Friday, May 28, 2010

RIBA KO HASARA

29th May 1999 daga wannan rana zuwa yau shekaru goma sha daya kenan kuma adadin shekarun da kasar Nigeria ta canja tsarin mulkin kasar zuwa tsari democradiya, irin tsarin da kasar America ke amfani dashi.

Cikin wannan shekaru Nigeria tayi shugabanni guda uku biyu daga kudu, daya daga arewa. Biyu daga ciki zaben su muka yi daya kuma ya samu mulkin ne a matsayin na mataimaki bayan shugaban daya ke kai Allah yayi mai rasuwa.

Nigeria kasa ce wadda Allah ya albarkan ce ta da arzukin noma, ma'adanan kasa da kuma man futar, wannan dalili yasa ake ganin duk nahiyar Africa ba wata kasa da takaita arzuki. Ga kuma yawan jama'a da Allah ya hore mata sama da mutum miliyan dari da talatin, 130,000000.

Amma kash duk da irin wannan abubuwa da Allah ya hore mana bamu samu shugabanni nagari ba. Sai dai muna adu'ar Allah ya albarkan ce mu da shugabanni nagari.

Tambaya anan wai shin a wannan tsarin da kasar mu ta zaba na democradiya ta koma. Shin Riba aka ci ko Hasara aka yi.

A karshe ina taya dukkan daukakin al'ummar kasar Nigeria da kuma dukkan masoyanta kasar Murnar zagayowar wannan rana ta demokradiya wato Democracy Day

No comments:

Post a Comment