Tuesday, September 21, 2010

BELLO GARBA BELLO (BABA) YA MUSANTA LAIFIN KISAN MAHAIFANSA DA KANNINSA UKU

A sati biyu da suka wuce a cikin birnin Kano aka tashi da wani mummunan tashin hankali mai tsoratarwa da dimautarwa, na kisan gilar wani jami'in tsaron farin kaya wato (SSS) Mai suna Garba Bello da Matarsa da 'Yayansa guda uku Mata biyu Namiji guda daya.

A washe garin wannan rana jami'en tsaron 'yan sanda dana SSS suka gano cewa dansa na cikinsa ne ya kashe Iyayen nasa da sauran kannin nasa. Wanda ake kira Bello Garba Bello (Baba).

Baba ya amsa laifinsa a lokacin da Yan Jaridu ke yi masa tambayoyi. Amma kuma da ake gurfanar dashi a kotu gaban Shari'ah, sai kuma yayi turjiya yace bashi ya kashe Mahaifan nasa da Kannun nasa ba. Yana fada yana zubda hawaye.

A yanzu haka Kotu ta dage sauraren wannan kara zuwa Ranar 7 ga watan October.

Fatan mu dai shine Allah Ubangiji ya bayana mai gaskiya game da wannan sarkakakken al amari mai tada hankalin masu hankali.

A karshe Allah Ubangiji ya samu a tafarkin gaskiya Alfarmar Annabi Muhammad (S.A.W.)

No comments:

Post a Comment