Thursday, February 9, 2012

Gaskiya Ta Fara Bayyana - Katako Ya Bayyana Shaidar Karya Yayi akan Hukuncin Al-Mustapha


Muhammad Abdul, wanda aka fi sani da Katako, daya daga cikin sahun gaba wuri bada sheda game da kisan da aka yi wa Hajiya Kudirat. Katako a karon farko ya bada shedar cewa Major Hamza Al-Mustapha ne tsohon dogarin Sani Abacha ya bada umarnin harbe Kudirat Abiola, wanda wannan dalili ya sa wata kotu a jihar Lagos ta yankewa Al-Mustapha hukuncin kisa ta hanyar rataya.

Katako a jiya ya bayyana cewa wannan sheda daya bada shedar zur ce, gwamnati ta ba shi cin hanci ne yayi wannan sheda. Kuma ya bayyana cewa Al-Mustapha ba mai lefi ba ne.

Ya bayyana hakan ne a gidan radiyon Hausa na France (RFI) Katako yace "Eh, shedar zur nayi, amma daga baya da nayi tunani na ga akwai ranar lahira, duk wani abu da na samu anan duniya akan karya ranar lahira gaskiya za ta bayyana, wannan ya sa na koma kotu na tabbatar da cewa karya nayi".

Da aka tambaye shi mai ya sa ya bada shedar karyar sai ya bada amsa da cewa "An yi min alkawari abubuwa masu tarun yawa, da farko an tsare ni akan maganar Muhammad Sani Abacha, sun tabbatar min cewa sun gano wasu kudi masu dumbin yawa a wurinsa, idan na bada shedar karya aka karbo wadannan kudade za'a ba ni kaso 10 a ciki ko nawa ne, kuma za su hada min da gida a ko ina nake son yin rayuwa. A karshe kuma sai suka kawo min maganar Al-Mustapha suka karanta min duk irin zargin da suke yi masa, da kuma irin abin da zan fada idan an je kotu".

Ya kara da cewa "Mun zauna da manyan lauyoyi da dama, har nake tambayarsu shin ba abinda zai same ni? Suka tabbatar min da ba abinda zai faru da ni, suka ce kar na damu wannan magana ce ta gwamnati kuma ni sheda ne na gwamnati".

Katako yace yanzu yana nadamar wannan karya da yayi, saboda a matsayinsa na Musulmi an hore shi da zamu mutumin kirki, kar ya cuci kowa ko yayi sanadin mutuwar wani, sannan ya kara da cewa "Duk da ya koma kotu tun da wuri ya sanar da cewa shedar zur ya bada, amma kotun ta ki amincewa da cewa karya nayi, da maganata ta farko za suyi amfani. Saboda haka yanzu nake son kowa da kowa yasan cewa shedar zur na bada a kotu, kuma Al-Mustapha ba shi da laifi"

Da aka tambaye shi ko an cika masa alkawuran da aka yi masa? Sai yace "Alkawari daya aka cika min an bani gida a Jos, kudi na bayyana cewa karya nake yi ba don ba'a cika min alkawuran da aka daukar min ba. Na yi hakan ne saboda sanin idan har aka kashe shi ta hanyar rataya ransa yana kai na, kuma duk dadewar da zanyi anan duniya dole zan mutu, don haka ina so duniya ta san cewa ba Al-Mustapha ne yayi sanadiyar mutuwar Kudirat Abiola ba, kuma shi ba mai laifi ba ne".

Ya Allah ka kara bayyana gaskiya, kuma ka baiwa gaskiya nasara akan karya, ka kubutar da bawanka Al-Mustapha daga hannun azzalumai.

Source: Nairaland.com via People Daily Newspaper.

1 comment:

  1. Allah ya kara tona musu asiri. Azzalumai kawai. Al Mustapha muna taya ka da addua. Idris Haruna Gumel

    ReplyDelete