Wednesday, August 3, 2011

Hamza Al-Mustapha ya fasa kwai a bainar Jama'a

Dogarin tsohon Shugaban kasar Nijeriya Marigayi General Sani Abacha, Major Hamza Al-Mustapha ya fasa kwai game da yadda shugabannin yankin Kudu maso yammacin kasar nan wato yankin Yarabawa, suka karbi cin hancin makudan kudi bayan kashe tsohon babban dan kasuwa kuma dan siyasa M.K.O Abiola.

Al-Mustapha ya baiyana hakan ne a babbar kotun jihar Lagos, yayin da ya baiyana don kare kansa game da zargin kisan Hajiya Kudirat Abiola matar tsohon marigayin, tun a shekarar 1998 ba tare da an yanke masa hukunci ba. Ya kuma kara baiyana cewar tsohon Shugaban kasa General Abdulsalam Abubakar ya sa an tsare shine domin tsoron kar ya baiyana irin badakalar da aka tafka a kisan na Abiola.

Al-Mustapha yace ai baiwa shugabannin Yarabawan sama da dalar Amurka miliyan 200 inda ya shaida cewar ya dade yana son baiyana wannan ta'asa amma saboda tsoron tashin hankali ya hakura sai yanzu da yaga ba mafita sai yayi hakan. A karshe ya shaidawa kotun a zama na gaba zai baiyana fefan bidiyo domin ya zama sheda.

Fatanmu Allah ya taimaki dukkan mai gaskiya akan azzalumai.

Bashir Ahmad
Bashahmad29@yahoo.com
08032493020, 08050600160

2 comments:

  1. Umar Nazir Mai AlewaAugust 20, 2011 at 5:05 PM

    Allah ya taimaki mai gaskiya. Allah ya taimaki Hamza el Mustapha, Allah yasa nan gaba ya zama shugaban kasar Nigeria.

    ReplyDelete