Wednesday, March 31, 2010

BAYAN SAMUN YANCIN KAN NIGERIA


Kadan daga cikin Muhimman abubuwan da suka faru bayan samun yancin kan kasarmu Nigeria.

Ranar 6 July 1967, aka fara yakin basasar Biafra har zuwa ranar 12 January 1970.

Ranar 1 October 1960, Nigeria ta samu yancin kai daga wurin turawan kasar Burtaniya.

Ranar 29 May 1967, Nigeria ta canja kudin kasar zuwa Naira da Kobo.

Ranar 22 May 1973, aka maida tsarin yan bautar kasa wato NYSC kasa da shekaru (24) ashirin da hudu.

Ranar 28 May 1975, aka gina ofishin kungiyar tattalin arzikin kasashen Afrika ta yamma wato ECOWAS a jihar Lagos.

Ranar 14 February 1976, General Murtala Ramat Muhammad ya dawo da birnin tarayyar Nigeria daga Lagos zuwa Abuja.

Ranar 15 February zuwa 12 March 1977, akayi biki nuna al'adun Afrika karo na biyu a jihar Lagos.

Ranar 13 February 1982, Pope John Paul, ya ziyarci kasar Nigeria a karo na biyu.

Ranar 16 October 1986, Professor Wole Soyinka, ya zama dan kasar Nigeria kuma dan Afrika na farko daya samu nasarar cin gasar Alfred Nobel Prize a Stock Holm dake kasar Sweden.

Ranar 18 February 1988, aka kirkiri Federal Road Safety Commission. Kuma Prof. Wole Soyinka ya zama shugaba na farko.

Ranar 4 April 1988, aka canja kayan yan sadan Nigeria zuwa kalar Baki.

Ranar 11 July 1991, sama da yan Nigeria mutum 250 ne suka rasu a sakamakon hadarin jirgin sama a Jiddah, kasar Saudi Arabia.

Ranar 27 August 1991, shugaba Ibrahim Badamasi Babangida, ya sanar da karin jihohi da kuma kananan hukumomi guda 47.

Ranar 27 zuwa 29 November 1991, akayi kidayar mutanen kasar Nigeria.

Ranar 2 August 1996, Nigeria ta zama kasa ta farko a nahiyar Afrika da ta fara lashe gasar Olympic wanda akayi a Atlanta, kasar America.

Ranar 8 August 1998, Allah (SWA) yayi wa General Sani Abacha, rasuwa a Aso Rock, yana da shekaru 54 an binne shi a jiharsa ta haihuwa Kano, a ranar daya rasu kamar yadda tsarin Addinin Musulunci ya tana da.

Ranar 29 May 1999, mulkin kasar Nigeria ya koma hannun farar hula.

No comments:

Post a Comment