Thursday, January 12, 2012

Ba'a samu matsaya guda ba tsakanin Gwamnati da 'Yan Kwadago

Zaman da shugabannin 'yan kwadago (NLC) da shugabannin 'yan kasuwa (TUC) da sukayi jami'an gwamnatin tarayya akan tattauwa game da janye tallafin man fetur, da yajin aikin da ma'aikatan kasar nan suka tafi, ba'a samu wata matsaya guda daya ba.

Zaman anyi shine a fadar gwamnatin tarayya dake Abuja (Aso Rock) tun da misalin 5:30 na yammacin wannan rana har zuwa misalin 10:00 na dare, wanda ya hada shugabannin majalissun kasar nan ta dattijai da wakilai (Senates and Reps) da kuma ministar kudi Mrs Ngozi Okunjo-Iweala.

Shugaba Goodluck Jonathan da mataimakinsa Muhammad Namadi Sambo sun bar dakin taro jin kadan da isowar shugaban 'yan kwadago Alhaji Abdulwaheed Omar da takwaransa na kungiyar 'yan kasuwa. Amma shugaban da mataimakin nasa sun sake dawowa dakin tattaunawar awa daya kafin tashi daga tattaunawar.

Za'a sake zama wannan tattaunawa tsakanin gwamnati da 'yan kwadagon a ranar Asabar da misalin 10:00 na safe, a fadar mulkin ta gwamnatin tarayya. Bayan fitowa daga tattaunawar shugaban 'yan kwadago Alhaji Abdulwaheed Omar yace yajin aikin da ma'aikata suka tafi zai ci gaba kamar yadda aka tsara.

No comments:

Post a Comment