Thursday, April 29, 2010

KANO STATE LOCAL GOVERNMENT AND THEIR CODES


Kano State Is The Highest Population And Its Has Most Local Government In Nigeria.
The Name Of Kano State Local Government is:

(1) Ajingi AJG
(2) Albasu ABS
(3) Bagwai BGW
(4) Bebeji BBJ
(5) Bichi BCH
(6) Bunkure BNK
(7) Dala DAL
(8) Dambatta DBT
(9) Dawakin Kudu DKD
(10) Dawakin Tofa DTF
(11) Doguwa DGW
(12) Fagge FGE
(13) Gabasawa GSW
(14) Garko GAK
(15) Garun Mallam GRL
(16) Gaya GYA
(17) Gezawa GZW
(18) Gwale GWL
(19) Gwarzo GRZ
(20) Kabo KBK
(21) Kano Munincipal KMC
(22) Karaye KRY
(23) Kiru KKU
(24) Kibiya KBY
(25) Kumbotso KBT
(26) Kunci KNC
(27) Kura KUR
(28) Madobi MBD
(29) Makoda MKD
(30) Minjibir MJB
(31) Nassarawa NSR
(32) Rano RAN
(33) Rimin Gado RMG
(34) Rogo ROG
(35) Shanono SNN
(36) Sumaila SML
(37) Takai TAK
(38) Tarauni TRN
(39) Tofa TFA
(40) Tsanyawa TYW
(41) Tudun Wada TWD
(42) Ungogo UGG
(43) Warawa WRA
(44) Wudil WDL

Thursday, April 22, 2010

SAHABBAI GOMA YAN ALJANNA TUN SUNA DUNIYA


Manzon Allah (S.A.W.) yana da Sahabbai 120,4000. Duk da cewa dukkan wadannan Sahabbai 'yan Aljanna ne to amma akwai wadanda akayi musu bishara da Aljanna tun suna da rai.
Akwai guda goma wannan Manzon Allah (S.A.W.) ya fada a hadisi cewa an yi musu bishara da gidan Aljanna, wato ASHARATUL MUBASHSHIRUN. Wannan Sahabbai sune:-
(1) Abubakar Saddik (R.T.A)
(2) Umar Bin Khaddab (R.T.A)
(3) Usman Bin Affan (R.T.A)
(4) Aliyu Bin Abi Dalib (R.T.A)
(5) Dhalha Ibn Ubaidullah (R.T.A)
(6) Zubair Ibnul Awwam (R.T.A)
(7) Abdurrahman Bin Auf (R.T.A)
(8) Sa'ad Bin Wakkas (R.T.A)
(9) Sa'id Bin Zaid Bin Amr (R.T.A)
(10) Abu Ubaidah Bin Jarrah (R.T.A)

Allah Madaukin Sarki ya bamu albarkacin wadandan bayi nasa.

KALANDAR HIJRAR MUSULUNCI


Abin mamaki a wannan zamanin sai kaga an tambayi mutum yau nawa ga wata sai kawai kaji yace "yau 21 April 2010" da ka ce masa a'a na Musulunci kake nufi sai kaji yace "ban sani ba" wannan gaskiya abin kunya ne ga dukkan Musulmin da za'a tambaye shi kwanan watan turawa ya fadi amma ya kasa fadin na Hijrar Musulunci.

TARIHIN HIJRAR MUSULUNCI

Asalin faruwar Kalandar Hijrar Musulunci, abu ne mai fadi da dogon tarihi, amma dai ta samu asalinta ne lokacin Khalifancin Sayyadina Umar Bin Khaddab (A.S.) a sakamakon wani abu mai muhimmanci daya faru a cikin watan Sha'aban wanda Sahabbai suka yi kokarin tantance wane Sha'aban ne amma abin ya faskara. Wannan dalili ne yasa Sayyadina Umar (A.S.) ya tara Sahabbai inda ya nemi shawarar yadda za'a rika tantance tarihin faruwar al'amura a Musulunci.

Don haka shawara ta tsaya akan fara lissafin kalandar Musulunci daga lokacin da Manzon Allah (S.A.W.) yayi hijra daga Makkah zuwa Madinah, kuma aka sanya watan Muharram ya zama shine watan farko a cikin jerin watannin kalandar Musulunci (Hijrah).

WATANNIN HIJRAR MUSULUNCI

Shekarar Musulunci (Hijrah) tana da watanni goma sha biyu 12 wadannan watanni sune:-
(1) Muharram
(2) Safar
(3) Rabi'ul Awwal
(4) Rabi'ul Thani
(5) Jumada Ula
(6) Jumada Thani
(7) Rajab
(8) Sha'aban
(9) Ramadan
(10) Shawwal
(11) Zhul Qi'idah
(12) Zhul Hajj

WATANNI HUDU MASU ALFARMA

A cikin watanni Hijrar Musulunci guda 12 Allah Madaukakin Sarki ya kebance guda hudu masu Alfarma, sune:-
Muharram wata na (1)
Rajab wata na (7)
Zhul Qi'idah wata na (11)
Zhul Hajj wata na (12)

A KARSHE
Shawara ga dukkan Musulmi ya dage ya ke sa kwanan watan Hijrar Musulunci a dukkan harkokimu na yau da kullum.
Allah ya daukaka Addinin Musulunci da Musulmai, Ya kare mu daga sharrin makiya Manzon Allah (S.A.W) ameen.

Thursday, April 8, 2010

(EL CLÀSICO) REAL MADRID VS BARCELONA


El Clásico lakabi ne da ake yiwa wani shahararren wasa a bangaren kwallon kafa, wannan wasa shine wasan da yafi kowanne wasa daukar hankalin masu sha'awar kwallon kafa a duniya.

Wannan wasa shine tsakanin shahararriyar kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid CF data fito daga Madrid babban birnin kasar Spain. Da kuma babbar kungiyar FC Barcelona data fito daga Barcelona babban birnin Catalonia dake kasar Spain.

Wadannan kungiyoyi guda biyu sune suka fi kowace kungiya samun nasarori a bangaren kwallon kafa a kasar Spain baki daya.

El Clasico shine wasa mafi daukar hakalin mutane a duniya, domin mutane sama da 100 milliyan suna ganin shi daga kasashen daban-daban a fadin duniya, ciki har da kasarmu Nigeria.

El Clásico ya samo asalin sunansa ne a lokacin da Real Madrid ta samu gagarumar nasara akan Barcelona a wasan kusa da karshe na gasar Spanish Cup.
(11-1) a shekarar 1943.

Real Madrid da Barcelona sune suka fi kowace kungiya magoya baya a kasar Spain.
Real Madrid tana da kaso 32.8%. Sannan Barcelona na da kaso 25.7%. Sai ta ukun su Valencia da kaso 5.3%. Game da kidayar da akayi a shekakar 2007.

Tsakanin Real Madrid da Barcelona an hadu sau 160 a gasar La-liga.

Real Madrid ta samu nasara sau 68. Sannan Barcelona ta samu nasara sau 62. Sunyi kunnen doki sau 30 a tsakaninsu.

Real Madrid ta samu nasara sau 50 a gida, sau 18 a waje. Kunnen doki sau 14 a gida sau 16 a waje. Rashin nasara sau 15 a gida, sau 46 a waje.

Barcelona ta samu nasara sau 47 a gida, sau 15 a waje. Kunnen doki sau 16 a gida, sau 14 a waje. Rashin nasara 18 a gida sau 50 a waje.

Yan wasan da suka fi cin kwallaye a El Clásico sune:

REAL MADRID CF
Alfredo di Stefano (14).
Raùl (11).
S. Bernabeu (11)
Lazcano (8).
Regueiro (6).
Van Nistelrooy (4).
Alday (4).
Zamarano (3).
Ronaldo (3).
Higuain (2).
S. Ramos (2).

FC BARCELONA
F. Gento (10).
Luis Enrique (6).
Lionel Messi (6).
Rivaldo (5).
Ronaldinho (5).
Escola (5).
Ventolra (4).
Samuel Eto'o (4).
Henry (3).
Kluivert (2).

El Clásico wasan daya wuce a Santiago Bernabeu. Real Madrid 0 - 2 Barcelona, Ranar 10 April 2010.

El Clásico wasan da za'ayi nan gaba a Camp Nou. Barcelona - Real Madrid. Ranar 29 November 2010.

Tuesday, April 6, 2010

ALHAJI (DR) MUHAMMAD ABUBAKAR RIMI


Inna lillahi wa inna illahi raji'un.

A dare ranar Lahadi 4 April 2010 ne, Allah (S.W.A.) yayi wa Alhaji (Dr.) Muhammad Abubakar Rimi tsohon gwamnan tsohuwar jihar Kano (Kano da Jigawa) rasuwa.

Akan hanyar sa daga jihar Bauchi zuwa Jihar Kano, bayan ya dawo daga bikin nadin sarautar gargajiya ya hadu da yan fashi a tsakanin garin Garko da Wudil. Duk da yan fashin basu taba shi ba amma za'a iya cewa sune sanadiyar mutuwar sa.

Bayan yan fashin sun karbe musu kudin su da wayoyin su, sannan suka taho kafin suzo Wudil Muhammad Abubakar Rimi ya gamu da bugun zuciya, nan take aka kai shi asibitin Koyarwa na Malam Aminu Kano. Wajen karfe 11:40 na dare Allah ya karbi ransa.

Washe garin ranar da ya rasu akayi jana'izar sa, a fadar Mai Martaba Sarkin Kano.
Jana'izar Muhammad Abubakar Rimi ta samu halartar mutane sama da mutum miliyan daya daga sassa daban-daban na kasar Nigeria baki daya.

TAKAITACCEN TARIHIN ALHAJI MUHAMMAD ABUBAKAR RIMI

An haifi Muhammad Abubakar Rimi a kauyen Rimi na karamar hukumar Sumaila, jihar Kano, Nigeria. A shekarar 1940.
Alhaji Abubakar Rimi na daya daga cikin manya-manyan fiatattun kuma jiga-jigan yan siyasar nahiyar Afrika. Yayi karatun sa na Kos a Zaria, kuma ya samu takardar shedar zuwa jami'ar London, kasar England a 1972. Ya hada diflomar sa a kasar kuma ya samu shedar babban digri.

Rimi yana daga cikin mutanen da suka kirkiri jam'iyyar PRP a shekarar 1978 kuma an zabe shi a matsayin mataimakin jam'iyyar na kasa a taron ta na farko a jihar Lagos.

Abubakar Rimi an zabe shi a matsayin gwamnan tsohuwar jihar Kano a October 1979 har zuwa May 1983 kuma shine gwamnan farar hula na farko a jihar. A farko 1983 Rimi ya fita daga jam'iyyar PRP ya koma Nigerian People's Party (NPP).

A lokacin mulki Rimi yayi wa jama'ar jihar Kano da Jigawa aikin da wani gwamna bai taba yi ba.
Muhammad Abubakar Rimi shi ya gina gidan jaridar jihar Kano Triumph, ya gina gidan television na CTV Kano, ya gina Kasco da kuma Knarda.

Rimi a lokacin mulkin sa ne ya kirkiro sabbin masarautu na sarakunan yanka. Kamarsu: Kano, Gaya, Rano, Karaye, Auyo da Ringim.

A 1993 Rimi ya zama ministan yada labarai sannan ya zama shugaban NACB da NSPMC. yana cikin mutanen da suka samar da jam'iyyar Peoples Democratic Party (PDP).

Rimi ya fita daga Jam'iyyar PDP a 2006 ya koma jam'iyyar Action Congress (AC) amma a 2007 Rimi ya sake komawa PDP.

A january 2006 wasu yan ta'adda suka shiga gidansa suka kashe masa matar sa Sa'adat Abubakar Rimi.

Ranar 4 April 2010 ya rasu a asibitin Mallam Aminu Kano. An bunne shi ranar 5 April 2010 kamar yadda Addinin Musulunci ya ta nada.

A karshe Allah ya jikansa, Allah ya kai rahma kabarin sa, Ya saka masa da gidan Aljanna firdausi. Ya baiwa iyalansa hakurin jurewa.