Sunday, June 3, 2012

Al'ummar Masar Sun Sake Fita Filin Zanga - Zanga Akan Hukuncin Da Aka Yankewa Hosni Mubarak


Dubun dubatar yan kasar Masar ne ke gudanar da zanga-zanga a dandalin Tahrir dake birnin Alkahira, kan hukuncin da aka yankewa tsohon shugaban kasar Hosni Mubarak da wasu mukarraban sa.

An dai yankewa Mubarak da tsohon Ministan harkokin cikin gidansa Habib al- Adly hukuncin daurin rai da rai sakamakon samun su da aka yi da laifin haddasa kisan daruruwan masu zanga-zanga a rikicin da ya faru cikin shekarar da ta gabata.

Manyan kwamandojin 'yan sanda shida ne kotun ta sallama, yayin da aka wanke Mubarak da dansa daga zargin cin hanci da rashawa. Masu zanga-zangar sun bukaci a yankewa wadanda ake tuhumar ne hukuncin kisa.

Don haka kungiyoyin siyasa suka yi kira ga jama'a su fito kwansu da kwarkwata domin yin Allah wadai da abinda suka ce rashin adalci a shari'ar.

To wai shin a tunaninku mai jama'ar kasar ta Masar ke nufi? Sanin kowa ne jama'ar kasar da goyon bayan su aka kawo karshen mulkin Hosni Mubarak, yau kuma ga shi sun sake dawowa suna nuna goyon bayansu gare shi. Gaskiyar masu iya magana da suke cewa "Duk wanda bai godewa Allah ba, to zai godewa azabarsa".

A karshe ina fatan al'ummar kasata Nijeriya za su dauki darasi daga wannan abu da ya faru kuma yake sake faruwa a kasar ta Masar.

1 comment:

  1. Kai amma akwai abin dubawa a wannan yunkuri na matasan Egypt karo na biyu.

    ReplyDelete