Monday, August 15, 2011

Tsangayar Alheri ta kai ziyara asibitin Kananan Yara

Kungiyar Tsangayar Alheri ta kai ziyara a karon farko tun bayan yiwa kungiyar kwaskwarima daga Sansanin Samari da 'yanmata, kuma shine karon farko data fitar da irin wannan alheri zuwa ga sauran jama'a, ba kamar da da alherin kungiyar ke tsayawa a tsakanin 'yayan kungiyar kadai ba.

Tsangayar Alherin ta kai ziyarar ne zuwa asibitin kananan yara na Hasiya Bayero dake Kofar Kudu a birnin Kanon Dabo. A yayin wannan ziyara kungiyar ta rarraba sabulan wanka da omon wanki ga masu zaman jinya a asibitin.

A jawabin shugaban kungiyar na kasa Abdulqadir Sardauna ya bayyana makasudin kawo wannan ziyara, sannan ya jawo hankalin iyaye da su rinka amfani da hanyoyin rigakafin kariya daga kamuwa da cututtuka musamman gidan sauro mai magani. Shugaban ya kuma bayyana aniyar kungiyar na kara kai wasu ziyarorin zuwa gidan Marayu da gidan Yari (prison) nan bada dadewa ba.

A martanin da wakiliyar ma'aikatan asibitin tayi Dakta Ummu Badaru, ta nuna farin cikinta da kuma godiya ga wannan kungiya, sannan ta bayyana samuwar irin wadannan kungiyoyi a wannan al'umma ba karamin ci gaba bane. Sannan ta kara da cewa suma a matsayinsu na likitoci Musulmai suna da makamanciyar irin wannan kungiya mai suna Islamic Medical Association (ISMA) wadda take taimakawa marassa lafiya masu karamin karfin wadanda basu da yadda zasu yi wurin siyan magunguna. A karshe tayi fatan Tsangayar Alheri zata tafi kafada da kafada da kungiyar tasu ta ISMA.

Bayan kammala ziyarar duba marassa lafiya ne, kai tsaye tawagar Tsangayar Alheri ta nufi wurin da aka tanada dan buda baki (shan ruwa) wanda kungiyar ta shiryawa 'yayanta a karo na biyu bayan wanda akayi a baya ranan 5 Ramadan / 5 August, kuma daya daga cikin 'yayan kungiyar Usman Aminu Alqadiri ya dauki nauyi kamar yadda na bayan ma 'yar kungiyar Shamsiyya Habib ta dauki nauyi. Kuma a ranan 25 Ramadan kungiyar zata gabatar da shan ruwan da ta shirya karo na karshe, wadda shi ma daya daga 'yayan kungiyar Abubakar Abdullahi Kofar Na'isa yayi alkwarin daukar nauyi, fatanmu Allah ya kaimu lokacin da rai da lafiya.

A wurin shan ruwan, an ci an sha anyi hani'an, an kuma yi wasanni da dariya, sannan shugabannin kungiyar na kasa dana reshen jihar Kano suka gabatar da jawabansu, kuma aka bawa wasu daga cikin 'yayan kungiyar suka tofa albarkacin bakinsu. Su ma Malaman kungiyar ba'a barsu a baya ba, sun gabatar da addu'o'i ga kungiya da 'yayanta baki daya. Daga nan aka gabatar da sababbin 'yayan kungiya. A karshe bayan gabatar da Sallan Isha'i kowa ya kama gabansa.

Bashir Ahmad
Acting National Secretary
08032493020, 08050600160.

No comments:

Post a Comment