Sunday, January 8, 2012

KUNGIYOYI ZASU TAFI YAJIN AIKI TARE DA GABATAR DA ZANGA - ZANGAR LUMANA

Kungiyar kwadago ta kasa NLC da kungiyar 'yan kasuwa TUC da kungiyar malam jami'o'i ASUU da kungiyar dalibai SUG da kungiyar lauyoyi NBA da kungiyar Muryar Talakawan Nigeriya da kungiyar gamayyar kungiyar UNG da sauran daruruwan kungiyoyi masu zaman kansu wadanda bana gwamnati ba, sun kira yajin aikin gama gari tare da zanga - zangar lumana mai taken (OccupyNigeria) a fadin kasar nan baki daya, domin nuna kin amincewa da janye tallafin man fetur da gwamnati tayi, wanda aka zartar a ranar sabuwar shekarar nan ta 2012.

Shugabannin wadannan kungiyoyi da zasu jagoranci zanga - zangar da yajin aikin, sun bayyana cewa zasu tafi wannan yajin aiki ne da kuma zanga - zanga saboda kuncin rayuwar da talakawan Nigeria wanda sune kaso 80% na yawan al'ummar kasar, zasu shiga idan har gwamnati bata dawo da tallafin man fetur da take badawa ba.

Za'ayi wannan yajin aiki ne da zanga - zangar a ranar Litinin 9/1/2012 a daukakin fadin tarayyar Nigeria. Sannan jagororin wannan zanga - zanga sun gargadi mutane da tada zaune tsaye, ko kuma jifan jami'an tsaro da yi musu ihu.

A karshe muna addu'ar Allah yasa wannan yajin aiki da zanga - zanga da za'ayi yasa shine silar daidaituwar al'amura a Nigeria.

OccupyNigeria!!!

No comments:

Post a Comment