Thursday, May 14, 2015

Ya Zama Dole Buhari Ya Cika Duk Alkawuran Da Ya Dauka Lokacin Yakin Neman Zabe - Sule Lamido

Gwamna Sule Lamido na jihar Jigawa, ya kalubalenci zababben shugaban kasa, Janar Muhammdu Buhari da jam'iyyarsa ta APC.

Lamido yayin da yake jawabi a yau a jihar Neja, yayin bude wasu ayyuka ya ce Buhari da APC ya zama dole su cika dukkan wasu alkawura da suka daukarwa 'yan Nijeriya lokutan yakin neman zabe, ba tare da neman kowane irin uzuri ba.

"Sun yi kokari ruguza Nijeriya da kawo tashin hankali tsakanin kabilu da mabiya addinai, sun yi alkawuran karya. Ya zama dole su cika wannan alkawura ba tare da neman ayi musu kowane irin uzuri ba" in ji Lamidon.

Ya kara da cewa a lokacin yakin neman zaben APC ta maida hankali ne wajen aibata PDP ta hanyar amfani da rashin tsaro, Boko Haram, rashin aikin yi, don haka ya zama dole su cika dukkan alkawuran.

No comments:

Post a Comment