dawakin Kudu a shekarar 1964, ya yi karatun allo a Zangon Barebari. Bai samu damar yin karatun boko ba sai da ya kai shekara ashirin, sannan ya fara zuwa makarantar yaki da jahilci ta masallachi, watau makarantar da aka fi sani a Kano da makarantar Baban Ladi,daga nan ya yi karatun Sakandare a GSS Warure inda ya samu SSCE a 1990. Daga nan ya yi kwas na shekara guda akan karatun makafi da koyon aikin kafinta, A shekarar 2005 kuma ya sami diploma akan aikin sadarwa daga jamiár Bayero ta Kano. 

Ado Ahmad na daya daga cikin fitattun marubutan Hausa na zamani kuma littafinsa mai suna In da So da Kauna na daya daga cikin fitattun littattafan Hausa na kowane zamani. 

Ya rike mukamai da dama a Kungiyoyin marubuta, shi ne shugaban Kungiyar Marubuta ta Raina Kama, ya taba zama Mataimakin shugabna ANA reshen Kano, ya zamar mata maáji kafin ya zama shugabanta a 2006. 

Gidan Dabino ya taba zama Edita na FIM magazine kasancewar daya daga cikin wadanda suka kafata a 1999. Kuma shi ne mawallafin Mumtaz. Kazalika shugaba/daraktan gudanawarwa na Gidan Dabino International Nigeria Limited. 

Ya gabatar da makalu a manyan tarrurruka na karawa juna sani a jami'o'i daban daban a gida Nijeriya da wasu daga cikin kasashen turai. 

Za a iya kiransa mashiryin wasan Hausa, dan jarida kuma mawallafi. 

Litattatafansa da suka fito sun hada da:

In Da So da Kauna 1 da 2 (1991)

Hattara Dai Masoya 1 & 2, (1993)

Masoyan Zamani 1& 2, (1993)

Wani Hani Ga Allah 1 & 2, (1995)

Duniya Sai Sannu (1996)

Kaico (1997)

Sarkin Ban Kano (2004) tare da Sani Yusuf Ayagi

Ina kara taya Ado Ahmad Gidan Dabino murna, ina kuma kara yi masa addu'a da fatan alheri, kamar yadda ya karbi wannan kyauta daga Nijeriya, Allah ya nuna mana ranar da zai karba daga Afrika da duniya baki daya. 
Takardar Shedar Girmamawa ta MON da aka bawa Gidan Dabino

Tarihin Galadiman Kano - Alhaji Tijjani Hashim

Marigayi Galadiman Kano
An haifi Galadiman Kano Ahmadu Tijjani dan Turakin Kano Hashimu dan Sarkin Kano Abbas dan Sarkin Kano Abdullahi I dan Sarkin Kano Ibrahimu Dabo a shekarar 1932 a cikin birnin Kano.

Ya fara karatun elementare a garin Bebeji a shekarar 1944. A shekarar 1944 ya shiga makarantar Medil ta Kano inda ya daina a 1951.

A 1952 ya fara aiki a En'e ta Kano da mukamin Malamin Dabbobi, mai duba tsaftar dabbobi da za a yanka a kara ta Kano. A 1956 aka zabe shi dan majalisa mai wakiltar Sumaila a majalisar dokoki ta Arewa.

A zaman sa a wannan majalisa ne ya rike mukamai da dama kamar shugaban hukumar bada kwangila ta Kaduna da shugaban kwamitin tabbatar da jam'iyyar NPC ta lashe zabe a lardin Sardauna. Ministan cikin gida na Jihar Arewa. Kwamishinan lardi mai kula Lardin Kabba wadda akan wannan mukami soja suka yi juyin mulki. Dawowarsa gida ne tasa Sarkin Kano Marigayi Ado Bayero, ya nada shi sarautar Dan Isan Kano kuma kansila mai kula da ayyukan gayya da taimakon kai da kai.

A 1976 ya sami karin girma zuwa sarautar Turakin Kano da bashi kulawa da gundumar Kumbotso. A 1980, ya sami canji zuwa kansila mara ofis saboda yawan harkokinsa. A 1989, ya sami karin girma zuwa sarautar Dan Iyan Kano da ci gaba rike mukamin kansila mara ofis.

A1992, ya sami karin girma a babbar sarautar Kano a matsayin Galadiman Kano kuma shugaban kwamitin kudi na majalisar Sarki. A 2012 Sarki ya kara masa aikin hakimcin birnin Kano. Kuma a kan wannan aiki ya ke zuwa yau da Allah ya amshi ransa. 

"Galadiman Kano Tijjani mashahurin mutum ne da babu iri nai a wanga zamani wajen taimako, adalci, tausayi da kyautatawa. Shi kadai na sani a wanga zamani mai sarauta attajiri mashahuri Kasaitacce da za ka je wuri nai har ka tadda shi ba mai tambayar ka ina za ka". 

Allah ka dube shi, Ka yi masa rahma ka tausaya masa Ka jikansa, Ka sa Aljanna ce makomarsa.

Friday, September 26, 2014

Game Da Ni (Bashir Ahmad) A Takaice

Cikakken sunana Bashir Ahmad Ishaq, Ni haifaffen jihar Kano ne, mazaunin birnin tarayyar Nigeria, Abuja. 

Ina aiki da kamfanin Leadership Group Limited, masu buga jaridun (Leadership Daily, Leadership Weekend, Leadership Sunday da Leadership Hausa).

Sai dai har yanzu ni dalibi ne mai neman ilmin addini Musulunci (Domin na san yadda zan bautawa Allah, Mahaliccina) Sannan mai neman ilmin zamani (Domin na san yadda zan tafiyar da rayuwata tare da mutanen zamani). 

Ina son jin labarai da tarihin al'ummomin da suka gabata musamman wadanda suka yi nasara a rayuwarsu (Domin daukar darasi daga gare su). 

Ina da burin tafiye - tafiye (Domin tafiya mabudin ilmi ce). 

Ina son haduwa da jama'a daban - daban, masu bambancin ra'ayi (Domin sanin al'adunsu da halayyen su).

Ina sha'awar zama da wadanda suka fi ni ilmi (Saboda koyaushe nayi hakan ina kara daukar sabon ilmi) 

A kodayaushe kuma ina sha'awar zama shahararre kuma sanannen dan jarida (Domin na samu damar bayyanawa duniya ra'ayoyin talakawan Nigeria, daya dade a kunshe cikin zuciyoyinsu ba tare da samun damar bayyanawa ba). 

A yanzu ina son shiga harkokin siyasa (Domin na bada gudunmawa wajen tabbatar da kyakkyawar Nigeria ga kowa).

HANYOYI TUNTUBA

Lamba = +2348032493020 | Email = bashahmad29@yahoo.com | Twitter = @BashirAhmaad | BBM = 2B2B92CB | Instagram = BashirAhmaad
Bashir Ahmad

Babu Tabbas Kan Mutuwar Shekau - Amurka


Gwamnatin Amurka ta ce har yanzu ba ta samu wata shaida da za ta tabbatar da ikirarin gwamnatin Nigeria ba, na mutuwar Shugaban Kungiyar Boko Haram Abubakar Shekau.

Wani jami'in harkokin wajen Amurka, Rodney D Ford ya ce suna ci gaba da kokarin tabbatar da sahihancin ikirarin gwamnatin Nigeria, da gaskiyar cewa akwai mutanen da ke shigar-burtu da sunan Abubakar Shekau.

A baya dai, rundunar tsaron Nigeria ta ce dakarunta sun kashe wani mutum da ke batar da kama da sunan shugaban Boko Haram, Abubakar Shekau yayin fafatawa a garin Kunduga.

Mai magana da yawun shalkwatar tsaron Nigeria, Manjo Janar Chris Olukolade ya yi ikirarin cewa Abubakar Shekau ya jima da mutuwa amma wasu ke yin shigar-burtu don ci gaba da yada angizon kungiyar.

Babu wata kafa mai zaman kanta da ta tabbatar da batun mutuwar Abubakar Shekau jagoran kungiyar Boko Haram.

- BBC Hausa

Saturday, September 13, 2014

Ni Da Dan Takarar Gwamna Jihar Jigawa, Pharm. Hashim Ubale Yusuf

Pharm. Hashim Ubale Yusuf, mai neman jam'iyyar APC ta sahale masa takarar gwamnan jihar Jigawa, tare da ni Bashir Ahmad, a gidan gwamnatin jihar Kano, lokacin taron Dandalin Siyasa Online Forum, karo na 5 da aka gudanar a Kano 2014.
Bashir Ahmad da Pharm. Hashim Ubale Yusuf

Tuesday, August 5, 2014

Ni Da Kadaria Ahmad

Ni (Bashir Ahmad) da shahararriya kuma gogaggiyar 'yar jarida, Hajiya Kadaria Ahmad, ta gidan telebijin na Channels TV, dake jihar Lagos.

Sunday, June 8, 2014

ABIN LURA: Allah Ne Ya Zabi Sanusi Lamido Ba Kwankwaso Ba

Bari na fara wannan rubutu na wa da wasu baitocin waka, da suka yi daidai da abinda zan rubuta....

"Fatan Mai Rabo Guda Ne Baya Fada,
Don Kowa Ya ja Da shi Sai Ya Bar Masa,
Koda Dambe Ne Bare Filin Kokawa,
Kowa Zai Karo Da shi Sai Ya je Kasa,
Gode Wa Ubangiji Don Shi Yai Maka,
Domin Ka Sani Ma Nema Wasu Sun Rasa."

A karshe dai, bayan shekaru 51, Kano ta sake yin sabon Sarki, hakan kuwa ya faru ne bayan rasuwar marigayi Sarkin Kano, Alhaji Ado Bayero a ranar Juma'ar da ta gabata, wanda Allah ya bawa sabon Sarkin shi ne Mai Martaba Sanusi Lamido Sanusi, tsohon gwamnan babban bakin CBN. Sai dai wasu na ganin Sanusin ba shi ne ya cancanta ba, hasalima gwamnan Kano, Rabiu Kwankwaso ne ya yi amfani da damarsa, ya yi karfa - karfa ya kakabawa Kanawa, Sanusi a matsayin sabon Sarki. Hmm, ni dai kam ina da ja akan hakan.

 Maganar gaskiya, mafiya yawan jama'ar Kano, ba sa goyon bayan nadin Sanusi Lamido Sanusi a matsayin sabon Sarkin da zai jagorance su, kuma suna da dalilin su na yin hakan. Ko ni har ga Allah a zuciyata na fi so daya daga cikin 'ya'yan marigayi Sarkin Kano ya gaje shi saboda wani dalili na wa. Amma hakan bai sa na gamsu tare da yin addu'ar fatan alheri ga Sanusi Lamido a matsayin sabon Sarkinmu ba. Ba don komai ba sai don saboda na san Allah shi ke bada mulki ga wanda ya so, kuma a lokacin da ya so. 

Duk karfin Sanusi, kudi da mukaminsa bai isa ya sa ya bawa kansa mulki ba, misali Sanusi ya rike mukamin gwamnan babban banki har na tsawon shekaru 5, amma hakan bai sa ya zama Sarkin Kano ba, sai lokaci da shugaban kasa, ya dakatar da shi, ko kuma na ce wa'adinsa ya kare, sannan Allah ya nufa zai zama Sarkin, kuma ya zama.

Kuma mu tuna cewa, da Gwamna Kwankwaso zai iya yin karfa - karfa ya dora wani ya zama Sarki, to ko tantama ba zan yi ba, da mahaifinsa, Mai Girma, Alhaji Musa Saleh Kwankwaso ne zai zama sabon Sarki, tun da kuwa, shi ma basarake ne. Na san za ku amince da haka, saboda kuwa duk irin soyayyar da Kwankwaso yake yi wa Sanusi, ba ta kai wanda yake yi wa mahaifinsa ba.

'Yan uwana Kanawa na san abin akwai ciwo a zuciya, ga shi Allah ya dauki ran Sarkinmu da kowa yake so, sannan wanda ba ma so saboda wani dalilai ya zama sabon Sarkin.

...Sai dai na lura da cewa da yawa daga cikin mutanen da ba a Kano suke ba, suna matukar goyon bayan Sanusin a matsayin sabon Sarki, kuma su ma na hakikance suna da kwararan dalilan su.

Allah ya zaunar da Kano lafiya!!!

Wednesday, June 4, 2014

SABON SALO: Sam Nda-Isaiah Zai Tattauna Da 'Yan Nigeria Kai Tsaye A Facebook

 Sam Nda-Isaiah, dan takarar shugabancin kasa a APC, zai tattauna da ku kai tsaye a shafin sada zumunta na Facebook.

Wannan dama ce ga 'yan Nigeria, ta wannan shirin za ku iya yi wa Sam duk wata tambaya da kuke bukatar amsarta daga gare shi, kuma ku samu amsa nan take.

Tattaunawar za ta kasance a gobe Alhamis 5th Yuni, 2014  da misalin 10:00am - 12:00pm da kuma 2:00pm - 3:00pm.

Lokaci ya yi da za ku ke shigowa ana damawa da ku a harkokin siyasar Nigeria, domin bada gudunmawa wajen samun canji na alheri.

Monday, June 2, 2014

Sam Nda-Isaiah Zai Tattauna Da Jama'a Kai Tsaye A Shafukan Sada Zumunta

 
#TAMBAYISAM (Tattaunawa)

Sam Nda-Isaiah dan takarar shugaban kasa a APC zai tattauna da ku kai tsaye game da takararsa da kuma Nigeria
____________________________________
* Facebook: Alhamis 5th Yuni, 2014 | 10am - 12pm da 2pm - 3pm
____________________________________
* Twitter: Asabar 7th Yuni, 2014 | 4pm - 7pm
____________________________________
* Google+: Laraba 11th Yuni, 2014 | 10am - 12pm

>>> AIKA TAMBAYA TA WADANNAN HANYOYI

Twitter: @SamNdaIsaiah ko @Sam4Hausa

Za kuma a iya amfani da wannan alama #ASKSAM a wadannan shafuka a yayin da tattaunawar ke gudana.

Friday, May 9, 2014

Janar Muhammadu Buhari Kan Sace Daliban Chibok

A dai-dai wannan lokaci da shuwagabannin duniya suke kawowa Najeriya dauki, wajen gani an nemo daliban Cibok mata wadanda aka sace su kusan 300 a makarantarsu ta Sakandare, dan siyasa, tsohon shugaban kasa kuma daya daga cikin shuwagabannin jam'iyyar APC Janar Muhammadu Buhari mai ritaya ya fitar da sanarwa.


"A makonnin da suka wuce, sace dalibai mata da akayi a Cibok, Jihar Borno ya nuna a fili irin barazanar da muka dade muna fama da ita a kasar nan, daga ayyukan mutanen da basu fahimci Musulunci ba.

Addu’o’in mu suna tare da iyalen wadanda suka rasa ‘yan uwansu a wannan tashe-tashen hankula da muke ta gani. Sannan kuma muna mika alhininmu ga iyayen da ‘ya’yansu suke cikin hannun wadannan mugayen mutane.

Wannan mummunan bidiyo da aka saka a yanar gizo, ya nuna a fili cewa shaidanun mutanennan basu da zuciya. Ya nuna ko suwaye su a fili, kuma maza kamar wadanda bai kamata a ce suna keta diyaucin kasa ba. Daga abubuwan da suka nuna, ya fito fili cewa babu Allah a zuciyarsu. Basu da nufin kirki ga kasarmu. Ni Musulmi ne, kuma ina aiki da koyarwar addinin Kirista ma, ta yin amfani da koyarwar addinan guda biyo domin zaman lafiya da kowa da kowa a duniya.

Ina mai sha’awar jaddada matsayi na, na sukar wannan ta’asa wanda bashi da waje duniyar bil-adama. Addinin Musulunci bai amince da shi ba, kuma babu wannan a cikin Bible.

Ya kamata mutanen nan su sani cewa duniyar wayayyu na adawa da ta’addanci. Muna matukar godiya da duniya take goyawa Najeriya a wannan matsanancin lokaci. Muna fata da addu’a na cewa wadannan yara mata zasu koma wajen iyayensu a kwanaki masu zuwa.

Yayin da gwamnatin Tarayya da sojoji suke aiki domin tabbatar da tsaron ‘yan kasa a wannan lokaci, munyi imanin cewa za’a iya kara matsa lamba wajen gani an tabbatar da tsaron Najeriya da ‘yan Najeriya. Saboda haka muna farin ciki da gwamnatin Tarayya ta amshi taimakon kasa da kasa wajen nemo wadannan dalibai, da kuma kawo karshen ta’addanci a wasu bangarorin Najeriya.

Nayi yaki domin hadin kan Najeriya. A shekaru na masu yawa, ina son tattaba kunne na, da naku tattaba kunnen, da matasa da ma duka ‘yan Najeriya su albarkata daga kasa mai cigaba da hadin kai, da kuma kyamar tarzomar bangaranci a cikin gida, da ma daga kasashen ketare.

Yanzu ba lokacin siyasa bane. Yanzu kuma ba lokacin nuna yatsa bane saboda ban-bancin akida. Hadin kan Najeriya ba abune na wasa ba, kuma babu abunda zai raba mu a matsayinmu na mutanen kasa daya. Saboda haka ina kira ga ‘yan Najeriya a gida, da ma kasashen ketare su goyi bayan kasa a yunkurin da takeyi na kawo karshen hare-hare akan fararen hular da basu ji ba, basu gani ba.

Sai mun ajje a gefe, duk wani buri namu, mun tabbata kasarmu ta hada kanta, ta kwato diyaucinta. Banda ma haka, sanin dukkaninmu ne cewa bamu da wata kasa banda Najeriya da zamu iya kira namu.

Allah Ya albarkaci Najeriya."

#KuDawoManaDaYaranmu #BringBackOurGirls

Daga VOA Hausa

Sunday, May 4, 2014

My ‘Sambisa’ Tale – Chibok Girl

It was going to be like a normal night

It was going to be a chat with my fellow girls until I give-in to sleep

It was going to be a night with Amina, Fatima and Hauwa

Just a normal night… just after I said my little prayer 

A night when the moon couldn’t whisper to my innocent heart like every other night

A night when my dreams will be engulfed by the darkest night

Have my innocent heart committed a crime to chase that dream?

If achieving my goals through education is forbidden, would an early marriage be acceptable?

If regrets could turn back the hands of time

If wishes could make the watchman not feel drowsy on duty

Oh! I wished my life never depended on the weak index of that soldier (God bless his efforts)

Or on the frail fence where we even jump over sometimes.

In my sleep I heard strange voices; on my feet was a tap…

‘HE’ touched me… Mama! He touched me!!!

Screams went louder from different sections; I closed my eyes and wished it was a dream

Lo and Behold! The very aspiration and my pursuit for empowerment delivered me unto ‘HIM’.

I reached out to Hauwa to at least be on same four-wheeled truck to share from her courage

Instead my worst fears gripped me as I heard more Horror and masculine voice

Gunshot loudly mellowed our screams for help

Could I have jumped off like Fatima and Amina; I thought of it but I couldn’t dare…

How can this same language they speak become foreign to me?

I called on same Allah as they too scream…

Does a different blood flow through their veins?

My heart beat stopped several times yet my thoughts were wide.

The sounds of Crickets and strong wind; cries and prayers proved we were going deep

Deep into Isolation; deep into a cave we talked dreadfully of in our little girl’s gossip

The plague I once feared has come upon me

What is forbidden? Is it my aspirations, HIS Hellish ideology or what I have been subjected into right now?

Father! I need now more than ever your love to rescue me from this hate

It’s the 7th day so far and for the first time in my tender life I have seen my period in the forest

Mama! Oh! Mama… they wouldn’t let me do what you have taught me.

Mama you have no idea what HE has done me…

I heard some of us have died… some of starvation and some from deep wounds

Mama, it’s going to be my turn tomorrow…

I contemplate suicide, would HE do this to me?

Mama it’s cold out here, I feel pains on my chest am I going to die?

You will not be wrong if you think we have taken oaths…

The heights of all imaginations have been done to me Mama…

I will be 13years tomorrow and I have seen it all

Mama, my tender eyes have seen the other side of Life

Be strong Mama, I have tried not to give-up…

Be brave as you have taught me to be

If I see you again, please don’t ask me what has happened to me.

If not mama, know that the worse is yet to happen because I choose not to give-up.

The stars will never shine bright again…

The moon will set at noon…

The cock will crow at Midnight…

It will never be the same again….

But I love you Mama!!!

...Dedicated to the abducted Chibok girls. #BringBackOurGirls

Monday, April 28, 2014

HIRA TSAKANIN BABAN DA MAMAN FAISAL KAN JARUMAN FINAFINAN HAUSA


Hira tsakanin miji (Baban Faisal) da maidakinsa (Maman Faisal) akan jaruman finafinan Hausa da suke goyon baya.

"Kai Safiya gaskiya fa duk 'yan fim din Hausa babu mai birge ni kamar Zainab Indome"

"Lallai maigida na ga kana yawan sayo fina finan da ta ke ciki"

"A she dai kin lura?"

"Haba Baban Faisal ai na dade da lura da haka"

"Wato Dear ko bata min rai kika yi idan na kalli idanuwan Indome sai na ji na huce"

"Ok shi ya sa na ga daga mun sami matsala ko ba wuta sai ka tayar da inji ka sanya fim din ta.?"

"Kwarai ma kuwa, ba ma kamar a ce fim din da ta ke dan rausayawa, kin san ta iya rawa"

"Gaskiya kam Zainab Indomee ta yi"

"Ga ta duk kayan da ta sanya sai ki ga ya yi daram a jikin ta.

"Gaskiya Baban Faisal ka gama yarda da alamarin Zainab Indome"

"A zakin murya kuma idan kika sami Nafisa sai wata rana an gama,"

"Kai maigida Nafisa har wani dadin murya ne da ita?"

"Kwarai ma kuwa idan ta na magana kamar ta na rera waka"

"Hm Baban Faisal ba ka da dama"

"Kin san kuma wa ta fi kira da diri?

" Sai ka fada maigida"

"Na ba ki gari sahibata Safiya"

" Maigida ai ni a duniya babu mai birge ni kamar Ali Nuhu, ban taba ganin namijin da a duniya ya iya sanya kaya kamar Ali nuhu ba. Babu ma kamar idan ya sanya kananan kaya, wani fim da ya sanya wani wando iya gwiwa har tsayar da wajen na yi dan kawai na sha kallo........."

" Ke Safiya ki na da hankali kuwa?"

" Haba Baban Faisal da hankalina mana, rawa kuma da iya girgiza ban taba gajiya da kallon Adam Zango ba, A jikin sa kuma kasumbar da ya ke bari ita ta fi daukar min hankali"

"Safiya dakata ya isa haka, wace irin magana ce wannan ta rashin hankali?"

" Baban Faisal yadda ka dire dole nima sai na dire, ba rashin hankali a ciki. Murmushin Maishunku kuma shi ke sanya ni nutsuwa a duk lokacin da ya yi"

" Idan kika sake magana sai na shake ki 'yar iskar banza kawai"

" Baban Faisal sahibi ko kashe ni za ka yi wallahi sai na kai karshe yadda yadda ka dire na ka. Abinda ya sa kuma ka ji ban rabuwa da wakar Alan Waka ko da a bandaki na ke kuma ko muna tare muryar sa na sumar da ni gaba daya, wani lokacin sai na ji kamar na yi mutuwar tsaye"

" Gaskiya Maman Faisal kin yi gamo da bakaken aljanu, wannan rashin hankali har ina, wadannan maganganu na ki kare ba zai ci ba, sai ka ce arniya"

" Kar ka hada ni da arniya, kafi kowa sanin ni musulma ce kamar kai"

" To lallai ki na bukatar a yi miki rukiyya ko kuma aje wajen malamai su rubuta miki Innahu Ala Rajaihi lakadir kafa bakwai bakwai na kwana bakwai"

" Lafiya ta ras"

" To kuwa ba karamar 'yar rainin wayau ba ce ke kuma dole manyan ki su san wannan maganar gaskiya ba zan lamunce ba wallahi, haba sai ka ce a garin gaba gaba, ki na matar aure ki na fadin wai ki na sha'awar mazan waje dan iskanci, daga yau ma ba za a sake kallon fim a gidan nan ba"

...Shin tsakanin Baban Faisal da Maman Faisal wane ne ya fi gaskiya?    

GAYYATA!!!

INTEGRITY ICONS INTERNATIONAL na farin cikin gayyatar daukakin jama'a zuwa laccar shekara-shekara karo na biyu ta SAM NDA-ISAIAH, mai taken "Adalci Da Kyautatuwar Shugabanci Shi Ke Kai Kasa Ga Gaci".

•Babban mai masaukin baki, Mai Girma Gwamnan jihar Sokoto, Aliyu Wamakko, (Sarkin Yakin Sokoto).

•Karkashin jagorancin shugabancin Kakakin Majalisar Tarayya, Hon. Aminu Waziri Tambuwal, (Matawallen Sokoto).

•Uban Taron, Mai Alfarma, Sarkin Musulmi, Alhaji Sa'ad Abubakar na III.

•Uwar Taron, Dr. Baraka Sani, tsohuwar kwamishiniyar noma ta jihar Kano.

•Bako mai jawabi, Dr. Tukur Muhammad Baba, na Jami'ar Usmanu Danfodio.

•Manyan Baki na Musamman, Alhaji Shehu Usman Shagari (Turakin Sokoto), tsohon shugaban kasa, Bishop Mathew Hassan Kukah.

>Rana: 1 ga Mayu, 2014
>Lokaci: 11:00 na rana
>Wuri: Sultan Maccido Institute for Qur'anic & General Studies, Sokoto.

Don Karin Bayani Tuntubi:
-Muhammad Saidu Etsu - 08069789087
-Bashir Ahmad - 08032493020
-Abdulmumin S. Balogun - 08069727798
-Sadauki Abubakar Gawu - 08057009909

Monday, March 24, 2014

National Conference: Youngest delegate at Confab, Yadomah Mandara, pledges to Start a foundation with allowance

As a delegate to the National Conference – the youngest of them all, i am humbled to be part of the process of making my country better, I am willing to make modest sacrifices so that my generation and generation yet unborn can live in better country.

The Federal Government has rationalized that delegates should be paid sitting allowances, in all honesty I am modestly comfortable and able to cater for my immediate needs. Some of my colleagues have indicated their intention not to receive the money which in itself is a pointer to the fact that we still have men and women with high redeeming qualities among us.

However, I am not unmindful of the appalling poverty and great need that exists where I come from and the people I represent. We have a situation where widows and orphans have been abandoned by society, these are individuals made vulnerable by the insurgency. They have no idea how to pay the school fees of their children and wards, and how to eat at least once a day. We have a scenario where things we take for granted mean the world to others – physically challenged people who will never be able to afford wheel chairs and thousands of people who can’t afford medical care because they are poor and have been injured by terrorists. I want them to consider my sitting allowance as a gift to them and humanity.

I do not do this for praise nor to look good in the eyes of the society, I am doing this because it is the right thing to do. I have received my first payment which is the sum of 1,460,000 naira yesterday evening (21st March 2014) from the National Conference.

I hereby pledge to use my allowances as a seed grant and start a foundation that will cater for vulnerable women especially widows and children in Borno State, if you understand their hopeless and helpless state in Borno State and Northern Nigeria in general you will support me in this new drive to put a smile on their faces.

Friday, February 21, 2014

Sharhin Littafin Batulu

Marubuci – Auwalu Anwar
Shekara – 2013
Sunan Littafi – BATULU
Madaba’a – ABU Press Ltd
Shafuka – 264
Mai Sharhi – Halima Musa

BATULU littafi ne da aka wallafa a shekara ta dubu biyu da goma sha uku. Marubucin littafin, Dr. Auwalu Anwar, ba bako ba ne ga duk wani makarancin rubuce-rubucen Hausa. Hasali ma, sanannen marubuci ne wanda ya wallafa kasidu da littattafai da wake-wake da dama. Haka shi malamin tarihi ne wanda ya koyar a jami’ar Maiduguri. Bugu da kari, wasu za su iya tuna shi a matsayin marubucin sharhin GADAR ZARE a jaridar Rariya.

An zayyana labarin BATULU a cikin shafuka dari biyu da sittin da hudu. An kuma kasafta shi babi-babi har ashirin da biyar, ta yadda kowane jigo ya kasance babi daya, da takensa, tare da jero su bibiye da juna yadda labarin ya dinga hauhawa, har karshe. Wannan ya bai wa mai karatu damar hangen abinda kowanne babi zai kunsa.

Littafin ya dace da matasa, ’yan jami’a, samari da ’yammata, har ma da masu burin zuwa jami’a. Saboda su babban jigon labarin ya fi shafa don ya zama ishara. Amma iyaye ma wannan littafi zai musu matukar amfani don su san abubuwan da ke wakana a kusurwoyin jami’o’in da ’ya’yansu ke karatu da kuma abin da ’ya’yansu ke aikatawa da hatsarin da za su iya abkawa ciki. Makarantan littafin baki daya, za su amfana ta hanyar fahimta da kuma kiyaye musabbabin faruwar wasu al’amura a jami’o’i.

Marubucin littafin ya yi amfani da salon zance mai sauki wajen gabatar da shi. Ya yi amfani da Karin Magana sau da dama wajen isar da sakon da ya ke muradin isarwa ta yadda duk wani mai jin Hausa zai iya karantawa ya fahimta. Saukaka salon rubutu da marubucin ya yi, ya kasance tamkar kwarin gwiwa ga mai karatu. Haka ya yi amfani da salon tattaunawa da zancen zuci, wanda ya kara kawata, ya kuma saukaka bin labarin ga mai karatu. Akwai ’yan wuraren da ya yi amfani da kalmomin Larabci (kamar wurin da ake maganar hubbul Nabiyi da hubbul nafsi da hubbul malu). Ko kadan hakan bai takaita saukin fahimtar littafin ba. Wani abin sha’awa ma, sai amfani da Larabcin ya kara kayatar da sakon da marubucin ke kokarin isarwa.

Duk wanda ya karanta BATULU zai yi mamakin yadda marubucin ya fede biri har wutsiya dangane da yanayin rayuwar dalibai a jami’a. Musamman badakalar soyayya tsakanin dalibai, tsakanin dalibai da malamai da kuma tsakanin dalibai da jama’ar gari. Abin mamakin a nan shi ne, yadda ya bayyana yaya fasikanci ke wakana karara tsakanin rukunin wadannan bayin Allah. Musamman tsakanin dalibai mata da malamansu, ta yadda ake shakuwa da cin amana da yaudara. Wannan hakika ya jaddada tunani da kuma muguwar fahimtar da mafiya yawan jama’a ke yi wa daliban jami’a mata. Yawanci ana yi musu kallon ’yan iska kuma watsattsu marasa mutunci da kunya. Hakan na iya kara tunzura masu ikirarin hana ’yayansu mata zuwa jami’a don tsoron kar su lalace, har sai sun yi aure. Wadanda suka dauki abin da zafi ma, wannan na iya sa su hana ’ya’yan nasu mata zuwa jami’ar dungurungun da zimmar kare mutuncinsu.

Hausawa sun ce duniya zaman marina ce. Watau kowa da inda ya sanya gabansa. Duk cikin hayaniya da badakalar soyayya, har ma da fasikancin da ake yi a jami’ar Goron Dutse, marubucin ya iya nuna cewa ba duka aka taru aka zama daya ba. Misali, marubucin ya gabatar da hazikan dalibai da ke dawowa da dakon littattafai daga wajen karatu da tsakar dare, daidai lokacin da ake dawo da wasu ’yan’uwansu dalibai daga dabdala da sharholiya cikin motoci na alfarma. Ya kuma iya zakulo da bayyana mutuntaka da da’a da tarbiyya ta gari, ta hanyar wasu taurari da suka kasance dalibai mata, masu kamun kai da nuna kyama ga halayen ashsha da takwarorinsu, suka dulmiya a ciki. Watakila kasancewar wasu daga cikin wadannan dalibai jinsin Fulbe, ya bankado dan abin da ba a rasa ba, na kyashi da kushe tsakanin kabilun Hausawa da na Fulani, sabanin gamayyar dole da ake yi wa kabilun biyu.

Idan manufar marubucin ya bayyana ruguntsumi da dambarwa da kwamacala da yaudara da munafunci da cin amana a soyayya ne, to lallai ya cim ma burinsa. Haka ya cim ma nasarar bayyana irin gumurzun da ke wakana tsakanin hukumomin jami’o’i da kungiyoyin dalibai, da kuma tsakanin malaman da hukumomin kasa. Kamar yadda abubuwa suka kasance a jami’ar Goron Dutse, tabbas haka suke a jami’o’i da dama a zahiri.

BATULU littafi ne da za a iya gabatarwa ga kowanne irin makaranci saboda akwai darussa masu yawa a cikinsa. Babban darasin shi ne, mutum ya yi takatsantsan a harkokin soyayya. Saboda mayaudara sun yawaita a duniya ba ma a jami’a kawai ba.

An yi amfani da taurari da dama wajen isar da sako a BATULU. Manyan taurarin dai su ne Amadu da Batulu. Duk dambarwar cikin littafin ta rayuwarsu ce. Sai kuma sauran kananan taurari da aka yi amfani da su wajen karin bayanai, wadanda suka kasance kawaye, ko abokanai ko kuma malamai ga masoyan, har ma da iyayen manyan taurarin.

Idan ana maganar jigo, akwai su da dama. Babban jigon dai su ne Yaudara da Munafunci. Marubucin da kansa a karshe ya tari numfashin mai karatu da ya canza wa Batulu suna zuwa “Butulu”.
Wanda kusan duk mai karatu zai yanke wannan hukunci tun kafin ma ya kai karshen littafin. Akwai kuma irin wannan yaudara da ta wakana tsakanin Batulu da Malam Bello. Wasu na iya ganin soyayya a matsayin babban jigon BATULU. Wannan za ta iya kasancewa. Saboda an dabaibaye labarin cikin harkokin soyayyar da ta kasance tun farko tsakanin Batulu da Salisu, ta kai kan Malam Bello, sai kuma Amadu, Sai Musa, ta kuma kare a kan Iliyasu. Akwai jigon siyasa da rarrabuwar akidar mutanen birnin Kano tsakanin masu bin akidar siyasar gurguzu da kuma ta jari hujja. Haka kuma ta kasance a siyasar jami’ar Goron Dutse, tsakanin malamai da kungiyoyin dalibai. BATULU kuma ya kunshi jigon rarrabuwar jama’ar garin Kano tsakanin ’yan boko da malaman addini da ’yan kasuwa (wadanda aka fi sani da ‘alhazan birni’), inda ya kyankyashi jayayya da gasa da ke tsakanin wadannan rabe-raben, ko gungu-gungun al’umma, wajen neman abin duniya.

Duk wadannan jigogin marubucin ya tubka su cikin labarin da ya bayar ta hanyar alakanta su da taurari daban-daban, kamar abokanai da kawaye da malamai da ma iyayen manyan taurarin littafin. Haka jigogin da suka shafi al’adu sanannu ne ba sababbi ba ga yanayin rayuwar garin Kano da ma na sauran al’umma baki daya.

Marubucin ya gabatar da zubi da tsarin BATULU daidai yadda ya dace da yanayin halayyar taurarin littafin da kuma yadda karshen labarin ya kasance. Ta yadda mai karatu zai kagara ya ga yadda za ta kaya, tare da jefo ba-zata a wasu lokutan. Ya kuma yi amfani da nau’o’in hatsari wajen kawar da wasu taurarin wadanda ci gaba da kasancewarsu, za ta haramta warware sarkakiyar cikin littafin. Misali, boren daliban jami’ar Goron Dutse ne ya kawar da Tanko daga labarin, kamar yadda faduwar Salisu jarrabawa ta kawar da shi daga labarin. Haka shiryeyyen tashin hankalin ashararai da ’yan iskar garin Kano ya kawar da Malam Bello daga labarin.

Shi dai Littafin BATULU an gabatar da shi ne a jami’ar Goron Dutse da ke garin Kano. Kusan duk manyan abubuwan da suka wakana a nan suka wakana, sai wanda ba a rasa ba. Wannan kamar wani sabon abu ne. Domin yawancin marubuta suna amfani da sunayen kirkira ne, ba sunayen gaske na garuruwan da aka sani ba. Hakan ta sa mai karatu ganin kamar yana cikin labarin, musamman idan a Kano ya ke zaune, ko ya san garin.

Saura da me? Sai masu karatu su nemi BATULU, don ganewa idanuwansu, kacokan, wainar da ake toyawa a jami’ar Goron Dutse ta Kanon Dabo birni.


Ana iya yin oda daga Kamfanin ABU Press Limited Zaria, ko Kamfanin Rariya Media Services Ltd, Lamba 53, Titin Mombolo, Wuse Zone 2, Abuja.

Don karin bayani za a iya kira ko a yi tes ga wadannan lambobi: 08032493020, 08037039914, 08065949711 ko a aika da imel ga: adnanwar@live.com; abupress2005@yahoo.co.uk; abupress2013@gmail.com

Saturday, January 18, 2014

A MUST READ MESSAGE: Are You Ready For Your Turn?

He was a student, probably in his early twenties. I didn't know his name I really didn't care. All I know is he was going for a lay-up while playing basketball, lost his balance and fell on the ground flat on his back.

We thought he would shake it off and continue the game so no one really cared. To everyone's surprise, he never got up. At first a few people on his team (later everyone) went up to him but he just wouldn't respond.

CPR did no good. The ambulance personnel couldn't save him from dying. The result at the ER was no better. HE WAS DEAD!

As I came home tonight, I thought to myself, it could have been me going up for that lay-up. It is very possible that I could be lying in the cold city morgue, right this minute, as I type this post to my friends on Facebook.

So am I ready to die? Did I communicate with Allah today? Did I perform my daily prayers? Did I seek the pleasure of Allah? Turkashi!

Did I treat my parents and family with respect and love? Did I give any at all in charity (Sadaqa) today? How many times did I remember Allah and recount His name?

The entire day I made time to go to Shehu Yar'adua Center for #GenVoices, check my e-mails, read the news, update posts on facebook, twitter, chat with friends, watch TV, play football... But did I even once say "Astagfirullah?" Did I ask Allah to forgive the sins that I've committed today? NO! I doubt.

Did I say "Alhamdulillah" other than in my daily prayers? NO! Not once my friends, I told you the truth. Would you like to know why? Because I was too busy with my daily activities.

Well, guess what. I could have lost my life during a playing football game and what do I have with me? Not a thing. Nothing that I did today do I get to bring with me to the grave. Nothing.

A few words that I could have uttered were the only things that I could have brought with me. A few words that would've taken a few seconds of concentration out of the 24 hours that was allotted to me.

A few cents in charity instead of cold drinks and candy bars could have saved my soul. But I insisted on continuing with my careless attitude. Thank God it wasn't my turn to go, because I sure I wasn't ready.

Now I close my eyes and say Alhamdulillah. Now I look back and say Astagfirullah. Now I have a different attitude. Now, I want to prepare for my turn.

Did you perform your daily prayers today? Did you give in charity and love? Did you ask for forgiveness yet? Do you care? I'm asking because I don't want to see you fall, knowing you aren't ready for your turn.

Are you ready for your turn?

Ya Allah ya baibaye mu da rahamarsa. Ya gafarta mana zunubanmu. Ya sa mu yi kyakkyawan karshe.

Yours forever @BashirAhmaad