Saturday, December 13, 2014

Yakin Neman Zaben Sam Nda-Isaiah: An Fara Da Murmushi An Kammala Da Murmushi

MASHA ALLAH! MASHA ALLAH!! Godiya ta tabbata ga Allah (SWA), an fara da murmushi an kammala da murmushi.

Yau 11/12/2014 APC ta kammala babban taronta na kasa, inda wakilan jam'iyyar suka zabi dan takarar shugabancin kasa a zaben 2015 na jam'iyyar, kuma Allah ya bawa Janar Muhammadu Buhari nasara da gagarumin rinjaye.

Maigidana Sam Nda-Isaiah na daya daga cikin masu neman takarar su biyar, sai dai Allah bai bashi nasara ba, a zahiri, amma a badini yayi nasara (duk wanda ya san tsakanin su da Buhari zai fahimci hakan).

Kusan watanni 10 ana wannan aiki, tun da aka fara Allah cikin ikonsa ya sa an shiga cikin lafiya, kuma yau ga shi an kammala cikin lafiya.

Bayan na mika dukkan godiya ta ga Allah, ina kuma godewa iyaye na da dukkan 'yan uwana da suka bani cikakken goyon baya, sai kuma edita na Al-Amin Ciroma (Leadership Hausa), da dukkan abokaina masu daraja, kwarai na samu muhimmiyar gudunmawa daga gare ku, kuma ina godiyar sosai da sosai Allah ya sanya alheri. Kullum ina kara godewa Allah da ya ba ni abokai irin ku.

Ina rokon ku addu'ar Allah ya sanya wa abinda zan sa anan gaba ya kasance mai alheri na gare ni da addinina.

...Ina taya Baba (Janar Muhammadu Buhari) murnar wannan gagarumar nasara, kuma in sha Allah zan bada duk wata gudunmawa da zan iya, da dukkan abinda Allah ya hore min don ganin Buhari da APC sun yi nasara a 2015!

No comments:

Post a Comment