Friday, December 5, 2014

TAYA MURNA GA 'YAN KADUNA KAN NASARAR EL-RUFAI

Kafin na taya Malam Nasir el-Rufai murnar nasarar zama dan takarar gwamna, sai na fara taya mutanen Kaduna murna, saboda hanyar da suka hau ta samun shugaban da zai sake dawo da martabar Kaduna a idon duniya. 

 Maganar gaskiya ba karamin farin ciki nayi ba, da nasarar el-Rufai, Kaduna uwa ce ga Arewa, amma tuntuni martabarta ta dusashe a idon duniya. 

 Idan 'yan Kaduna suka zabi el-Rufai ba shi suka yi wa alfarma ba, kan su suka yi wa, kamar yadda Janar Muhammadu Buhari ya bayyana lokacin kaddamar da takarar ta el-Rufai. 

Ina matukar kishin el-Rufai ba dan Kano ba ne, da dan Kano ne.... Fada ma bata baki ne. 

 Allah ya bawa el-Rufai nasara a Kaduna!

No comments:

Post a Comment