Tuesday, August 30, 2011

Barka Da Sallah Daga Bashir Ahmad

A yau ne (30 August 2011) daukakin al'ummar Musulman Nigeria suka bi sahun takwarorinsu Musulmai dake sassan duniya daban - daban wurin gabatar da bikin Sallar Idi karama, bayan sauke azumin watan Ramadan.

Allah mai iko! Kamar ko yaushe an samu wasu 'yan tsirarun mutane da su kayi Sallar Idin su tun jiya, saboda sabanin ra'ayi. Abin mamaki wasu mutanen kuma sai gobe 31 August 2011 zasu gabatar da Sallar Idin tasu. Wannan ba shine farko ba, kusan kowane lokacin daukar Azumi da sauke shi hakan tana faruwa, saboda banbancin akida ko kuma rashin ganin wata bai dayawa, ko kuma wasu idan basu ga watan da idonsu ba basa yarda su dauki Azumin ko sauke shi. Fatanmu dai Allah ya kawo mana hadin kai a addininmu na Musulunci, wadda zai kawo samuwar magana da murya daya. Amin!

A karshe zanyi amfani da wannan dama na mika sakon taya murna da barka da shan ruwa ga ilahirin 'yayan kungiyoyin Tsanyarar Alheri, Muryar Talaka, Zauren Shawara Facebook, Gizago Club, Dandalin Siyaya, Nigerian Youth Forum, da sauran kungiyoyin matasa da suka sadaukar da kawunansu wurin fafutukar ganin cigaban kasarmu abar alfarinmu Nigeria.

Duk da tuni na mika wannan gaisuwa tunda da sanyin safiya amma zankara mika wannan gaisuwa a yanzu saboda muhimmancinta ga dukkan abokanaina da nake zaune tare dasu, a gida da makaranta, sannan ga daukakin abokaina dake shafukan sada zumunta na yanar gizo musamman na shafukan Facebook, Twitter, 2go. Bazan taba mantawa daku ba masu ziyartar matattarar tunani wato DANDALIN BASHIR AHMAD. Nagode! Allah ya saka muku da alheri abokaina, ko yaushe addu'ata a gare ku itace Allah ya biya muku bukatunku na Alheri.

Allah ya karbi ibadunmu na watan Ramadan, Allah yasa muna cikin bayin da aka 'yanta akayi musu gafara. Allah ya maimaita mana. BARKA DA SALLAH!

Bashir Ahmad
bashirgy@yahoo.com
+2348032493020

No comments:

Post a Comment