Wednesday, June 9, 2010

ZAGAYOWAR RANAR HAIHUWA TA

Alhamdulillah:
Godiya ta tabbata ga Allah Madaukakin Sarki mai kowa mai komai, Ubangijin sammai da kassai da dukkan abinda ke cikinsu.

Tsira da Aminci su tabbata ga fiyayyen halitta wanda aka yi duniya, lahira, Aljanna da wuta dominsa, cikamakin Annabawa, Annabi Muhammad (S.A.W.) da Alayensa da Sahabbansa da kuma dukkan wanda suka gastata shi baki daya. Ameeen.

Ranar Litinin 10th June 1991 daidai da 27 Dhul Qidah 1411 wato shekaru 19 kenan yau, ranar ne aka haife ni. Lalle na girma sai Aure!

Godiya Ta musamman kuma mai tarun yawa ga Iyaye na da kuma Kakanni na da suka dauki nauyi na da Allah ya dora musu, kuma suka tarbiyantar dani bisa tarbiyar Addinin Musulunci. Tun ina dan karami suka sani a makarantar Al Qur'ani mai girma, kuma sukai ta dawainiya dani har Allah ya bani haddar Al Qur'ani mai girma (Alhamdulillah) kuma duk da haka suka sakani a makarantar boko a halin yanzu.

Tabbas don haka bani da wata kalma da zan iya furtawa don nuna godiya ta a garesu, game da wannan abinda suka yi min sai dai kawai nace Allah (S.W.T.) ya saka musu da mafificin abinda suka yimin, ameen summa ameen.

Kamar yadda lissafi ya nuna yau Alhamis 10th June 2010 / 26 Jumada Thani 1431. Ina da shekaru 19, watanni 228, makonni 991, ranaku 6,939, sa'o'i 166,551, mintuna 9,993,103 da kuma dakika 599,586,227.

A KARSHE: Ina godiya ga sauran yan uwana da abokai na, maza da mata game da irin shawara da suke bani idan sunga zanyi ko kuma nayi wani abu ba daidai ba. Allah ya saka muku da alkhairi. Ameen.

1 comment:

  1. Salaam, your blog is not at all bad, its good anyways Allah bada Sa'a ameen.

    ReplyDelete