Friday, August 27, 2010

MA'ANAR AZUMIN A SHARI'A

AZUMI Shine kamewa daga barin ci da sha, jima'i da kuma maganganun banza, tun daga ketowar alfijir har zuwa faduwar rana da niyyar yin Ibada ga Allah (S.W.T). Saboda fadin Allah cewa "Ku ci ku sha har sai alfijir ya fito daga duhun dare, sannan sai ku cika azuminku zuwa faduwar rana" (Bakara 187).

Hadisin Abu Huraira (R.A) Yace Manzon Allah (S.A.W) Yace "Duk wanda bazai bar kirkire-kirkiren karya ko aikin ashsha ko jahilci (wauta) to lallai Allah baya bukatar ya bar ci da sha don yin azumi (Bukhari da Abu Dauda)

Idan muka yi duba da wannan ayar da hadisin zamu ga cewa lallai idan mutun yana son yayi azumi irin na Shari'a to lallai ne mutum ya bar abubuwan da aka zayyana. Sannan kuma ya kare idonsa da bakin daga abinda Ubangiji ya haramta.

Yana daga abinda yake wajibi akan mai azumi ya nisanta kansa daga kallon fina-finan turawa musamman na batsa. Domin kaucewa kishirwar banza da yunwa wacce ba lada a cikinta.

A karshe muna rokon Allah Ya karemu daga munanan halaye a wannan lokacin na Azumi. Ameen.

No comments:

Post a Comment