Friday, September 26, 2014

Game Da Ni (Bashir Ahmad) A Takaice

Cikakken sunana Bashir Ahmad Ishaq, Ni haifaffen jihar Kano ne, mazaunin birnin tarayyar Nigeria, Abuja. 

Ina aiki da kamfanin Leadership Group Limited, masu buga jaridun (Leadership Daily, Leadership Weekend, Leadership Sunday da Leadership Hausa).

Sai dai har yanzu ni dalibi ne mai neman ilmin addini Musulunci (Domin na san yadda zan bautawa Allah, Mahaliccina) Sannan mai neman ilmin zamani (Domin na san yadda zan tafiyar da rayuwata tare da mutanen zamani). 

Ina son jin labarai da tarihin al'ummomin da suka gabata musamman wadanda suka yi nasara a rayuwarsu (Domin daukar darasi daga gare su). 

Ina da burin tafiye - tafiye (Domin tafiya mabudin ilmi ce). 

Ina son haduwa da jama'a daban - daban, masu bambancin ra'ayi (Domin sanin al'adunsu da halayyen su).

Ina sha'awar zama da wadanda suka fi ni ilmi (Saboda koyaushe nayi hakan ina kara daukar sabon ilmi) 

A kodayaushe kuma ina sha'awar zama shahararre kuma sanannen dan jarida (Domin na samu damar bayyanawa duniya ra'ayoyin talakawan Nigeria, daya dade a kunshe cikin zuciyoyinsu ba tare da samun damar bayyanawa ba). 

A yanzu ina son shiga harkokin siyasa (Domin na bada gudunmawa wajen tabbatar da kyakkyawar Nigeria ga kowa).

HANYOYI TUNTUBA

Lamba = +2348032493020 | Email = bashahmad29@yahoo.com | Twitter = @BashirAhmaad | BBM = 2B2B92CB | Instagram = BashirAhmaad
Bashir Ahmad

2 comments: