Thursday, May 7, 2015

Allah Ya Sa Aljanna Ta Zama Masaukin Zainab Na Karshe

ALLAH YA JIKAN ZAINAB ALIYU


Zainab Aliyu, daliba ce 'yar shekaru 21, ta sha fama da cutar Blood Cancer, shekaru biyu da suka gabata cutar tayi tsanani, tun daga lokacin har zuwa yau da Allah ya dauki ranta ba ta sake samun lafiya ba.


Kafin cutar da kwantar da ita Zainab na karatu ne a Jami'ar Ahmadu Bello, Zaria.


Tun shekarar da ta gabata Zainab take kwance a cibiyar lafiya ta duniya (International Medical Centre) dake birnin Cairo, na kasar Egypt, kafin daga bisani a dauke ta zuwa kasar India, inda anan Allah ya yi mata cikawa.


Allah ya sa jinyar da Zainab ta dade tana yi ta zama sanadiyar gafararta. Allah ya sa Aljanna ta zama masaukinta na karshe.

No comments:

Post a Comment