Thursday, February 5, 2015

AREWA MUN FARKA DAGA BACCI: Jonathan Ya Sa Mun Fara Hada Kan Mu

Masha Allah, yanzu kam zan iya cewa watakila Arewa mun farka daga dogon baccin da muka dade muna yi.

Sakamakon zaman majalisar zartarwa na kasa da aka kammala dazu ya kara min karfin guiwa kan lalle Arewa wannan karon da gaske muke yi.

Kamar yadda wani da yake da masaniyar yadda zaman majalisar ya gudana yake shaida min a waya yanzu, ya ce bayan Jega ya tashi yayi jawabinsa a gaban majalisar, inda ya bayyana cewa INEC ta shirya gudanar da zabe a ranakun 14 da 28 na watan nan, gwamnatin tarayya da 'yan kanzaginta sun nemi kin amincewa da hakan, sai dai gwamnonin APC su 14 da suka halarci taron, da Janar Buhari da kuma Hon. Aminu Tambuwal duk sun goyi bayan maganar ta Jega.

Haka kuma wasu daga cikin gwamnonin PDP daga yankin Arewa su ma sun nuna goyon bayan su ga Jegan, abinda ba a yi tsammanin hakan daga wurin su ba.

Da na nemi ya fada min wadanne gwamnoni ne daga Arewa sai yace na bari na karanta a jarida idan labarin ya fita, amma akwai gwamnan jihar J... da kuma B... haka kawai ya fada min bai karasa min sunan ba.

Yanzu dai zabe zai gudana a ranar 14 da 28, zabi ya rage gare mu, ya zama dole mu fita mu karbi katin zaben mu na dindindin don zaben shugabannin da muke gani za su yi mana abinda za mu zabe su don su.

...Ni dai na yake shawara tuntuni, a zaben shugaban kasa, Janar Muhammadu Buhari, na jam'iyyar APC zan zaba kamar yadda na saba, zabensa tun daga 2003.

No comments:

Post a Comment