Tuesday, June 12, 2012

Gidauniyar Rochas Okorocha Za Ta Gina Jami'ar Kyauta A Kasar Nan


Gidauniyar ci gaban ilmi da samar da shi kyauta ga masu karamin karfi ta Rochas Okorocha, ta bayyana kudirinta na gina Jami'ar farko a kasar nan da za ta ke bayar da ilmi kyauta ga masu karamin karfi.

Gidauniyar a halin yanzu na da mallakin makarantun sakandare har guda biyar a fadin kasar nan, wanda duk ake bawa masu karamin karfi ilmi a kyauta a cikin su, makarantun akwai su a bangarorin kasar nan daban daban, akwai a Ogboko jihar Imo, Owerri, Kano, Ibadan da kuma Jos.

Lalle Rochas ya jiri tuta a fadin tarayyar kasar nan, ya kuma zama abin kwatance, da za a samu masu tausayin talakawa kamar sa guda goma a cikin masu mulki da masu arzikin da ke dunkule a kasar nan da ilmi bai gagari 'yan talakawa ba.

Wannan gidauniya ta dade tana tuttula ilmi ga 'yayan da iyayen su ba za su iya daukar dawainiyar biyan kudade karatun 'yayansu ba, kuma wani abin sha'awa tun kafin ya samu mulkin jihar Imo da yake kai a halin yanzu gidauniya ta ke, kuma take yin aikin alkhairai daban daban da suka shafi fannin samar da ilmin zamani.

No comments:

Post a Comment