Tuesday, November 13, 2012

Kotu Ta Yanke Wa Jarimi Sani Musa Danja Hukunci Daurin Shekara Guda A Gidan Yari

Kotun tafi da gidanka ta Hukumar tace finafinai ta jihar Kano ta yankewa shahararren dan wasan kwaikwayon nan na Hausa Sani Musa Danja daurin shekara guda a gidan yari.

Kotun ta daure Sani Danja ne sakamakon fitar da wani fim din sa mai suna Gudaliya ba tare da bin dokar hukumar tace finafinan ta jihar Kano ba, wanda hakan ya sabawa dokar hukumar ta sashi na 100 (2) ta shekarar 2001, sannan hukuncin da aka yanke masa na karkashin sashi na 112 na kundin tsarin mulkin hukumar.

Bayan samun sa da laifin, alkalin kotun mai shari'a Mukhtar Ahmad ya yanke wa Sani Musa Danja hukuncin zaman yari na tsawon shekara guda ko kuma biyan tarar N30,000, karkashin sashi na 157 na kundin hukunta masu laifuka, na shekara ta 2001.

Yan Fashi Sun Kai Farmaki Kasuwar Chanji ta Wapa a Jihar Kano

Da tsakar ranar Talatar nan ne wasu yan fashi da makami suka kai farmaki kasuwar yan chanji dake Wapa a birnin Kano. Yan fashin su kimanin 9 da suke akan babura da kuma mota kirar Golf sun ringa harbi babu kakkautawa a kasuwar daga bisani suka kutsa cikin wani shago suka yi awon gaba da miliyoyin kudi da har yanzu ba a tantance yawansu ba.

Shugaban kasuwar Wapa Alhaji Auwal Umar Nagari ya bayyana takaici bisa rashin isowar jami'an tsaro akan lokaci da kuma yadda yan fashin suka bar wasu kwanson harsasai mai dauke da tambarin 'yan sanda lamarin da yasa suke zargin kodai akwai lauje cikin nadi. yawan fashi a kasuwannin jihar Kano dai wani babban al amari ne da a yanzu ke nema zama ruwan duk da yawan jami'an tsaro dake baje a hanyoyin jihar.

Freedom Radio FM, Kano

Kano tribunal jails Sani Danja

Kano State Censorship Tribunal sitting has sentenced popular Hausa film actor, Sani Musa Danja to one year imprisonment.Sani Danja was sentenced yesterday for exhibiting for sale an uncensored and unlicensed copy of a film titled “Gudaliya” in contravention of Section 100 (2) of the state Cinematography Censorship Regulation 2001 and punishable under Section 112 of the same law.

He pleaded guilty and asked the court for leniency. Senior State Counsel Hussain Hassan therefore applied for summary trial under section 157 of the criminal procedure court. Chief Magistrate Mukhtar Ahmed sentenced him to one year imprisonment or to pay a fine of N30,000.

Culled: Daily Trust

Saturday, November 10, 2012

Yau Jama'a Za Su Bayyana Ra'ayoyinsu Ga Gyaran Kudin Tsarin Mulkin Kasa

Yau ne, abisa mafi yawancin sanarwar da ake ta bayarwa, za a fara jin ra'ayoyin al'umma don gyaran kundin tsarin mulkin kasa, mai cike da son zuciya da kura-kurai da rashin girmama addinin Musulunci. Wannan yasa ya kamata ga kowa yasan dama ce tazo.

Malamanmu wajibi ne su shiga wannan batu, su fadakar da 'yan majalissunmu Musulmai game da damar da idan har ta kubuce, to ba mu san sai yaushe kuma za ta sake dawo ba! Malamai, 'yan siyasa, masana fannin shari'ar Musulunci, malaman Jami'o'i da makarantun gaba da sakandare, 'yan kasuwa Musulmai (musamman na Arewa), masu tunani a cikin mu, dalibai, da sauran mu............

Wajibi ne a gare mu, abu na farko a kodayaushe da zamu ke kula dashi: Addininmu! (Musulunci) sannan, Al'ummarmu (Hausawa) sannan yankinmu (Arewa) dole ne a ba mu damar yin rayuwa kamar kowa, a dai na kashe mu, a dai na cin zarafinmu.

A ba mu damar amfana da arzikin kasarmu kamar kowa, da duk wani abu wanda mai kyau ne ga addininmu da al'adarmu. Don Allah, kada musulmai su kara mika wuya ga secularism, wanda kowa yasan kai tsaye yayi kamanceceniya da kafirci!!!

(Sunnah Akhabariyah)

Friday, November 9, 2012

'Yan Kasa Ne Za Su Gyara Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya

Kamar yadda mu ka sani, Majilisar Dokoki ta kasa ta na shirye - shiryen sake yin gyare - gyare ga Tsarin Mulki na Shekarar 1999.

Wannan gyare - gyare sun shafi harkokin siyasa, tattalin arziki, zaman takewa da kuma tsarin yadda a ke tafiyar da Gwamnati. A cikin shirye - shiryen gyaran Tsarin Mulkin, Majilisar Wakilai ta Tarayya ta yanke qudurin cewa gyaran da za ta yi wa Tsarin Mulkin zai sami gudunmuwa daga Jama'ar kasa ne.

A bisa wannan ne Majalisar ta fitar da cewa duk abinda za'a yi gyara a kansa sai kowanne 'Dan Majalisa ya je Maza'barsa ya tattauna da Jama'ar da ya ke wakilta don jin ra'ayinsu a kan wa'dannan abubuwa. Idan ba'a sami ha'duwar ra'ayi ba sai a yi quri'a wanda ya fi rinjaye shi ne matsayin wannan Maza'ba a kan gyaran Tsarin Mulkin.

Bayan an kammala wannan tarurruka na Maza'bu, za'a tattara sakamako a kai Majalisa wanda wannan sakamakon ra'ayin Jama'a ne Majalisar Tarayya za ta yi amfani da shi a kan abubuwan da a ke son yin gyara a kan su.

Wa'dannan tarurruka na Maza'bu an ware ranar Asabar 10 ga Nuwamba, 2012 dan yin su a fa'din qasa ba ki 'daya a lokaci guda. An fitar da sanarwa ta musamman a gidajan radiyon yankuna - yankuna da sauran kafafan ya'da labarai dangane da wa'dannan tarurruka da kuma inda za'a yi su a kowacce Maza'ba ta Tarayya. Akwai bukatar mu halacci wa'dannan tarurruka a dukkanin Maza'bunmu dan ganin cewa ba mu bari wasu sun ari bakin mu sun ci ma na albasa ba.

Thursday, November 1, 2012

Sanarwa: Daurin Auren Gali Da Gimbiya Asma'u

To fa. . . . Bari dai na fara da mabudin kunne kafin na zarce inda na nufa “Aure rufin asirin Musulmai” na san daga jin wannan karin waka da yawa daga cikinmu za su fuskanci inda na nufa, hmmm! Kar dai kuce na cika ku da surutu bari na tafi kai tsaye:

Muhammad Gali Abubakar ne da amaryarsa Asma'u Lawan Hamza (Ummi) cike da farin ciki marar misaltuwa suke gayyatarku domin kuyi tururuwa da dafifi zuwa shaida daurin aurensu.

An tsara za a gudanar da bikin kamar haka: Rana: Juma'a 2/11/2012 = 17/12/1433

Wurin Haduwa: Za a hadu a Goron Dutse Bayan Wreca Kano, Gidan Gwani Malam Lawan Gaya

Wurin Daurin Aure: Sheka Baranda Unguwar Kudu Kano, Gidan Malam Lawan Dan Gaya Ango da amarya na cike da fatan dukkanku zaku dungumo ku shaida wannan daurin aure na su tare da taya su adduar fatan alheri.

Dandali ya samu wannan sanarwa ne daga Lawiza da Hauwa 'yayan Murtala Jar Kasa, Zuru, Jihar Kebbi.