Friday, September 14, 2012

Na Yi Nadamar Yin Zanga - Zangar Janye Tallafin Man Fetur


Ban taba tunanin zan yi nadamar kasancewa daya daga cikin miliyoyin jama'ar kasar nan da suka gudanar da zanga - zangar nuna rashin amincewa da kudirin gwamnatin tarayya na janye tallafin albarkatun man fetur ba, hasalima a kullum na tuna lokacin sai naji nishadi ya baibaye dukkan zuciyata koda kuwa ina cikin yanayin bakin ciki ne, kai har alfahari nake da lokacin musamman ranar da ni da wasu jajirtattun matasa muka fita shatale-talen Silver Jubilee dake tsakanin fadar masarautar Kano da fadar gwamnatin Kano da daddare da niyyar kwana a filin duk don mu nunawa duniya cewar bama goyon bayan kudirin na gwamnati, duk da bamu yi nasarar kwana a wurin ba kamar yadda muka shirya yi sakamakon jami'an tsaro da suka tarwatsa mu cikin talatainin dare da harbin harsashi da barkonon tsohowa.

Ba komai yake sani alfahari da ranar ba, sai don a tarihin Nijeriya mu kadai ne muka taba yunkurin yin hakan duk kuwa da bamu yi nasarar kwana a wurin ba. Amma duk da irin jami'an tsaron da aka jibge a Silver Jubilee a lokacin sai da washe gari jama'a suka sake fitowa nuna rashin goyon bayansu duk saboda a tunaninmu idan gwamnati ta janye tallafin man fetur din nan zamu shigo wani sabon kangi na wahalhalun rayuwa, to a karshe dai gwamnatin ba ta fasa aiwatar da kudirin na ta ba, sai dai 'yar kwaskwarima kadan da tayi masa, wadda wasu ke alakanta hakan da zanga - zangar da muka yi a sassa daban - daban na kasar nan.

Kamar yadda na fada a baya bana tunanin zan taba yin nadamar yin hakan a sauran rayuwata da ta rage, wanda nasan kuma ba za ku ga laifina ba, saboda kuwa na nuna kishin kasata da kokarin kwatowa talakawa 'yanci, wadanda wahalhalun da muke tunanin za a shiga za ta fi shafa, sai ga shi lokaci daya nadamar yin hakan ta wanzu cikin zuciyata ta hanani sukuni da jin dadin rayuwata.

Tun a ranar da tsinannun kafiran Amurka suka fito da wani yanki daga cikin wasan kwaikwayon da suka shirya mai taken Innocence of Muslims wanda suka shirya isgilanci da batancin da ba'a taba yin irin sa a tarihin duniya ba akan Annabi Muhammad (SAW) na shiga wannan nadama tawa, ba don komai ba sai a duk lokacin da na kamo gidajen television da suke nuna labaran da suka shafi duniya sai naga ba labarin da suke nunawa sai zanga - zangar da ake kan gudanarwa a kasashen larabawa sakamakon shirya wannan wasan kwaikayo, sai naga cewa shin mu menene dalilin daya sa bamu fita zanga - zangar ba domin nuna rashin amincewarmu akan fim din, saboda fita wannan zanga - zangar itace mai asali da kuma tushe ba wadda muka yi a baya ba.

Kowace kasa aka nuno za ka ga manyan malamai da attajirai sune a sahun gaba, ana kona tutar Amurka da yin tofin alatsine a gare su, a kasar Libya kuwa tun da sanyin safiya suka dauki matakin kashe jakadan Amurka dake kasar, wanda kuma shi ne karo na farko da aka taba yiwa Amurka haka, a kasar Sudan manyan jami'an gwamnatin kasar ne suka shirya zanga - zangar, haka kasar Egypt, Tunisia, Pakistan, Iran, India, Morocco, Syria da sauran kasashe masu kishin addinin Islama.

To a Nijeriya fa???

Ina malamanmu suke? Menene dalilansu nayin shiru akan wannan maganar, shin ko sun manta da cewa wannan maganar ta fi karfi a yi shiru a barta a fatar baki? Menene dalilin da zai sa su zauna a gida ba zasu fito su jagorance mu ba, mu shiga sahun miliyoyin Musulmai duniya wurin yin Allah wadai ga Amurka?

Ya Allah ka gaggauta daukar mataki mummuna akan dukkan wanda yake da hannu a cikin shirya fim din.

No comments:

Post a Comment