Tuesday, November 9, 2010

YADDA NA FAHIMCI GENERAL MUHAMMAD BUHARI (RTD)


Yadda na fahimci General Muhammad Buhari a matsayi na na dalibi dan shekara kasa da 20 wanda a lokacin da Buhari yayi mulkinsa ko haifa ta ma ba'ayi ba. Kuma lokacin da ya rike hukumar PTF bani da wayo sosai. Amma duk da hakan tabbas na fahimci General Muhammad Buhari mutum ne mai gaskiya, rikon amana da kaunar talakawa.

Dalili kuwa shine yadda General Muhammad Buhari ya rike manyan manyan mukamai a kasar amma har yanzu talakawa ke sonsa kuma suna muradin ya dawo ya sake mulkarsu a matsayin shugaban kasa,
Na fahimci a kasar nan ko mukamin Chairman mutum ya rike to a karshe magoya bayansa ne zasu dawo suna yakarsa saboda rashin gaskiyarsa da kuma rashin bai tsinana musu abin azo a gani ba.

Amma General Buhari ya rike mukamai kamar haka: Gwamnan jihar Arewa maso gabas (Borno), ya rike shugaban hukumar man fetur ta kasa (NNPC) kuma shine shugaban hukumar karo na farko, sannan ya zama shugaban kasar Nigeria na tsahon shekaru biyu, a karshe kuma ya rike shugaban hukumar PTF a lokacin mulkin General Sani Abacha.
To amma duk wadannan manyan manyan mukaman da General ya rike bai yi amfani da su ba wajen sace kudin talakawa, wannan yasa har yanzu talakawan Nigeria suke Addu'ar Allah (SWA) ya dawo musu da shi.

Buhari yayi takarar shugaban kasa har karo biyu a 2003 da 2007 duk a karkashin jam'iyar ANPP amma saboda rashin yin zaben adalci duk aka ce duk baiyi nasara ba, alhalin kuwa talakawa shi suka fita suka zaba. Duk da hakan General baiyi kasa a gwiwa ba, yanzu ma ya sake tsayawa takara a zaben 2011 amma a karkashin sabuwar jam'iyar da ya kirkira wadda bata fi shekara daya ba, tuni magoya baya suka cika ta makil wato CPC Change, mai dauke da alamar tuta da alkalami a jiki.

A karshe Allah ya karfafawa talakawa gwiwa sama da zabukan da suka wuce baya, su sake fita don kadawa Buhari kuri'a, ba don komai ba sai don shugaban hukumar zaben na yanzu da alama kamar zai kamanta adalci. fitar kuma ita ce hanya mafi sauki da za mu samarwa kanmu mafita a halin da muke ciki a kasar nan. Allah ya taimake mu a wannan zabe na gaba da shugaba adali a kasar mu Nigeria ameeeeeeeeen....!

No comments:

Post a Comment