Monday, October 22, 2012

Wacece Safeena Buhari? - Daga Yasir Ramadan Gwale

Safeena Buhari diya ce ga Gen Muhammadu Buhari. Abin da yake faruwa shine akwai wata baiwar ALLAH da watakila 'yan uwa suke ganin post dinta a koda yaushe a facebook da wannan suna na Safeena Buhari, mun yi kokari domin gano shin da gaske safeenan Gen Buhari ce ko kuwa ta karya ce, Alhamdulillah wakilinmu ya je har gidan Gen Buhari a kaduna inda aka tabbatar masa da cewar wannan Safeena Buhari da muke ganin a fzbk ba ita ce ba.

Wato muna da yawa wadanda muke musayar kalamai da ita ta bayan fage wato Inbox, na taba tambayarta tsakaninta da ALLAH ita diyar General ce, ta yi min rantsuwa akan cewa ita diyarsa ce, wanda sakamakon bincikenmu ya tabbatar mana da cewa karya take.

Abinda yake faruwa shine, kusan da yawanmu da muke magana da ita ta shaidamana cewar tana aiki a QATAR amma kuma yanzu tana zaune a Germany sakamakon jinyar mijinta, wasu kuma ta shaidamusu cewar tana England, akwai daga cikinmu wadanda ta yaudara da sunan zata samar masa da Scholarship dan su yi karatu a QATAR, haka kuma tayi wa wani alkawarin tuntubar Sarkin DUBAI domin nema masa taimako, duk da take yin wadannan maganganu da alkawura, mu tuni mun gane ta, kawai shiru muka yi mata, amma kuma yanzu lokaci yayi da muke ganin ya kamata mu bankada wannan Asiri, domin ta fara yaudarar wasu da samar musu da kwangilar harkar mai a kasashen larabawa, wanda idan muka ci-gaba da yin shiru zata bata sunan Gen Buhari ne, kuma zata damfari wadanda basu santa ba, haka kuma itace dai take amfani da wani account mai suna YUSUF BUHARI wanda shima dane ga Gen Buhari amma bai da masaniyar ana amfani da sunansa anan facebook.

Dan haka jama'a a kiyaye Mu'amala da ita, domin ba Safeenar gaskiya bace, watakila wani Dan iskan kato ne yake amfani domin ya bata musu suna kuma ya nemi abin duniya. Hakika mai amfani da wannan suna na Safeena Buhari yana da masaniyar gidan Buhari sosai, dan kawai ya samu ya ci-kasuwarsa, a kwanakin baya ta sanya wani hoto na Matar Gen Buhari da matar Tunde Bakare da kuma Safeena Buhari ta ainihin, idan kuka duba Profile dinta zaku gani. Muna addu'ar duk wanda yake wannan danyan aiki ALLAH ya shirye shi, idan kuma ba mai shiryuwa bane, ALLAH ya shiga tsakanin nagari da Mugu.

Sunday, October 21, 2012

Gwamnonin Kasar Nan Da Suka Fi Bajinta

Sakamakon binciken da wata kungiya mai suna Eagle Eyed Youth Association of Nigeria tare da hadin gwiwar kungiyoyin sa kai fiye da 100 da kuma jin ra'ayoyin jama'a a sassan kasar nan daban - daban, ya bayyana sunayen gwamnoni a kasar guda 10 da suka fi yiwa talakawansu aiki. Gwamnonin su ne: 1) Dr. (Barr) Ibrahim Shehu Shema, na jihar Katsina. 2) Barr. Babatunde Raji Fashola na jihar Lagos. 3) Chief Rochas okorocha na jihar Imo. 4) Alh. Aliyu Wamakko na jihar Sokoto. 5) Eng. Rabi'u Musa Kwankwaso na jihar Kano. 6) Alh. Tanko Al Makura na jihar Nasarawa. 7) Dr. Rotimi Amaechi na jihar Rivers. 8) Rear Admiral Murtala H. Nyako na jihar Adamawa. 9) Alh. Sule Lamido na jihar Jigawa. 10) Comrade Adams Oshiomole na jihar Edo. Shin a naku ra'ayin wannan sakamako yayi daidai ko da son zuciya a cikinsa? Idan akwai son zuciya a naka ra'ayin wane gwamna ya kamata ya zama a matakin farko?

Saturday, October 13, 2012

Sarkin Kano Ya Cika Shekaru 49 Akan Gadon Sarauta

Allah mai yadda ya so. A yau Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji (Dr.) Ado Bayero ya cika shekaru 49 akan gabon sarauta (13 Oktoba 1963 - 13 Okboba 2012) Idan Allah ya kaimu shekara mai zuwa zai cika shekaru 50 daidai wato rabin karni akan gadon na sarauta. A madadin ni kaina da sauran maziyarta wannan shafi muna taya Mai Martaba San Kano da sauran daukakin jama'ar Kano munnar wannan rana. Allah ya karawa Sarki lafiya da imani, Allah ya bamu zaman lafiya da kwanciyar hankali a jiharmu Kano da kasarmu Nijeriya baki daya. Bashir Ahmad