Saturday, January 14, 2012

Yau ma Gwamnati da NLC/TUC basu cimma matsaya guda ba. Yajin Aiki da Zanga Zanga zasu ci gaba Ranar Litinin

Yau ma kamar ranar Alhamis kungiyar Kwadago (NLC) da kungiyar 'Yan kasuwa (TUC) ba su cimma matsaya guda ba a zaman da sukayi da jami'an gwamnatin tarayya akan janye tallafin man fetur da gwamnati tayi da kuma yajin aikin gama gari da kungiyoyin suka kira tun ranar Litinin da ta gabata.

A halin yanzu bamu samu labarin yadda zaman ya kasance ba, amma wani jami'in kungiyar Kwadago ya sanarwa yan jarida cewa yajin aiki da zanga zanga zai ci gaba a ranar Litinin bayan tafiya hutun kwana biyu da akayi domin bada dama ga jama'a su sake shiri. Wannan yana nuna lalle zaman ba'ayi nasara ba.

A yammacin wannan rana ma dai kungiyar PENGASSON mai hakar man fetur ta bada sanarwar tafiya yajin aiki a daren ranar Lahadi idan har gwamnati basu daidai ta da 'yan Kwadagon ba.

No comments:

Post a Comment