Monday, August 9, 2010

RAMADAN KAREEM

RAMADAN na daya daga cikin jerin watannin Musulunci guda goma sha biyu. Kuma shine a jeri na tara.
Dukkan Musulmi wajibi ne a gare shi ya azumci wannan wata na RAMADAN Mai Alfarma.

AZUMI na daya daga cikin jerin Shikashikan Musulunci guda biyar. Bayan Shahada da Sallah. Sannan kuma daga shi sai Zakkah da Aikin Hajji ga duk wanda Allah Ubangiji ya nufa da zuwa.

Wannan wata na RAMADAN nada matukar muhimmanci wurin Allah, dan haka sai mu dage wurin neman gafarar Allah a wannan wata mai Alfarma.

Abubuwa da dama sun faru masu muhimmanci a cikin wannan wata, kadan daga ciki sun hada da:
Wahayin Alkur'ani Mai Girma.
Yakin Badar a shekara ta biyu baya hijira.

Allah Madaukakin Sarki na cewa a cikin Alkur'ani Mai Girma " Alkur'ani an saukar da shine a watan Ramadan, sannan kuma Ramadan shiriya ne ga mutane da bayani na shiriya wanda yake banbance tsakanin shiriya da bata. Wanda ya ga wata ko ya ji bayanin ganinsa to ya dau Azumi.
(Baqrat 180).

Allah bamu ikon bauta masa cikin wannan Wata Mai Alfarma kuma ya Gafarta mana dukkan zunubanmu. Ameen.

No comments:

Post a Comment