Sunday, October 12, 2014

Abin Da Janar Buhari Ya Fada Min

Janar Muhammadu Buhari, bai da mantuwa, ya fada min magana kusan shekaru biyu, jiya muna haduwa, ina gaida shi, ya sake maimaita min wannan magana.

Mun hada da Janar jiya a Owerri jihar Imo, wurin daurin auren 'yar Gwamna Rochas Okorocha, a lokacin da naje gaida shi na yi tunanin ya manta sunana, ashe bai manta ba, yana kallo na ya ce Bashir, na durkusa na gaida shi, na tambaye shi kanwata Fatimatu Buhari (Karamar 'yarsa) ya ce tana lafiya.

Ga mamakina sai na ji ya ce "Bashir, Nijeriya fa ta ku ce" maganar ta ban mamaki sosai, saboda ba a lokacin ya taba fada min hakan ba, sannan ya ci gaba da cewa "dole ku so ta, ku sa ta a zuciyarku, ku kyautata mata, sannan ku yi sadaukarwa a gare ta, haka ne zai sa ita ma a nan gaba ta kyautata muku".

Duk da ba kowa ya ji maganar da yake fada min ba, sai wadanda suke kusa da shi, shugaban jam'iyyar APC, Cif John Oyegun da matarsa, su kuma ba Hausa suke ji ba, amma na ga idanun mutane, cikin har da gwamnoni suna kallon mu... Ban sani ba ko tunani suke Baba Buhari yana cewa Bashir kai zaka gaje ni... (Dariya)!

Ba iya wadannan maganganun Buharin ya fada min ba, amma sauran na dauke su a matsayin sirri, ya fada ne a kaina, ni kuma ina gani idan na fito na fadi, wasu za su ga kamar na yi alfahari...

...Allah ya karawa Janar Buhari lafiya, Ya kara masa nisan kwana mai amfani.