Wednesday, May 4, 2011

INA MAFITA MATASAN AREWA?

Matasan Arewa gaisuwa gareku, ya
zabukan da suka gabata? Matasan
Arewa, mafi yawancinmu Hausawa ne
kuma mabiya addini daya wato
Musulunci sannan masu akida daya
wato akidar son ganin Nigeria ta
cigaba, ana gogayya da ita cikin
manya manyan kasashen duniya
masu tattalin arziki, kamarsu America,
England, Germany da sauransu.
Shin yaushe wannan buri namu da
muke ta mafarki da muradi zai cika?
Shin kuma wace irin gudunmawa
zamu bayar wajen ganin wannan buri
ya cika? A tunani bamu da wata
gudunmawa illa ta zaben shugabanni
nagari, tabbas munyi hakan har karo
uku amma Allah bai cika mana
wannan buri ba (wato shugaban da
muke ganin shine nagari Allah bai
bashi nasara ba karo ukun) kuma
gashi ahalin yanzu ya sanar da ajiye
muradinsa nason zama shugaban
namu ba don ya karaya ba sai don
yawan shekaru.
To yanzu wane mataki kuma ya dace
mu dauka nan gaba, kowa yana sane
da yadda wannan kabila tamu ke
zama koma baya a ko yaushe a kasar
nan, alhali mune mafiya rinjaye,
Hausawa ya kamata mu farka baccin
ya isa haka kafin lokacin da za'a zo a
tashe mu ace mu ba yan kasar bane,
Eh mana tabbas idan zamu tafi a haka
to nan gaba za'a ce Hausawa ba yan
Nigeria bane.
A tunani na mafita itace mu shiga
wayar da kan yan uwanmu matasan
Arewa, game da halin da wannan
kabila ke ciki, kowa yana sane da
cewa ba wata kabila a kasan nan da
bata da iyaye sai kabilarmu ta Hausa,
wadanda suke ikirarin sune iyayen to
dasu akewa kabilar zagon kasa, kuma
kowa yasan haka. A duk cikin
Hausawa babu wani mutum guda
daya da yake kare wannan kabila da
kuma kwato mata hakkinta.
Hakan tasa mu matasa ya zame mana
dole mu tashi mu karbi jagorancin
wannan kabila mu kwace ta daga
hannun makiyanta, idan kuwa ba
haka ba, wata ran za'a wayi gari
zaman Nigeria yayiwa Bahaushe
wuya. Mu tashi muyi gwagwarmaya
dan kwato hakkinmu a wurin masu
siyar mana dashi.
"Mu tashi mu farka yan Arewa mu bar
bacci aikin kawai ne" Mamma Shata.
Allah ubangiji ya bawa Arewa
jagorori nagari, masu kishinmu,
al'adarmu da addininmu. Amin.

SHIN OSAMA BIN LADEN YA RASU KO YANA RAYE?

Osama Bin Laden shine mutumin da
kasar America tafi kishirwar ganin ta
kama shi ko da rai ko babu, saboda
zargin shi yakai harin 11 September
2011 kan cibiyar kasuwancin duniya
dake America. Kuma suna ikirarin
shine shugaban 'yan ta'adda na
duniya.
A yau ne (2nd May 2011) da sanyin safiya shugaban
Kasar America Barack Obama ya bada
sanarwar cewa sojojinsa na
musamman sun kashe shugaban
kungiyar al-Qa'ida Osama Bin Laden a
wani gida dake Birnin Islamabad dake
kasar Pakistan.
Wannan sanarwa ta dauki hankalin
dukkan wani mutum dake bibiyar
siyasar duniya, wasu sunyi jimamin
abin da Allah-wadai akan wannan
munmunan aiki, wasu kuma sunyi ta
murna da jinjinawa America, akan
wannan namijin kokari da tayi, domin
suna ganin shine ya hanasu jin dadin
rayuwarsu taduniya.
Amma kuma wasu basu ma yarda da
cewar an kashe Osaman ba, saboda
rashin nuna gawarsa da ba'ayi ba.
Amma sojojin kasar American sunce
bayan sun kashe shi sunyi masa
jana'iza kamar yadda addinin
Musulunci ya koyar sannan suka
bunne shi a cikin teku.
Tabbas idan kayi nazari akan abin
zaka gane akwai wani abu a kasa,
abin mamaki ne ace a yadda America
ke neman Osama ruwa a jallo ko a
mace ko a raye, amma su samu
nasarar kashe shi basu nuna kawarsa
ba. Dukkan mai hankali yasan ba'a
binne mutum cikin ruwa kamar yadda
suka sanar.
A karshe wani abin haushi wai duk
kasashen Musulmi na duniya da
kungiyoyin Musulmi ba wata da ta fito
tayi suka akan wannan abu, su kuwa
shugabannin kasashen duniya sai
turawa da sakon goyan baya suke ga
kasar America, wai yanzu duniya zata
zauna lafiya tunda an kashe shugaban
yan ta'adda.
Allah ya taimaki Musulunci da
Musulmai a ko ina a fadin duniya.
Allah ya karawa kasashen kafirai
tsoron Musulmai. Ameen.