Saturday, November 10, 2012

Yau Jama'a Za Su Bayyana Ra'ayoyinsu Ga Gyaran Kudin Tsarin Mulkin Kasa

Yau ne, abisa mafi yawancin sanarwar da ake ta bayarwa, za a fara jin ra'ayoyin al'umma don gyaran kundin tsarin mulkin kasa, mai cike da son zuciya da kura-kurai da rashin girmama addinin Musulunci. Wannan yasa ya kamata ga kowa yasan dama ce tazo.

Malamanmu wajibi ne su shiga wannan batu, su fadakar da 'yan majalissunmu Musulmai game da damar da idan har ta kubuce, to ba mu san sai yaushe kuma za ta sake dawo ba! Malamai, 'yan siyasa, masana fannin shari'ar Musulunci, malaman Jami'o'i da makarantun gaba da sakandare, 'yan kasuwa Musulmai (musamman na Arewa), masu tunani a cikin mu, dalibai, da sauran mu............

Wajibi ne a gare mu, abu na farko a kodayaushe da zamu ke kula dashi: Addininmu! (Musulunci) sannan, Al'ummarmu (Hausawa) sannan yankinmu (Arewa) dole ne a ba mu damar yin rayuwa kamar kowa, a dai na kashe mu, a dai na cin zarafinmu.

A ba mu damar amfana da arzikin kasarmu kamar kowa, da duk wani abu wanda mai kyau ne ga addininmu da al'adarmu. Don Allah, kada musulmai su kara mika wuya ga secularism, wanda kowa yasan kai tsaye yayi kamanceceniya da kafirci!!!

(Sunnah Akhabariyah)

No comments:

Post a Comment