Tuesday, January 10, 2012

Gwamnatin Jihar Kaduna ta sanya dokar yawo na tsawo awa Ashirin da Hudu

Gwamnatin jihar Kaduna, karkashin jagorancin gwamna Patrick Ibrahim Yakowa, ta bada dokar hana yawo ga al'ummar birnin jihar da kewaye na tsawon awa 24.

Gwamnatin ta sa wannan doka ne saboda masu zanga - zangar nuna kin amincewa da janye tallafin man fetur da gwamnatin tarayya tayi, suna neman karya doka da oda a cewar Patrick Yakowa.

Shugabannin 'yan kwadago na jihar ta Kaduna wadanda suke jagorantar zanga - zangar, su ma sun sanar da dakatar da zanga - zangar zuwa wani lokaci, amma sun bayyana cewa yajin aiki yana nan daram har sai gwamnatin tarayya sun janye kudirinta na janye tallafin man fetur din.

@thisdaynews

No comments:

Post a Comment