Sunday, June 17, 2012

Wa Ke Da Alhakin Tashin Bama - Bamai A Kaduna?


Yau mutanen arewacin Kaduna sun ga tashin hankali, sakamakon tashin wasu bama bamai a wasu majami'u a birnin Zaria da cikin garin Kaduna, wanda hakan ya haifar da asarar rayuka da dokiyoyi masu yawa, dalilin faruwar wannan al'amari ya sa wasu matasan kiristoci sanya shingaye akan titunan da zasu dawo da matafiya Kaduna daga Abuja, da suna daukar fansa, saboda a zargin su Musulmai ne suke da alhakin faruwar al'amarin. Duk kuwa da cewa ba sau daya ko sau biyu ba ana kama kirista da bam na kokarin sanyawa a coci.

Bayan isar wannan mummunan labari cikin kunnuwa na, ba komai zuciyata ta fara tuno min da shi ba, sai wata magana da shugaba Goodluck Jonathan ya bayyana a kwanakin baya da yake tabbatarwa 'yan Nijeriya cewa gwamnatinsa za ta kawo karshe da murkushe kungiyar nan ta Boko Haram, wadda ake zargi da irin wannan aika aika a sassan kasar nan daban daban, a watan June da muke ciki a yanzu.

Ina tunanin ba komai ya sa zuciyata ta yi saurin tuno min da wannan magana ba sai don sanin ba kowa za a zarga da yin wannan aika aika ba sai kungiyar ta Boko Haram, ba don komai ba, sai don kaurin sunan da tayi akan hakan kamar yadda na fada a baya.

To ana cikin haka, sai wani tunanin ya kara kunnuwa cikin zuciyar tawa hade da tambaya. Shin tunda Boko Haram ta zo karshe a wannan wata, kamar yadda shugaba Jonathan ya dau alwashi, kuma kaso mafi rinjaye na al'ummar kasar nan suka gastata maganar tasa, to wa kuma yake da alhakin kai hare - haren bama baman yau din a Kaduna?

Ya Allah ka kawo mana zaman lafiya a kasarmu.

2 comments:

  1. John Odia ne, sai suyi kokarin tambayarsa sunan sabuwar kungiyar tasa tunda kuwa ba Boko Haram ba ce.

    ReplyDelete