Wednesday, September 14, 2011

Lambar Mutuwa 09141 Karya ko Gaskiya?

Duk mutumin da yace kace bai ji labarin jita-jitar 'Lambar Mutuwa' ta 09141 a yau 14 September 2011 kai tsaye zance shi ba dan asalin Nigeria, ko kuma nace baya kasar a halin yanzu.

Wannan jita jita ta lambar mutuwa ta cika shafukan yanar gizo, inda ake cewa idan an kira mutum da lambar 09141 a wayar tafi da gidanka kuma ya amsa kiran nan take zai mutum, hakan tasa aka sawa lambar suna 'The killer number' wato lambar mutuwa.

A irin wadannan jita jita akwai wadda ake cewa wai mutane sama da 10 sun mutu sakamako amsa kiran da sukayi daga wannan lamba ta mutuwa a karamar hukumar Wukari dake Jihar Adamawa, duk da har yanzu babu tabbacin hakan daga majiya kwakkwara.

Duk da a matsayinmu na Musulmai mun tabbata babu mai kashewa da rayawa sai Allah don haka ko kadan ba zamuyi imani da cewa wannan lamba ce ke kisan ba, sai mu yarda idan itace sanadin mutuwar mutum to tabbas sai ya mutum koda idan an kira shi da ita bai amsa ba, saboda haka ya kamata muke lura da irin mu'amalar da zamu ke yi da mutane musamman a shafukan sada zumunta na yanar gizo. Kowa dai yana sane da irin yadda matsafa suka cika irin wadannan shafuka, kuma wannan lamba ko shakka babu tsafi ne.

Wasu kuma na ganin kawai wani ne ya zauna ya kirkiri jita jitarsa ya rinka yadawa, domin lambar da ake amfani da ita tayi daidai da kwanan wata da shekarar da muke ciki a yau. Misali 09 = September 14 = Kwanan watan 1= 2011. Ko ma dai menene fatanmu Allah ya kare Musulunci da Musulmai duk inda suke a fadin duniya.

Don Allah ka sanar da wanda bai sani ba! Save innocent life!

Bashir Ahmad
Bashirgy@yahoo.com
08032493020

No comments:

Post a Comment