Wednesday, June 4, 2014

SABON SALO: Sam Nda-Isaiah Zai Tattauna Da 'Yan Nigeria Kai Tsaye A Facebook

 Sam Nda-Isaiah, dan takarar shugabancin kasa a APC, zai tattauna da ku kai tsaye a shafin sada zumunta na Facebook.

Wannan dama ce ga 'yan Nigeria, ta wannan shirin za ku iya yi wa Sam duk wata tambaya da kuke bukatar amsarta daga gare shi, kuma ku samu amsa nan take.

Tattaunawar za ta kasance a gobe Alhamis 5th Yuni, 2014  da misalin 10:00am - 12:00pm da kuma 2:00pm - 3:00pm.

Lokaci ya yi da za ku ke shigowa ana damawa da ku a harkokin siyasar Nigeria, domin bada gudunmawa wajen samun canji na alheri.

No comments:

Post a Comment