Sunday, January 22, 2012

Ba Zamu Janye Yajin Aiki Ba - Shugaban ASUU

Shugaban Kungiyar gamayyar malaman jami'o'in kasar nan ASUU Prof. Ukachuchwu Awuzie ya bayyana cewa ba zasu koma aiki ba daga yajin aikin da suka tafi har sai gwamnati ta biya musu bukatun da suka nema a wurinta. Ba kamar yadda ministan ilimi Prof. Ruqayya Ahmad Rufai ta bayyana ba, cewa malaman zasu janye yajin aikin a koma karatu ranar Litinin, ta bayyana hakan ne a wata hira da tayi da manema labarai bayan fitowa daga wata tattauwa da tayi da wasu daga cikin mataimakan shugabanin jami'o'i a birnin tarayya Abuja.

Amma shugaban na ASUU Prof. Awuzie ya bayyanawa jaridar Leadership a daren jiya cewa kungiyar malamai ba kungiyar mataimakan jami'o'i ba ce, saboda haka basu san maganar janye yajin aiki ba, har sai bukatunsu sun biya.

Prof. Awuzie yace ASUU zasu zauna su tattauna da shugaba Goodluck Jonathan ranar Litinin, kuma da zarar an biya mana bukatunmu to zamu janye yajin aiki su koma aiki.

No comments:

Post a Comment