Sunday, June 10, 2012

Alhamdulillah! Yau Na Cika Shekaru 21 A Duniya


Godiya ta tabbata ga Allah (SWT) Mai kowa mai komai. Tsira da aminci su tabbata ga fiyayyen halitta Annabi Muhammad (SWA). Ina kara godiya ga Allah daya raya ni yau tsawon shekaru ashirin har da daya a wannan duniya mai cike da fadi tashi. Allah ina godiya da ka halicce ni cikin mabiya addinin Musulunci kuma ka zaba min addinin a matsayin addinina, kuma ka dora rayuwata akan tafarkin koyarwar addinin, lalle wannan shi ne babban abin godiya. Ya Allah ina rokonka ka bani ikon karasa rayuwata ba tare da na saba da koyarwa addinin Musulunci ba.

Wannan rana ta 10th June, rana ce mai matukar muhimmanci a gare, kuma rana ce da duk wani masoyina yake taya ni farin cikin zagayowarta. Kamar yadda lissafi ya nuna yau ma Allah ya sake nufarmu da zagayowa wannan rana, saboda haka yau na cika shekaru 21 da haihuwa daidai da watanni 252 ko satuka 1095 ko kwanaki 7671 ko awanni 184104 ko mintuna 11046287 ko sakonni 662777275 hhmm lalle na girma. Ina alfari da wannan rana a matsayin ranar da Allah ya nufi wanzuwata a wannan duniya domin na bauta masa.

A kodayaushe idan wannan rana ta zagayowa abinda yafi tsaya min a raina shi ne yadda iyaye na suka dauki dawainiyata tun daga haihuwata har zuwa yanzu, sun sani makarantu daban daban domin nasan yadda zan bautawa mahaliccina kuma na iya zama da duniya da al'ummar da ke cikin ta lafiya. Zahiri babu wata kalla da zan bayana ta godiya a gare su naji na gamsu sai kawai naci gaba da yi musu addu'ar Allah ya saka musu da mafificin abinda suka yi min na alheri.

'Yan uwa da abokaina ma sun taka muhimmiyar rawa a fannin rayuwata, a koyaushe suna zuwa gare ni idan na bukaci hakan, suna taimako na da bani shawarwari na alkhairi, sukan nuna goyon bayansu a gare ni a dukkan ra'ayi, sukan nuna farin cikin su gare idan abin farin cikin ya same ni, da nuna bakin ciki idan akasin farin ciki ya faru, sukan kasance dani kodayaushe domin kada su bar ni cikin kadai ci. Nagode! Nagode!! Nagode!!!.

Ya Allah ka raya mu, ka bamu ilmi mai amfani da zamu taimaki yan uwanmu da addininmu.

2 comments:

  1. Allah ya raya ka Bashir. Allah ya cika maka burinka. Happy birthday.

    ReplyDelete
  2. Nagode Yallabai, Allah ya kara daukaka.

    ReplyDelete