Sunday, July 3, 2011

KAMUN DA HUKUMAR SSS TA YI WA SU EL-RUFA'I BAYA NUFIN KOMAI SAI ADAWAR SIYASA

A safiyar ranar 2nd July, 2011 ne hukumar tsaro ta farin kaya wato SSS ta kama tsohon Ministan birnin tarayya Abuja Mallam Nasir el-Rufa'i tare da wasu jiga-jigan jam'iyyar CPC a filin jirgin saman kasa da kasa na Nmandi Azikiwe dake birnin tarayya Abuja. Jim kadan da saukarsu daga birnin London, inda suka raka dan takarar shugaban kasa a zaben 2011 Janar Muhammad Buhari a wata mukala da aka shirya game da zaben da ya gabata a watan April.

Mutane da dama na ganin wannan kamu da aka yi wa su el-Rufa'i an yi shine ba tare da wani kwakkwaran dalili ba, kawai dai an kama su ne saboda adawa irin ta siyasa da gwamnati me ci a yanzu ke yi da Janar Muhammad Buhari, domin kuwa a lokacin da el-Rufa'i ya dawo Nigeria daga England a shekarar da tagaba bayan rasuwar tsohon shugaban kasa Alhaji Umar Musa Yar'adua, bai samu matsin lamba ba ko kadan, amma tun daga lokacin da ya nuna bangaren da yake goyan baya a siyasa nan suka fara takun saka da gwamnati. Tun daga lokacin ake ta kakalen laifin da za'a lika masa a kama shi amma ba'a samu ba.

Da manema labarai suka nemi jin dalilin kama tsohon ministan, mai magana da yawun hukumar Uwargida Marilyn Ogar tace ''An kama tsohon Ministan ne saboda wasu tambayoyi da zasu yi masa game da wasu kage da yayi wa gwamnatin tarayya, wanda aka wallafa a jaridar National Daily ta ranan Juma'a da ta gabata. wanda kuma a cewarta maganganun da ya fada ba gaskiya ba ne''

Uwargida Ogar ta bayyana cewa kagen da Mallam el-Rufa'i yayi wa gwamnatin Nigeria ya sabawa "Freedom of Information" (FOI) amma kuma bata yin gamsasshen bayani akan kagen ba.

Janar Muhammad Buhari ya bayyana cewa a gaggauta sakin el-Rufa'i da sauran mutane da ake tsare da su, sannan kuma yace ko kadan hakan bai kamata ba, don kuwa maganganunsa basu sabawa kundin tsarin mulki ba.

A mukalar el-Rufa'i ta ranan 1st July, 2011 ya bayyana irin magudan kudin da Nigeria tayi kasafin wannan shekara, kuma ya tabo kasafin kudin shekarar da ta gabata idan kuma ya tabbatar da cewa ko kadan wadannan makudan kudade da aka batar basu amfanar da dan Nigeria da ita kanta Nigerian komai ba. Ya bayyana kudaden da kasar ta samu dalla-dalla. Wanda hakan gwamnati dake ganin ya sabawa dokar bayyana yancin fadin bayyanai (FOI).

A gaskiyance maganganun Mallam el-Rufa'i basu sabawa doka ba, ko kudin tsarin mulki, ko wata hukuma ta daban. A matsayin shi na dan kasa kuma mai bibiyar al'amuran mulkin kasar yana da yancin fadawa talakawa irin bada kalar da watandar da ake yi da kudaden su, tun da kuwa kasar na tafiya ne akan turbar demokradiyya.

To a karshe abin tambayar anan shi ne su sauran manyan jam'iyyar CPC da aka kama su tare menene makomarsu? Wane dalili yasa aka kama su? Ko su ma rubutun suka yi wanda ya sabawa (FOI)? Ko daman suna da wani laifi na daban? Tabbas ni kam a tunani na wannan kamun an yi shi ne da wata manufa ta daban, ba wai akan rubutun da Mallam Nasir el-Rufa'i yayi ba.

Allah yana bayan mai gaskiya!!!

Bashir Ahmad
Bashirgy@yahoo.com
2348032493020

No comments:

Post a Comment